< Karin Magana 2 >

1 Ɗana, in ka yarda da kalmomina ka kuma ajiye umarnaina a cikinka,
Ndodana yami, uba usemukela amazwi ami, ugcine kuwe imilayo yami,
2 kana kasa kunne ga abin da yake na hikima, kana kuma yin ƙoƙari ka fahimce shi,
ukuthi wenze indlebe yakho ilalele inhlakanipho, uthobise inhliziyo yakho ekuqedisiseni,
3 in kuma ka kira ga tsinkaya ka kuma kira da ƙarfi don ganewa,
yebo, uba ukhalela ukuqedisisa, ukhuphele ilizwi lakho ekuzwisiseni,
4 in ka neme shi yadda ake neman azurfa ka kuma neme shi kamar yadda ake neman ɓoyayyiyar dukiya,
uba ukudinga njengesiliva, ukuphenye njengezimpahla eziligugu ezifihliweyo,
5 to, za ka gane tsoron Ubangiji ka kuma sami sanin Allah.
khona uzaqedisisa ukuyesaba iNkosi, uthole ulwazi lukaNkulunkulu.
6 Gama Ubangiji yana ba da hikima, daga bakinsa kuma, sani da ganewa sukan fito.
Ngoba iNkosi inika inhlakanipho; ulwazi lokuqedisisa kuvela emlonyeni wayo.
7 Yana riƙe da nasara a ma’aji don masu yin gaskiya, shi ne mafaka ga waɗanda tafiyarsu ba ta da laifi,
Iyababekela abaqotho inhlakanipho eqotho; iyisihlangu kubo abahamba ngokuqonda,
8 gama yana tsare abin da masu adalci suke bukata yana kuma tsare hanyar amintattunsa.
ukugcina indlela zesahlulelo; izalondoloza indlela zabangcwele bayo.
9 Sa’an nan za ku fahimci abin da yake daidai da abin da yake na adalci da abin da yake gaskiya, da kowace hanya mai kyau.
Khona uzaqedisisa ukulunga, lesahlulelo, lokuqonda; yonke indlela elungileyo.
10 Gama hikima za tă shiga cikin zuciyarka, sani kuma zai faranta maka rai.
Lapho inhlakanipho izangena enhliziyweni yakho, lolwazi lube mnandi emphefumulweni wakho;
11 Tsinkaya za tă tsare ka, ganewa kuma za tă yi maka jagora.
ingqondo izakugcina, ukuqedisisa kukulondoloze;
12 Hikima za tă cece ka daga hanyoyin mugayen mutane, daga kalmomin mutane masu ɓatanci,
ukukophula endleleni embi, emuntwini okhuluma izinto eziphambeneyo;
13 waɗanda suke barin miƙaƙƙun hanyoyi don su yi tafiya a hanyoyi masu duhu,
abatshiya indlela zobuqotho, ukuze bahambe ngendlela zobumnyama;
14 waɗanda suke jin daɗin yin abin da ba shi da kyau suna kuma farin ciki a mugayen ɓatanci,
abathokoza ngokwenza okubi, bejabula ekuphambukeni komubi;
15 waɗanda hanyoyinsu karkatattu ne waɗanda kuma suke cuku-cuku a hanyoyinsu.
abandlela zabo ziphambene, begobile emikhondweni yabo;
16 Zai kiyaye ku kuma daga mazinaciya, daga mace mai lalata, mai ƙoƙarin kama ka da daɗin bakinta,
ukukophula kowesifazana wemzini, kowezizwe okhohlisa ngamazwi akhe;
17 wadda ta bar mijin ƙuruciyarta ta kuma ƙyale alkawarin da ta yi a gaban Allah.
otshiya umngane wobutsha bakhe, ekhohlwa isivumelwano sikaNkulunkulu wakhe;
18 Gama gidanta yana kai ga mutuwa hanyarta kuma ga ruhohin matattu.
ngoba indlu yakhe itshonela ekufeni, lemikhondo yakhe emimoyeni efileyo.
19 Duk wanda ya ziyarce ta ba ya ƙara komowa ba zai ƙara komowa ga hanyar rai.
Bonke abangena kuye kabayikubuya, njalo kabayikufinyelela endleleni zempilo.
20 Don haka dole ku yi tafiya a hanyoyin mutanen kirki ku kuma yi ta bi hanyoyin adalai.
Ukuze uhambe endleleni yabalungileyo, ugcine imikhondo yamalungisa.
21 Gama masu aikata gaskiya za su zauna a cikin ƙasar, marasa laifi kuma za su kasance a cikinta;
Ngoba abaqotho bazahlala elizweni, labapheleleyo basale kulo;
22 amma za a fid da mugaye daga ƙasar, za a tumɓuke marasa aminci kuma daga gare ta.
kodwa abakhohlakeleyo bazaqunywa basuswe elizweni, labaphambekayo badatshulwe basuswe kulo.

< Karin Magana 2 >