< Ƙidaya 32 >
1 Mutanen Ruben da mutanen Gad, da suke da garken shanu da kuma garke tumaki masu yawa, suka ga cewa ƙasashen Yazer da Gileyad wurare ne masu kyau don kiwon shanu da tumaki.
HE nui loa na holoholona a na mamo a Reubena, a me na mamo a Gada: a i ka manawa i ike ai lakou i ka aina o Iazera a me ka aina o Gileada, aia hoi, he wahi pono ia no na holoholona;
2 Saboda haka suka zo wurin Musa da Eleyazar da kuma shugabannin jama’a, suka ce,
Hele mai la na mamo a Gada a me na mamo a Reubena, a olelo mai la ia Mose, a ia Eleazara ke kahuna, a i na luna o ke anainakanaka, i mai la,
3 “Atarot, Dibon, Yazer, Nimra, Heshbon, Eleyale, Sebam, Nebo da Beyon,
O Atarota, o Dibona, o Iazera, o Nimera, o Hesebona, o Eleale, o Sebama, o Nebo, a o Beona,
4 ƙasar da Ubangiji ya ci da yaƙi a gaban mutane Isra’ila, suna da kyau don dabbobi, bayinku kuma suna da dabbobi.”
O ka aina a Iehova i luku ai imua o ke anainakanaka o ka Iseraela, he aina ia no na holoholona; a he holoholona ia makou o kau poe kauwa.
5 Suka ce, “In mun sami tagomashi daga gare ka bari a ba da wannan ƙasa ga bayinka, tă zama mallakanmu. Kada ka sa mu haye Urdun.”
I mai la lakou, No keia mea, a i loaa ia makou ke aloha imua o kou maka, e ae mai oe e haawiia mai keia aina i wahi e noho ai no kau mau kauwa, aole no e kai aku ia makou ma kela aoao o Ioredane.
6 Musa ya ce wa mutanen Gad da mutanen Ruben, “Wato, sai’yan’uwanku su yi ta yaƙi ku kuwa ku zauna nan?
Ninau aku la o Mose i na mamo a Gada, a i na mamo a Reubena, E hele no anei ko oukou poe hoahanau i ke kaua, a e noho no oukou manei?
7 Don me za ku karya zuciya Isra’ilawa daga hayewa zuwa ƙasar da Ubangiji ya ba su?
No ke aha la hoi e hoonawaliwali ai oukou i na naau o na mamo a Iseraela, i hele ole ai lakou i ka aina a Iehova i haawi mai ai no lakou?
8 Haka iyayenku suka yi sa’ad da na aike su daga Kadesh Barneya don su dubo ƙasar.
Pela no i hana'i ko oukou poe makua, ia'u i hoouna aku ai ia lakou mai Kadesabanea aku e makaikai i ka aina.
9 Gama bayan suka haura Kwarin Eshkol suka hangi ƙasar, sai suka karya zuciyar Isra’ilawa daga shigar ƙasar da Ubangiji ya ba su.
No ka mea, i ka manawa i pii aku ai lakou ma ke awawa o Esekola, a ike aku la i ka aina, hoonawaliwali lakou i ka naau o na mamo a Iseraela, i hele ole aku ai lakou i ka aina a Iehova i haawi mai ai no lakou.
10 A ranar kuwa Ubangiji ya husata har ya yi wannan rantsuwa cewa,
A ua hoaia ka inaina o Iehova ia la, a hoohiki iho la ia, i ka i ana mai,
11 ‘Tabbatacce ba wani daga cikin mutanen da suka fito daga Masar, tun daga mai shekara ashirin zuwa gaba, da zai ga ƙasar da na rantse zan ba Ibrahim, da Ishaku, da Yaƙub, domin ba su bi ni sosai ba,
He oiaio, aole kekahi o na kanaka i hele mai nei mai Aigupita mai, na mea o na makahiki he iwakalua a keu aku, e ike aku i ka aina a'u i hoohiki ai no Aberahama, no Isaaka a no Iakoba; no ka mea, aole lakou i hahai pono mamuli o'u:
12 ba ko ɗaya sai dai Kaleb ɗan Yefunne Bakenizze da Yoshuwa ɗan Nun, don su ne kaɗai suka bi Ubangiji da zuciya ɗaya.’
O Kaleba wale no o ke keiki a Iepune ka Kenezi, laua o Iosua ke keiki a Nuna: no ka mea, ua hahai pono no laua ia Iehova.
13 Ubangiji ya husata da Isra’ila har ya sa suka yi ta yawo a hamada shekara arba’in, sai da dukan tsaran da suka aikata wannan mugunta a gabansa, suka mutu.
A hoaia ka inaina o Iehova i ka Iseraela, a hoauwana ae la oia ia lakou ma ka waonahele i na makahiki he kanaha, a pau loa ae la ka hanauna a pau i hana hewa imua o Iehova.
14 “Ga shi ku kuma, tarin masu zunubi, kuna tsaya a matsayin kakanninku, kuna sa Ubangiji yă sāke husata da Isra’ila.
Aia hoi, ua ku ae nei oukou i pani no ka hakahaka o ko oukou poe makua, he hanauna kanaka hewa, e hoomahuahua aku i ka inaina nui o Iehova i ka Iseraela.
15 In kun juye daga binsa, zai sāke barin dukan wannan mutane a hamada, ku ne kuwa za ku zama sanadin hallakarsu.”
No ka mea, a i huli aku oukou maimuli ona aku, e haalele hou mai auanei oia ia lakou iloko o ka waonahele, a e make keia poe kanaka a pau ia oukou.
16 Sai suka zo wurin Musa, suka ce, “Muna so mu gina katangar dutse don dabbobinmu, da kuma birane don matanmu da’ya’yanmu a nan.
Hele mai lakou a kokoke io na la, i mai la, E hana no makou i na pahipa no ko makou holoholona, a me na kulanakauhale no na keiki a makou:
17 Matanmu da’ya’yanmu za su zauna a biranen da suke da katanga, don kāriya daga mazaunan ƙasar, amma mu, za mu ɗauki makamai mu tafi tare da sauran Isra’ilawa, har mu kai su wuraren zamansu.
Aka, e hele makaukau no makou i ke kaua imua o na mamo a Iseraela a alakai makou ia lakou i ko lakou wahi: a e noho na keiki a makou i na kulanakauhale i paa i ka pa, no na kanaka o ka aina.
18 Ba za mu koma gidajenmu ba sai kowane mutumin Isra’ila ya sami gādonsa.
Aole no makou e hoi hou i na hale o makou, a loaa i kela kanaka i keia kanaka o na mamo a Iseraela kona ainahooili.
19 Ba za mu ci gādo tare da su a wancan hayin Urdun ba, domin mun sami gādonmu a wannan hayin gabashin Urdun.”
No ka mea, aole makou e ai aina me lakou ma kela aoao o Ioredane; a ma o aku; no ka mea, ua loaa ia makou ko makou ainahooili ma keia aoao o Ioredane ma ka hikina.
20 Sai Musa ya ce musu, “In za ku yi haka, in za ku sha ɗamara da makamai a gaban Ubangiji, ku tafi yaƙi,
I aku la o Mose ia lakou, Ina paha oukou e hana ia mea, a e hele me ka makaukau i ke kaua imua o Iehova,
21 in kuma dukanku za ku yi ɗamara, ku ɗauki makaman yaƙi a hayin Urdun a gaban Ubangiji har lokacin da ya kori abokan gābansa daga gabansa,
A e hele oukou a pau me ka makaukau ma kela aoao o Ioredane imua o Iehova, a pau kona poe enemi i ka hookukeia'ku e ia mai kona alo aku,
22 to, sa’ad da aka ci ƙasar a gaban Ubangiji, kwa kuɓuta daga alhakinku ga Ubangiji da kuma Isra’ila. Ƙasan nan kuwa za tă zama mallakarku a gaban Ubangiji.
A pio ka aina imua o Iehova; a mahope iho e hoi hou auanei oukou, me ka hala ole imua o Iehova, imua hoi o ka Iseraela: a e lilo keia aina no oukou imua o Iehova.
23 “Amma in ba ku yi haka ba, kun yi zunubi ke nan ga Ubangiji; kuma ku san cewa zunubinku zai tone ku.
Aka, i hana ole oukou pela, aia hoi, ua hana hewa aku oukou ia Iehova; a e ike pono oukou e pili auanei ko oukou hewa ia oukou iho.
24 Ku gina birane domin matanku da’ya’yanku, ku gina katanga kuma domin dabbobinku, amma fa ku cika abin da kuka yi alkawari.”
E hana oukou i na kulanakauhale no na keiki a oukou, a me na pa no na hipa a oukou; a e hana oukou i ka mea a ko oukou waha i olelo mai ai.
25 Mutanen Gad da mutanen Ruben, suka ce wa Musa, “Mu bayinka za mu yi yadda ranka yă daɗe ya umarta.
Olelo mai la na mamo a Gada, a me na mamo a Reubena, i mai la, E hana no na kauwa au e like me kuu haku i olelo mai nei.
26 ’Ya’yanmu da matanmu, garkunan shanunmu da na tumakinmu, za su kasance a nan biranen Gileyad.
O ka makou poe kamalii, o na wahine a makou, o ko makou holoholona uuku, a me ko makou holoholona nui a pan, e waihoia ilaila maloko o na kulanakauhale o Gileada:
27 Amma bayinka, kowane mutum a cikinmu zai haye a gaban Ubangiji, zuwa yaƙi kamar yadda ranka yă daɗe ya faɗa.”
Aka, a kau poe kauwa, o kela mea keia mea e hele makaukau imua o Iehova i ke kaua, e like me ka olelo ana mai a kuu haku.
28 Sai Musa ya yi wa Eleyazar firist, da Yoshuwa ɗan Nun, da shugabannin gidajen kakannin kabilan mutanen Isra’ila kashedi a kansu,
A kauoha aku la o Mose no lakou ia Eleazara ke kahuna, a me Iosua ke keiki a Nuna, a me na lunakahiko o na ohana mamo a Iseraela:
29 ya ce, “In kowane sojan mutanen Gad da na mutanen Ruben, ya ɗauki makaman yaƙi, ya haye Urdun tare da ku a gaban Ubangiji, to, sa’ad da a ci ƙasar a gabanku, ku ba da ƙasar Gileyad tă zama mallakarsu.
I aku la o Mose ia lakou, Ina e hele pu aku me oukou na mamo a Gada, a me na mamo a Reubena ma kela aoao o Ioredane, o kela kanaka o keia kanaka me ka makaukau i ke kaua imua o Iehova, a e hoopioia ka aina imua o oukou; alaila e haawi oukou i ka aina o Gileada i kuleana no lakou:
30 Amma in ba su haye tare da ku da shirin yaƙi ba, to, sai ku ba su gādo a wancan haye kamar sauran kabilun a Kan’ana.”
A i ole lakou e hele makaukau aku me oukou ma kela aoao, alaila e loaa ia lakou ko lakou kuleana iwaena o oukou ma ka aina o Kanaana.
31 Mutanen Gad da mutanen Ruben suka amsa, suka ce, “Barorinka za su yi abin da Ubangiji ya faɗa.
Olelo mai la na mamo a Gada a me na mamo a Reubena, i mai la, E like me ka Iehova i olelo mai ai i kau poe kauwa, pela no makou e hana aku ai.
32 Za mu haye a gaban Ubangiji zuwa Kan’ana, amma mallakarmu ta gādo, za tă kasance a wannan hayi na Urdun.”
E hele makaukau aku no makou imua o Iehova iloko o ka aina o Kanaana, i lilo ai no makou ka aina o ko makou kuleana ma keia aoao o Ioredane.
33 Sai Musa ya ba wa mutanen Gad, mutanen Ruben, da rabin mutanen Manasse ɗan Yusuf, masarautar Sihon, sarkin Amoriyawa, da masarautar Og na Bashan, dukan ƙasar, tare da biranenta da kuma yankunan da suke kewaye.
A haawi aku la o Mose no lakou, no na mamo a Gada a me na mamo a Reubena, a me ka ohana hapa a Manase a ke keiki a Iosepa, i ke aupuni o Sihona ke alii o ka Amora, a me ke aupuni o Oga ke alii o Basana, i ka aina me na kulanakauhale ona, ma ua palena, na kulanakauhale o ia aina a puni.
34 Mutanen Gad suka gina Dibon, Atarot, Arower,
A kukulu aku la na mamo a Gada ia Dibona, me Atarota, me Aroera,
35 Atrot Shofan, Yazer, Yogbeha,
Me Aterota, me Sopana, me Iazera, a me Iogebeha,
36 Bet-Nimra, da Bet-Haran a matsayin birane masu katanga, suka kuma gina katanga don dabbobinsu.
Me Betenimera a me Beteharana, na kulanakauhale i puni i ka pa, a me na pahipa.
37 Mutanen Ruben suka sāke gina Heshbon, Eleyale, da Kiriyatayim,
A kukulu aku la na mamo a Reubena ia Hesebona, me Eleale, a me Kiriataima,
38 haka kuma suka gina Nebo da Ba’al-Meyon (an canja waɗannan sunaye) suka kuma gina Sibma. Suka ba wa biranen da suka sāke ginawa sunaye.
A me Nebo, me Baalameona, (ua hoololiia ko lakou mau inoa, ) a me Sibema: a mamuli o ua inoa, kapa aku lakou i na inoa o na kulanakauhale a lakou i kukulu ai.
39 Zuriyar Makir ɗan Manasse suka tafi Gileyad, suka ci ta da yaƙi, suka kori mutanen Amoriyawa da suke can.
A hele aku la na keiki a Makira ke keiki a Manase i Gileada, a lawe pio iho la ia wahi, a hookuke aku la i ka Amora e noho ana iloko olaila.
40 Saboda haka Musa ya ba da Gileyad ga mutanen Makir, zuriyar Manasse, suka kuma zauna a can.
A haawi aku la o Mose ia Gileada ia Makira ke keiki a Manase, a noho iho la ia ilaila.
41 Yayir, wani ɗan Manasse, ya ci ƙauyukansu da yaƙi, ya kuma ba su sunan Hawwot Yayir.
Hele aku la hoi o Iaira ke keiki a Manase, a lawe pio aku la i na kauhale o ia wahi, a kapa aku la i ko lakou inoa, o Havota-iaira.
42 Noba kuma ya ci Kenat da ƙauyukanta da yaƙi, ya kuma ba ta suna Noba, bisa ga sunansa.
A hele aku la o Noba a lawe pio aku la ia Kenata, a me na kauhale ona, a kapa aku ia wahi, o Noba, mamuli o kona inoa iho.