< Karin Magana 23 >

1 Sa’ad da ka zauna domin cin abinci da mai mulki, ka lura sosai da abin da yake gabanka,
Wenn du sitzest und issest mit einem Herrn, so merke, wen du vor dir hast,
2 ka kuma sa wuƙa a maƙogwaronka in kai mai ci da yawa ne.
und setze ein Messer an deine Kehle, wenn du gierig bist.
3 Kada ka yi marmarin abincinsa mai daɗi gama wannan abinci ruɗu ne.
Wünsche dir nichts von seinen feinen Speisen; denn es ist falsches Brot.
4 Kada ka gajiyar da kanka don ka yi arziki; ka kasance da hikimar dainawa.
Bemühe dich nicht reich zu werden und laß ab von deinen Fündlein.
5 Da ƙyiftawar ido a kan wadata ta ɓace, gama tabbatacce sukan yi fikafikai sukan tashi sama kamar gaggafa.
Laß dein Augen nicht fliegen nach dem, was du nicht haben kannst; denn dasselbe macht sich Flügel wie ein Adler und fliegt gen Himmel.
6 Kada ka ci abincin mai rowa, kada ka yi marmarin abincinsa mai daɗi;
Iß nicht Brot bei einem Neidischen und wünsche dir von seinen feinen Speisen nichts.
7 gama shi wani irin mutum ne wanda kullum yana tunani game da tsadar abincin. Zai ce maka, “Ci ka sha,” amma zuciyarsa ba ta tare da kai.
Denn wie ein Gespenst ist er inwendig; er spricht: Iß und trink! und sein Herz ist doch nicht mit dir.
8 Za ka yi amai ɗan abin da ka ci dukan daɗin bakinka kuwa zai tafi a banza.
Deine Bissen die du gegessen hattest, mußt du ausspeien, und mußt deine freundlichen Worte verloren haben.
9 Kada ka yi magana da wawa, gama zai yi wa maganar hikimarka ba’a.
Rede nicht vor des Narren Ohren; denn er verachtet die Klugheit deiner Rede.
10 Kada ka kawar da shaidar iyaka ta dā ko ka ɗiba gonar marayu,
Verrücke nicht die vorigen Grenzen und gehe nicht auf der Waisen Acker.
11 gama mai Kāriyarsu yana da ƙarfi; zai kuwa yi magana dominsu.
Denn ihr Erlöser ist mächtig; der wird ihre Sache wider dich ausführen.
12 Ka mai da hankali ga umarni ka kuma kasa kunne ga kalmomin sani.
Gib dein Herz zur Zucht und deine Ohren zu vernünftiger Rede.
13 Kada ka bar yaro ba horo; in ka yi masa horo da sanda, ba zai mutu ba.
Laß nicht ab den Knaben zu züchtigen; denn wenn du ihn mit der Rute haust, so wird man ihn nicht töten.
14 Ka hukunta shi da sanda ka ceci ransa daga mutuwa. (Sheol h7585)
Du haust ihn mit der Rute; aber du errettest seine Seele vom Tode. (Sheol h7585)
15 Ɗana, in zuciyarka mai hikima ce, to, zuciyata za tă yi murna;
Mein Sohn, wenn dein Herz weise ist, so freut sich auch mein Herz;
16 cikin cikina zai yi farin ciki in leɓunanka suna maganar abin da yake daidai.
und meine Nieren sind froh, wenn deine Lippen reden, was recht ist.
17 Kada ka bar zuciyarka tă yi ƙyashin masu zunubi, amma kullum tsoron Ubangiji za ka yi kishi.
Dein Herz folge nicht den Sündern, sondern sei täglich in der Furcht des HERRN.
18 Tabbatacce akwai sa zuciya ta nan gaba dominka, kuma sa zuciyarka ba za tă zama a banza ba.
Denn es wird dir hernach gut sein, und dein Warten wird nicht trügen.
19 Ka saurara, ɗana, ka zama mai hikima, ka kafa zuciyarka a hanyar da take daidai.
Höre, mein Sohn, und sei weise und richte dein Herz in den Weg.
20 Kada ka haɗa kai da waɗanda suke shan ruwan inabi da yawa ko masu haɗama kansu da abinci,
Sei nicht unter den Säufern und Schlemmern;
21 gama bugaggu da ruwan inabi da masu yawan ci sukan zama matalauta, gama jiri yakan yi musu sutura da tsummoki.
denn die Säufer und Schlemmer verarmen, und ein Schläfer muß zerrissene Kleider tragen.
22 Ka kasa kunne ga mahaifinka, wanda ya ba ka rai, kada kuwa ka rena mahaifiyarka sa’ad da ta tsufa.
Gehorche deinem Vater, der dich gezeugt hat, und verachte deine Mutter nicht, wenn sie alt wird.
23 Ka saye gaskiya kada kuwa ka sayar da ita; ka nemi hikima, horo da fahimi.
Kaufe Wahrheit, und verkaufe sie nicht, Weisheit, Zucht und Verstand.
24 Mahaifin adali yana da farin ciki sosai; duk wanda yake da ɗa mai hikima yakan ji daɗinsa.
Der Vater eines Gerechten freut sich; und wer einen Weisen gezeugt hat, ist fröhlich darüber.
25 Bari mahaifinka da mahaifiyarka su yi murna; bari wadda ta haife ka tă yi farin ciki!
Laß sich deinen Vater und deine Mutter freuen, und fröhlich sein, die dich geboren hat.
26 Ɗana, ka ba ni zuciyarka bari kuma idanunka su kiyaye hanyoyina,
Gib mir, mein Sohn, dein Herz, und laß deinen Augen meine Wege wohl gefallen.
27 gama karuwa rami ne mai zurfi mace marar aminci matsattsiyar rijiya ce.
Denn eine Hure ist eine tiefe Grube, und eine Ehebrecherin ist ein enger Brunnen.
28 Kamar’yan fashi, takan kwanta tana jira tana kuma ninka rashin aminci a cikin maza.
Auch lauert sie wie ein Räuber, und die Frechen unter den Menschen sammelt sie zu sich.
29 Wa yake wayyo? Wa yake baƙin ciki? Wa yake neman fada? Wa yake gunaguni? Wa yake da raunuka ba dalili? Wa yake da jan idanu?
Wo ist Weh? wo ist Leid? wo ist Zank? wo ist Klagen? wo sind Wunden ohne Ursache? wo sind trübe Augen?
30 Waɗanda suke daɗe suna shan ruwan inabi, waɗanda suke neman ƙoƙon damammen ruwan inabi.
Wo man beim Wein liegt und kommt, auszusaufen, was eingeschenkt ist.
31 Kada ka ƙyifce ido a ruwan inabi sa’ad da ya yi ja, sa’ad da yana da kyan gani a cikin ƙwarya, sa’ad da yana gangarawa sumul a maƙogwaro!
Siehe den Wein nicht an, daß er so rot ist und im Glase so schön steht. Er geht glatt ein;
32 A ƙarshe yana sara kamar maciji da kuma dafi kamar gamsheƙa.
aber danach beißt er wie eine Schlange und sticht wie eine Otter.
33 Idanunka za su riƙa gane-gane, zuciyarka kuma za su riƙa tunani abubuwa masu rikitarwa.
So werden deine Augen nach andern Weibern sehen, und dein Herz wird verkehrte Dinge reden,
34 Za ka zama kamar wanda yake barci a tsakiyar tekuna, kwance a sama itacen jirgin ruwa.
und wirst sein wie einer, der mitten im Meer schläft, und wie einer schläft oben auf dem Mastbaum.
35 Za ka ce “Sun buge ni, amma ban ji ciwo ba! Sun daddoke ni, amma ba na jin zafinsa! Yaushe zan farka don in ƙara shan wani?”
“Sie schlagen mich, aber es tut mir nicht weh; sie klopfen mich, aber ich fühle es nicht. Wann will ich aufwachen, daß ich's mehr treibe?”

< Karin Magana 23 >