< Karin Magana 22 >

1 An fi son suna mai kyau fiye da wadata mai yawa; tagomashi kuma ya fi azurfa ko zinariya.
Ein guter Ruf ist köstlicher denn großer Reichtum, und Gunst besser denn Silber und Gold.
2 Mawadaci da matalauci suna da abu guda. Ubangiji ne Mahaliccinsu duka.
Reiche und Arme müssen untereinander sein; der HERR hat sie alle gemacht.
3 Mai basira kan ga damuwa tana zuwa yă nemi mafaka, amma marar azanci kan yi ta tafiya yă kuma sha wahala.
Der Kluge sieht das Unglück und verbirgt sich; die Unverständigen gehen hindurch und werden beschädigt.
4 Sauƙinkai da tsoron Ubangiji sukan kawo wadata da girmamawa da kuma rai.
Wo man leidet in des HERRN Furcht, da ist Reichtum, Ehre und Leben.
5 A hanyoyin mugu akwai kaya da tarko, amma duk wanda ya kiyaye ransa kan kauce musu.
Stachel und Stricke sind auf dem Wege des Verkehrten; wer sich aber davon fernhält, bewahrt sein Leben.
6 Ka hori yaro a hanyar da ya kamata yă bi, kuma sa’ad da ya tsufa ba zai bar ta ba.
Wie man einen Knaben gewöhnt, so läßt er nicht davon, wenn er alt wird.
7 Mawadaci yakan yi mulki a kan matalauci, mai cin bashi kuwa bawan mai ba da bashi ne.
Der Reiche herrscht über die Armen; und wer borgt, ist des Leihers Knecht.
8 Duk wanda ya shuka mugunta yakan girbe wahala, za a kuma hallaka sandar fushinsa.
Wer Unrecht sät, der wird Mühsal ernten und wird durch die Rute seiner Bosheit umkommen.
9 Mai bayarwa hannu sake shi kansa zai sami albarka, gama yakan raba abincinsa da matalauta.
Ein gütiges Auge wird gesegnet; denn er gibt von seinem Brot den Armen.
10 Ka hori mai ba’a, hatsaniya kuwa za tă yi waje; fitina da zargi kuma za su ƙare.
Treibe den Spötter aus, so geht der Zank weg, so hört auf Hader und Schmähung.
11 Duk mai son tsabtar zuciya wanda kuma jawabinsa mai alheri ne zai zama aminin sarki.
Wer ein treues Herz und liebliche Rede hat, des Freund ist der König.
12 Idanun Ubangiji na lura da sani, amma yakan ƙi kalmomin marar aminci.
Die Augen des HERRN behüten guten Rat; aber die Worte des Verächters verkehrt er.
13 Rago kan ce, “Akwai zaki a waje!” Ko kuma “Za a kashe ni a tituna!”
Der Faule spricht: Es ist ein Löwe draußen, ich möchte erwürgt werden auf der Gasse.
14 Bakin mazinaciya rami ne mai zurfi; duk wanda yake a ƙarƙashin fushin Ubangiji zai fāɗa a ciki.
Der Huren Mund ist eine Tiefe Grube; wem der HERR ungnädig ist, der fällt hinein.
15 Wauta tana da yawa a zuciyar yara, amma sandar horo zai kore ta nesa da su.
Torheit steckt dem Knaben im Herzen; aber die Rute der Zucht wird sie fern von ihm treiben.
16 Duk wanda yake danne matalauta don yă azurta kuma duk wanda yake kyauta ga mawadata, dukansu kan talauta.
Wer dem Armen Unrecht tut, daß seines Guts viel werde, der wird auch einem Reichen geben, und Mangel haben.
17 Ka kasa kunne ka kuma saurara ga maganganu masu hikima; ka yi amfani da abin da nake koyarwa,
Neige deine Ohren und höre die Worte der Weisen und nimm zu Herzen meine Lehre.
18 gama yana da daɗi sa’ad da ka kiyaye su a zuciyarka ka kuma kasance da su a shirye a leɓunanka.
Denn es wird dir sanft tun, wo du sie wirst im Sinne behalten und sie werden miteinander durch deinen Mund wohl geraten.
19 Domin dogarawarka ta kasance ga Ubangiji, ina koya maka yau, har kai ma.
Daß deine Hoffnung sei auf den HERRN, erinnere ich dich an solches heute dir zugut.
20 Ban rubuta maka maganganu talatin ba, maganganun shawara da sani,
Habe ich dir's nicht mannigfaltig vorgeschrieben mit Rat und Lehren,
21 ina koya maka gaskiya da kalmomin da za ka dogara a kai, saboda ka iya ba da amsa daidai ga duk wanda ya aike ka?
daß ich dir zeigte einen gewissen Grund der Wahrheit, daß du recht antworten könntest denen, die dich senden?
22 Kada ka zalunci matalauta a kan suna matalauta kada kuma ka ƙwari wanda ba shi da mai taimako a gaban shari’a,
Beraube den Armen nicht, ob er wohl arm ist, und unterdrücke den Elenden nicht im Tor.
23 gama Ubangiji zai yi magana dominsu zai kuwa washe waɗanda suka washe su.
Denn der HERR wird ihre Sache führen und wird ihre Untertreter untertreten.
24 Kada ka yi abokantaka da mai zafin rai, kada ka haɗa kai da wanda ba shi da wuya ya yi fushi,
Geselle dich nicht zum Zornigen und halte dich nicht zu einem grimmigen Mann;
25 in ba haka ba za ka koyi hanyoyinsa ka kuma sa kanka a tarko.
du möchtest seinen Weg lernen und an deiner Seele Schaden nehmen.
26 Kada ka zama mai ɗaukar lamuni ko ka ba da jingina saboda bashi;
Sei nicht bei denen, die ihre Hand verhaften und für Schuld Bürge werden;
27 gama in ka kāsa biya za a ƙwace gadon da kake kwanciya a kai ma.
denn wo du es nicht hast, zu bezahlen, so wird man dir dein Bett unter dir wegnehmen.
28 Kada ka matsar da shaidar kan iyakar da kakanninka suka kafa.
Verrücke nicht die vorigen Grenzen, die deine Väter gemacht haben.
29 Kana ganin mutumin da yake da gwaninta a cikin aikinsa? Zai yi wa sarakuna hidima; ba zai yi hidima wa mutanen da ba su iya ba.
Siehst du einen Mann behend in seinem Geschäft, der wird vor den Königen stehen und wird nicht stehen vor den Unedlen.

< Karin Magana 22 >