< Nehemiya 1 >

1 Kalmomin Nehemiya ɗan Hakaliya. A cikin watan Kisleb a shekara ta ashirin, yayinda nake a fadar Shusha.
[I am] Nehemiah, the son of Hacaliah. [I am writing] this account [of what I did when I returned to Jerusalem. After King Artaxerxes had been ruling the Persian Empire] for almost 20 years, near the end of that year, I was in Susa, the capital [of Persia].
2 Hanani, ɗaya daga cikin’yan’uwana, ya zo daga Yahuda tare da waɗansu mutane. Na kuwa tambaye shi game da raguwar Yahudawan da suka tsira daga kwasan zuwa zaman bauta, da kuma game da Urushalima.
My brother Hanani came to visit me. He and some other men had just returned from Judah. I queried them about the Jews who were living there, whose [parents] had been (exiled/taken forcefully) [to Babylonia many years previously]. I also asked them about [what was happening in] Jerusalem.
3 Suka ce mini, “Waɗanda suka tsira daga kwasan zuwa zaman bauta da kuma suka komo cikin yankin suna cikin babban damuwa da wulaƙanci. An rushe katangar Urushalima aka kuma ƙone ƙofofin da wuta.”
They said to me, “The Jews in Jerusalem who returned there from Babylonia are living in a very difficult situation. The walls of the city have been broken down, and even the city gates have been burned down.”
4 Da na ji waɗannan abubuwa, sai na zauna na yi kuka. Na yi kwanaki ina makoki da azumi, na kuma yi addu’a a gaban Allah na sama.
When I heard that, I sat down and cried. For several days I mourned, and I (fasted/abstained from eating food), and I prayed to our God, [who is/rules] in heaven.
5 Na ce, “Ya Ubangiji Allah na sama, Allah mai girma da mai banrazana, wanda yake kiyaye alkawarinsa na ƙauna da waɗanda suke ƙaunarsa, suke kuma yin biyayya da umarnansa,
I said, “Yahweh, [you who are/rule] in heaven, you are a wonderful and awesome God. You keep your promise to faithfully love those who love you and who obey your commands.
6 ka sa kunne ka kuma buɗe idanunka ka ji addu’ar da bawanka yake yi a gabanka dare da rana saboda bayinka, mutanen Isra’ila. Na furta zunuban da mu Isra’ilawa, har da ni da kuma gidan mahaifina muka yi maka.
Now please look down and listen to what I am praying. I pray during the day and at night for your Israeli people. I confess that we Israeli people have sinned. Even my family and I have sinned against you.
7 Mun yi mugunta gare ka. Ba mu yi biyayya da umarnai, ƙa’idodi da kuma dokokin da ka ba wa bawanka Musa ba.
We have acted very wickedly. [Many years ago] your servant Moses gave us your laws and all the things you commanded us to do [DOU], but we have not obeyed/done them.
8 “Ka tuna da umarnan da ka ba wa bawanka Musa, kana cewa, ‘In kun yi rashin aminci, zan warwatsar da ku a cikin al’ummai,
“But please remember what you told your servant Moses. You said, ‘If you sin, I will scatter you among the ([heathen nations/nations that do not believe in me]).
9 amma in kuka dawo gare ni kuka kuma yi biyayya da umarnaina, to, ko mutanenku da aka kwasa zuwa zaman bauta suna can wuri mafi nisa, zan tattara su daga can in kawo su wurin da na zaɓa yă zama wurin zama don Sunana.’
But if you return to me and obey my commands, even if you have been exiled to very remote/distant places on the earth, I will bring you back here [to Israel], the land that I [MTY] have chosen to be honored in.’
10 “Su bayinka ne da kuma mutanenka da ka fansa ta wurin ƙarfinka mai girma da kuma hannunka mai iko.
“We are your servants. We are the people whom you brought here by your very great power [MTY, DOU]
11 Ya Ubangiji, ka kasa kunne ga addu’ar wannan bawanka da kuma ga addu’ar bayinka waɗanda suke farin cikin girmama sunanka. Ka ba wa bawanka nasara a yau ta wurinsa yă sami tagomashi a gaban wannan mutum.” Ni ne mai riƙon kwaf sarki.
Yahweh, please hear this prayer of mine, and the prayers of all your people who are delighted to revere you [MTY]. Today I will go to the king, to request that he do me a great favor. Please motivate him to act kindly toward me, in order that I will be successful [in obtaining what I want].” At that time, I was the one whose work was to taste all the food and drink before it was served to the king, [to be sure that no one had put poison in it].

< Nehemiya 1 >