< Karin Magana 5 >
1 Ɗana, ka mai da hankali ga hikimata ka saurara da kyau ga kalmomin basirata,
My son, attend to my wisdom, and bow your ear to my understanding:
2 don ka ci gaba da yin kome daidai leɓunanka za su adana sani.
That you may regard discretion, and that your lips may keep knowledge.
3 Gama leɓunan mazinaciya na ɗigan zuma, maganarta tana da sulɓi fiye da mai;
For the lips of a strange woman drop as an honeycomb, and her mouth is smoother than oil:
4 amma a ƙarshe tana da ɗaci kamar tafashiya, mai ci kamar takobi mai kaifi biyu.
But her end is bitter as wormwood, sharp as a two-edged sword.
5 Ƙafafunta na kaiwa ga mutuwa; sawunta na jagora kai tsaye zuwa kabari. (Sheol )
Her feet go down to death; her steps take hold on hell. (Sheol )
6 Ba ta wani tunanin rayuwa; hanyoyinta karkatacce ne, amma ba tă sani ba.
Lest you should ponder the path of life, her ways are moveable, that you can not know them.
7 Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; kada ku juye daga abin da nake faɗa.
Hear me now therefore, O you children, and depart not from the words of my mouth.
8 Ku yi nesa da hanyarta, kana ku je kusa da ƙofar gidanta,
Remove your way far from her, and come not near the door of her house:
9 don kada ku ba da ƙarfi mafi kyau ga waɗansu da kuma shekarunku ga wani marar imani,
Lest you give your honor to others, and your years to the cruel:
10 don kada baƙi su yi biki a kan dukiyarku wahalarku ta azurta gidan wani mutum dabam.
Lest strangers be filled with your wealth; and your labors be in the house of a stranger;
11 A ƙarshen rayuwarku za ku yi ta nishi, sa’ad da namanku da jikinku suka zagwanye.
And you mourn at the last, when your flesh and your body are consumed,
12 Za ku ce, “Me ya sa na ƙi horo! Me ya sa zuciyata ta ƙi gyara!
And say, How have I hated instruction, and my heart despised reproof;
13 Ban yi biyayya da malamaina ba ko in saurari masu koyar da ni.
And have not obeyed the voice of my teachers, nor inclined my ear to them that instructed me!
14 Na zo gab da hallaka gaba ɗaya a tsakiyar dukan taron.”
I was almost in all evil in the middle of the congregation and assembly.
15 Ku sha ruwa daga tankinku, ruwa mai gudu daga rijiyarku.
Drink waters out of your own cistern, and running waters out of your own well.
16 In maɓulɓulanku suka cika suna malala har waje, rafuffukan ruwanku a dandalin jama’a?
Let your fountains be dispersed abroad, and rivers of waters in the streets.
17 Bari su zama naka kaɗai, don kada ka raba da baƙi.
Let them be only your own, and not strangers’ with you.
18 Bari maɓulɓulanka ya zama mai albarka, bari kuma ka yi farin ciki da matar ƙuruciyarka.
Let your fountain be blessed: and rejoice with the wife of your youth.
19 Ƙaunatacciyar mariri, barewa mai kyan gani, bari mamanta su ishe ka kullum, bari ƙaunarta ta ɗauke hankalinka kullum.
Let her be as the loving hind and pleasant roe; let her breasts satisfy you at all times; and be you ravished always with her love.
20 Ɗana, me ya sa za ka bari mazinaciya ta ɗauke maka hankali? Don me za ka rungume matar wani?
And why will you, my son, be ravished with a strange woman, and embrace the bosom of a stranger?
21 Gama hanyar mutum a bayyane take a gaban Ubangiji, yana kuma lura da dukan hanyoyinsa.
For the ways of man are before the eyes of the LORD, and he ponders all his goings.
22 Ayyukan mugunta na mugun mutum tarko ne gare shi; igiyoyin zunubinsa za su daure shi kankan.
His own iniquities shall take the wicked himself, and he shall be held with the cords of his sins.
23 Zai mutu saboda rashin ɗa’a yawan wawancinsa zai sa yă kauce.
He shall die without instruction; and in the greatness of his folly he shall go astray.