< Nehemiya 4 >

1 Da Sanballat ya ji cewa muna sāke ginin katangar, sai ya husata, ya haukace ƙwarai. Ya yi wa Yahudawa dariya,
When Sanballat heard that we were rebuilding the city wall, he was very angry. He was enraged/furious. He made fun of us Jews.
2 a gaban abokansa da kuma sojojin Samariya ya ce, “Me waɗancan Yahudawan nan marasa ƙarfi suke yi? Za su maido da katangarsu ne? Za su miƙa hadayu ne? Za su gama a rana ɗaya? Za su iya samun duwatsun gini daga tsibin matattun duwatsu?”
While his colleagues and officials of the army troops who had come from Samaria were listening, he said, “What do these feeble/pathetic Jews [think they] are doing? Do they think that if they offer enough/many sacrifices, [their gods will hear them and enable] them to finish building the wall in one day? The stones [that were in the wall previously have been weakened by] being burned in a fire. Those stones that they are pulling out of the rubbish/garbage heaps—do they think that they can make them strong again?” [RHQ]
3 Tobiya wakilin mutanen Ammon wanda yake a gefensa ya ce, “Abin nan da suke gini, ko dila ma ya hau, zai rushe shi!”
Tobiah was [standing] beside Sanballat. He said, “That stone wall [that they are building] is very weak; so if even a fox climbed up on it, the wall would fall down!”
4 Ka ji mu, ya Allahnmu, gama an rena mu. Bari zagin da suke yi mana yă koma kansu. Ka sa a kwashe su a kai su bauta a wata ƙasa.
Then I prayed. I said, “Our God, hear us, because they are ridiculing us! Cause the words of their insults to fall back on them! Allow their enemies to come and capture them and force them to go to a foreign land!
5 Kada ka rufe laifinsu, kada kuwa ka gafarta musu, gama sun ci mutuncinmu, mu da muke gini.
They are guilty; they have [said things that] caused you to be angry while the people here who are building the wall are listening; so punish them!”
6 Sai muka sāke ginin katangar sai da duka ta kai rabin tsayinta, gama mutane sun yi aiki da dukan ƙarfinsu.
But after some time, we finished building the wall around the whole city, up to half as high as the first wall had been. We were able to do that because we worked very hard.
7 Amma da Sanballat, da Tobiya, da Larabawa, da Ammonawa, da kuma mutanen Ashdod suka ji cewa gyare-gyaren katangar Urushalima yana cin gaba, ana kuma tattoshe wuraren da suka tsattsaga, sai suka husata ƙwarai.
But when Sanballat, Tobiah, the men from Arabia, the people from the Ammon [people-group] and from Ashdod [city] heard that the work on the wall was continuing and that we were filling in the gaps in the wall, they became very angry.
8 Dukansu suka ƙulla su zo, su yi yaƙi da Urushalima, su tā da hankali a cikinta.
They all planned to come and fight against the people of Jerusalem [MTY] and to cause trouble.
9 Amma muka yi addu’a ga Allahnmu muka kuma sa masu tsaro da rana da kuma dare don mu magance wannan barazana.
But we prayed to our God [to protect us], and we put men [around the walls] to guard [the city] day and night.
10 Ana cikin haka, mutane a Yahuda suka ce, “Ƙarfin ma’aikata yana kāsawa, akwai kuma sauran tarkace da yawa da ba za mu iya sāke gina katangar ba.”
Then the people of [MTY] Judah started to say, “The men who are working [on the wall] are becoming very tired. There is a lot of [heavy] rubble that we must remove; we ourselves cannot finish the work.
11 Abokan gābanmu sun ce, “Ba za su sani ba, ba kuwa za su gan mu ba, sai dai kawai su gan mu a cikinsu, za mu karkashe su, mu tsai da aikin.”
“Besides, our enemies are saying, ‘Before the Jews see us, we will swoop down on them and kill them and stop their work [on the wall]!’”
12 Sau da yawa Yahudawan da suke da zama kusa da abokan gābanmu sun yi ta zuwa suna yin mana magana, suna cewa “Ko’ina muka juya, za su fāɗa mana.”
The Jews who were living near our enemies came and told us many times, “You should leave the city and go to other places, in order that your enemies will not attack you!”
13 Saboda haka na sa jama’a su ja ɗamara bisa ga iyalinsu a bayan katanga, a wuraren da ba a gina ba. Suna riƙe da takuba, da māsu, da bakkuna.
So I put guards at the places where the wall was not very high yet and at places where there were gaps in the wall. I put guards to protect each of their family groups. I gave the guards daggers, spears, and bows [and arrows].
14 Bayan na dudduba abubuwa, sai na miƙe tsaye na ce wa manyan gari da shugabanni da kuma sauran jama’a, “Kada ku ji tsoronsu. Ku tuna da Ubangiji, wanda yake mai girma da banrazana, ku yi yaƙi don’yan’uwanku, da’ya’yanku maza da mata, da matanku da kuma gidajenku.”
Then after I inspected everything, I summoned the leaders and [other] officials and [many of] the other people, and I said to them, “Do not be afraid of our enemies! Think about [what] Yahweh, who is great and glorious, [can do]! And fight to protect your friends, your families, and your homes!”
15 Da abokan gābanmu suka ji muna sane da shirinsu, Allah kuma ya wargaje shirin nan, sai duk muka dawo ga katangar, kowa ya kama aikinsa.
Our enemies heard that we knew what they were planning to do and that God had (spoiled their plans/prevented them from doing what they planned). [But we were sure that God would defend us, ] so we all started to work on the wall again.
16 Daga wannan rana zuwa gaba, rabin mutane suka yi aiki, yayinda sauran rabin suka kintsa da māsu, da garkuwa, da bakkuna da makamai. Shugabanni suka goyi bayan dukan mutanen Yahuda
But after that, only half of the men who were working for me worked on the wall. The others stood there on guard, holding their spears, shields, bows [and arrows], and [wearing their] coats made of metal plates. [To encourage the people] were building the wall, their leaders stood behind them.
17 waɗanda suke ginin katanga. Waɗanda suke ɗaukan kaya suka yi aikinsu da hannu ɗaya, suna kuma riƙe da makami a ɗaya hannun,
Those who carried [baskets of supplies on their heads/shoulders] and those who built the wall did their work with one hand, and held a weapon with the other hand.
18 kuma kowane mai gini ya ɗaura takobinsa a gefe yayinda yake aiki. Amma mutum mai busa ƙaho ya kasance tare da ni.
All those who were building [the wall] had a dagger fastened to their side. The man who would blow the trumpet [if our enemies attacked] was standing at my side.
19 Sai na ce wa manyan gari, da shugabanni, da sauran jama’a, “Aikin nan babba ne kuma mai yawa, ga shi muna a rarrabe nesa da juna a katangar.
Then I said to the officials, the other important men, and the other people, “This wall is very long, and we are far apart from each other along the wall.
20 Duk inda kuka ji an busa ƙaho, sai ku taru a wurin. Allahnmu zai yi yaƙi dominmu!”
If you hear the man blowing the trumpet, gather around us at that place. [Remember that] our God will fight for us!”
21 Saboda haka muka ci gaba da aiki, rabin mutane suna riƙe da māsu, daga wayewar gari har zuwa fitowar taurari.
So we continued to work. Half of the men continued to hold their spears all day, from when the sun rose [in the morning] until the stars appeared [at night].
22 A wannan lokaci na kuma ce wa mutane, “A sa kowane mutum da mataimakinsa su zauna a Urushalima da dare, domin a yi tsaro da dare, da safe kuma a kama aiki.”
At that time, I also said to the people, “Tell every worker and his helper that they must stay inside Jerusalem at night. By doing that, they can guard us at night, and they can work [on the wall] during the daytime.”
23 Saboda haka ni, da’yan’uwana, da bayina, da matsaran da suke tare da ni, ba wanda ya tuɓe tufafinsa; kowa ya rataye makaminsa, ko ya je shan ruwa ma.
During that time, none of us ever took off our clothes (OR, we wore our clothes all the time)—I and my relatives and my workers and the guards who were with me. And we had our weapons with us, in our hands.

< Nehemiya 4 >