< Karin Magana 1 >

1 Karin maganar Solomon ɗan Dawuda, sarkin Isra’ila.
Izaga zikaSolomoni, indodana kaDavida, inkosi yakoIsrayeli;
2 Ga karin magana da za su taimake ka don samun hikima da horo; don ganewa kalmomi masu zurfi;
ukwazi inhlakanipho lokulaywa, ukuqedisisa amazwi okuqedisisa,
3 don neman rayuwa ta horo da kuma ta hankali, kana yin abin da yake daidai, mai adalci da kuma wanda ya dace;
ukwemukela ukulaya kwenhlakanipho, ukulunga, lesahlulelo, lokuqonda;
4 don sa marar azanci yă yi hankali, yă sa matasa su sani, su kuma iya rarrabewa,
ukunika abangelalwazi inhlakanipho, ijaha ulwazi lengqondo.
5 bari masu hikima su saurara, su kuma ƙara ga saninsu, bari masu tunani kuma su sami jagora,
Ohlakaniphileyo uzakuzwa, andise ukufunda, loqedisisayo uzazuza izeluleko,
6 don su fahimci karin magana da kuma misalai, kalmomi da kuma kacici-kacici masu hikima.
ukuqedisisa isaga lomzekeliso, amazwi abahlakaniphileyo, lamalibho abo.
7 Tsoron Ubangiji shi ne masomin ilimi, amma wawaye sun rena hikima da horo.
Ukwesaba iNkosi kuyikuqala kolwazi; izithutha ziyadelela inhlakanipho lokulaywa.
8 Ɗana, ka saurari umarnin mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
Ndodana yami, zwana ukulaya kukayihlo, ungawudeli umlayo kanyoko;
9 Za su zama kayan ado don su inganta ka da kuma sarƙar wuya don su yi wa wuyanka ado.
ngoba kuzakuba ngumqhele womusa ekhanda lakho, lemigaxo entanyeni yakho.
10 Ɗana, in masu zunubi sun jarabce ka, kada ka yarda.
Ndodana yami, uba izoni zikuhuga, ungavumi.
11 In suka ce, “Zo mu tafi; mu yi kwanton ɓauna, mu nemi wani mu kashe, mu fāɗa wa marasa laifi;
Uba zisithi: Hamba lathi, siyecathamela igazi, sicatshele ongelacala kungelasizatho;
12 mu haɗiye su da rai gaba ɗaya kamar kabari, kamar waɗanda suke gangarawa zuwa rami; (Sheol h7585)
sibaginye bephila njengengcwaba, yebo, ngokupheleleyo, njengabehlela egodini. (Sheol h7585)
13 za mu sami dukiya masu daraja iri-iri, mu kuma cika gidajenmu da ganima;
Sizathola yonke impahla eligugu, sigcwalise izindlu zethu ngempango.
14 ka haɗa kai da mu, za mu kuwa raba abin da muka sato”
Phosela inkatho yakho phakathi kwethu; sonke sibe lesikhwama semali sinye.
15 ɗana, kada ka tafi tare da su, kada ka taka ƙafarka a hanyarsu;
Ndodana yami, ungahambi lazo endleleni; unqande unyawo lwakho emkhondweni wazo.
16 gama ƙafafunsu kan yi sauri ga yin zunubi, suna saurin yin kisankai.
Ngoba inyawo zazo zigijimela ebubini, ziphangisa ukuchitha igazi.
17 Ba shi da amfani a kafa tarko a idanun dukan tsuntsaye!
Isibili, imbule lendlalelwa ize phambi kwamehlo aloba yiyiphi inyoni.
18 Waɗannan irin mutane kansu suke kafa wa tarko; ba sa kama kome, sai rayukansu!
Lalaba bacathamela igazi labo, bacatshele imiphefumulo yabo.
19 Dukan waɗanda suke neman ribar da ba a samu a hanya mai kyau; ƙarshen wannan yakan ɗauke rayukansu.
Zinjalo indlela zakhe wonke ozuza inzuzo ngokuphanga; ithatha impilo yabaniniyo.
20 Hikima tana kira da ƙarfi a kan titi, tana ɗaga muryarta a dandalin taron jama’a;
UkuHlakanipha kuyamemeza ngaphandle, kukhupha ilizwi lakho emidangeni.
21 tana kira da ƙarfi a kan tituna masu surutu, tana yin jawabinta a hanyoyin shiga gari.
Kuyamemeza endaweni eqakathekileyo yokuxokozela, ekungeneni kwamasango; emzini kutsho amazwi akho,
22 “Har yaushe ku da kuke marasa azanci za ku ci gaba a hanyoyinku marasa azanci? Har yaushe ku masu ba’a za ku yi ta murna cikin ba’arku wawaye kuma ku ƙi ilimi?
kusithi: Koze kube nini, lina elingelalwazi, lithanda ukungabi lalwazi, labaklolodayo bezifisela ukukloloda, leziphukuphuku zizonda ulwazi?
23 Da a ce kun saurari tsawatata, da na faɗa muku dukan abin da yake zuciyata in kuma sanar da ku tunanina.
Phendukelani ekukhuzeni kwami; khangelani, ngizathululela umoya wami kini, ngilazise amazwi ami.
24 Amma da yake kun ƙi ni sa’ad da na yi kira ba kuma wanda ya saurara sa’ad da na miƙa hannuna,
Ngoba ngibizile, kodwa lala; ngelulile isandla sami, kodwa kakho onanzayo;
25 da yake kun ƙi dukan shawarata ba ku kuma yarda da tsawatata ba,
ladelela sonke iseluleko sami, kalivumanga ukukhuza kwami;
26 Zan yi muku dariya sa’ad da masifa ta same ku, zan yi muku ba’a sa’ad da bala’i ya same ku,
mina-ke ngizahleka ukuchitheka kwenu, ngiklolode ekufikeni kokwesaba kwenu,
27 sa’ad da bala’i ya sha kanku kamar hadiri, sa’ad da masifa ta share ku kamar guguwa, sa’ad damuwa da wahala suka mamaye ku.
ekufikeni kokwesaba kwenu njengesiphepho, lokuchitheka kwenu kufika njengesivunguzane, lapho ubuhlungu losizi kulehlela.
28 “Sa’an nan za su kira gare ni amma ba zan amsa ba; za su neme ni amma ba za su same ni ba.
Khona bazangibiza, kodwa kangiyikusabela; bazangidingisisa, kodwa kabayikungithola.
29 Da yake sun ƙi sani ba su kuwa zaɓi tsoron Ubangiji ba,
Ngenxa yokuthi babezonda ulwazi, bengakhethanga ukwesaba iNkosi.
30 da yake ba su karɓi shawarata ba suka kuwa yi kunnen ƙashi ga tsawatata,
Kabavumanga iseluleko sami, bedelela konke ukukhuza kwami.
31 za su sami sakayyar abubuwan da suka yi su kuma ƙoshi da sakayyar makircinsu.
Ngakho bazakudla okwesithelo sendlela yabo, basuthiswe ngamacebo abo.
32 Gama rashin hankalin marasa azanci zai kashe su, rashin kulawar wawaye kuma zai hallaka su;
Ngoba ukuhlehla kwabangelalwazi kuzababulala, lokonwaba kweziphukuphuku kuzababhubhisa.
33 amma duk wanda ya saurare ni, zai zauna lafiya yă kuma kasance da rai kwance, ba tare da tsoron lahani ba.”
Kodwa ongilalelayo uzahlala evikelekile, onwabe ekwesabeni okubi.

< Karin Magana 1 >