< Ayuba 18 >

1 Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
Then Bildad replied [again]:
2 “Yaushe za ka gama maganganun nan? Ka dawo da hankalinka sa’an nan za mu iya yin magana.
“When are you going to stop talking [RHQ]? If you would stop talking and listen, we could tell you something.
3 Don me muke kamar shanu a wurinka, ka ɗauke mu mutanen wofi?
Why do you think that we are [as stupid] as cattle? [DOU, RHQ]
4 Kai da ka yayyage kanka don haushi, za a yashe duniya saboda kai ne? Ko kuma duwatsu za su matsa daga wurinsu?
By being [very] angry and hurting yourself, do you think that doing that will shake the earth, or cause the rocks in the mountains to move? [RHQ]?
5 “An kashe fitilar mugu; harshen wutarsa ya daina ci.
“What will happen is that the lives of wicked people [like you] end [as quickly as we can] put out a light or extinguish the flame of a fire.
6 Wutar cikin tentinsa ta zama duhu; fitilar da take kusa da shi ta mutu.
And when the lamps above them [in their tents] are extinguished, there will be no light in those tents.
7 Ƙarfin takawarsa ya ragu; dabararsa ta ja fāɗuwarsa.
[For many years] they walked confidently, but later [in life it was as though] they stumbled and fell, because [they themselves did not heed] the advice [that they gave to others].
8 Ƙafafunsa sun kai shi cikin raga, yana ta yawo a cikin ragar.
[It was as though] they walked into their own net or fell into a pit that they themselves have dug.
9 Tarko ya kama ɗiɗɗigensa; tarko ya riƙe shi kam.
[It was as though] a trap grabbed their heels and held them fast [DOU],
10 An ɓoye masa igiya da za tă zarge shi a ƙasa; an sa masa tarko a kan hanyar da zai bi.
[as though the noose of] a rope that was hidden on the ground, [whose other end was fastened to the limb of a tree], seized them when they walked into it.
11 Tsoro duk ya kewaye shi ta kowane gefe yana bin shi duk inda ya je.
Everywhere they went, there were things that caused them to be terrified; [it was as though] those things were pursuing them and biting at their heels.
12 Masifa tana jiransa; bala’i yana shirye yă fāɗa masa a lokacin da zai fāɗi.
They became hungry, with the result that they had no strength. They experienced disasters [PRS] constantly.
13 Ya cinye wani sashe na gaɓar jikinsa; ɗan fari na mutuwa ya cinye ƙafafunsa.
Diseases spread all over their skin/bodies; diseases that (caused their bodies to decay/destroyed their arms and legs).
14 An yage shi daga zaman lafiyar da yake yi a cikin tentinsa aka sa shi tsoro sosai.
[When they died, ] they were snatched away from their tents and brought to the one who rules over the dead.
15 Wuta ta cinye tentinsa; farar wuta ta rufe wurin da yake zama.
Now their tents will burn down, when burning sulfur rains down on those tents!
16 Jijiyoyinsa sun bushe a ƙasa rassansa sun mutu a sama.
[Because those who died had no descendants], they were [like trees whose] roots have dried up and whose branches have all withered [MET].
17 An manta da shi a duniya; ba wanda yake ƙara tunawa da shi.
No one on the earth will remember them any more; no [one on any] street [will even remember] their names [MTY].
18 An tura shi daga cikin haske zuwa cikin duhu, an kore shi daga duniya.
They will be expelled from the earth where there is light, and they will be sent into the place where it is dark.
19 Ba shi da’ya’ya ko zuriya cikin mutanensa, ba sauran wanda yake a raye a wurin da ya taɓa zama.
They will have no children or grandchildren, no descendants where they previously lived.
20 Mutanen Yamma suna mamakin abin da ya faru da shi; tsoro ya kama mutanen gabas.
People from the east to the west [who hear about what happened to them], will be shocked and horrified.
21 Ba shakka haka wurin zaman mugun mutum yake, haka wurin zaman wanda bai san Allah ba yake.”
And that is what happens to ungodly/sinful people [like you], to people who (have no interest in/have rejected) God.”

< Ayuba 18 >