< Ezra 1 >

1 A shekara ta farko ta mulkin sarkin Farisa, wato, sarki Sairus, domin a cika maganar Ubangiji da aka yi ta bakin Irmiya, sai Ubangiji ya taɓa zuciyar Sairus sarkin Farisa ya yi shela a duk fāɗin ƙasarsa, ya kuma rubuta cewa,
During the first year that Cyrus ruled [the] Persian [Empire], he did something that fulfilled what Jeremiah had prophesied. Yahweh motivated Cyrus to write this message, and then Cyrus sent this message throughout his empire:
2 “Ga abin da Sairus sarkin Farisa yake shela, “‘Ubangiji Allah na sama ya ba ni iko in yi mulkin duniya duka, ya kuma zaɓe ni in gina masa haikali a Urushalima cikin Yahuda.
“I, King Cyrus, who rule [the] Persian [Empire], declare this: 'Yahweh, the God [who is in/rules] from heaven, has caused me to become the ruler of all the kingdoms [that I know about] on the earth. And he has appointed me [to enable his people] to build a temple for him in Jerusalem, in Judah [land].
3 Duk wanda yake nasa a cikinku bari Allahnsa yă kasance tare da shi, bari yă tafi Urushalima cikin Yahuda yă gina haikalin Ubangiji, Allah na Isra’ila, Allah wanda yake a Urushalima.
All you people who belong to God may go up to Jerusalem to rebuild this temple for Yahweh, the God who lives in Jerusalem, the God [who is worshiped by you] Israeli people. I desire/hope that your God will be with you [and help those who go there].
4 Duk inda akwai mutumin Yahuda da ya rage, sai mutanen da suke zama kusa da shi, su taimake shi da azurfa, da zinariya, da kaya, da kuma dabbobi, tare da kyautai na yardar rai saboda Gidan Allah wanda yake a Urushalima.’”
Those people who are in places where Israelis are living, whose ancestors were exiled here, should contribute silver and gold to those who go. They should also give them supplies [that they will need for the journey to Jerusalem]. They should also give them some livestock, and gifts of money to help build the temple of God in Jerusalem.'”
5 Sai shugabannin zuriyar Yahuda da na Benyamin, da firistoci da Lawiyawa, duk wanda Allah ya taɓa zuciyarsa, suka shirya don su je su gina haikalin Ubangiji a Urushalima.
Then God motivated some of the priests and (Levites/men who did work in the temple) and some of the leaders of the tribes that were descended from Judah and Benjamin to return to Jerusalem. Those whom God motivated got ready to return to Jerusalem and build the temple for Yahweh there.
6 Dukan maƙwabtansu kuwa suka taimake su da gudummawa na kayan azurfa da na zinariya, da kaya, da dabbobi, da kuma kyautai masu daraja bisa bayarwar yardar rai da suka yi.
All of their neighbors helped them by giving them things made of silver and things made of gold, and supplies for the journey, and livestock. They also gave them other valuable gifts, and also gave them money [to buy things for building the temple].
7 Sai sarki Sairus ya fitar da kayan da suke na haikalin Ubangiji waɗanda Nebukadnezzar ya kwashe daga Urushalima ya sa a haikalin allahnsa.
King Cyrus brought out the valuable things that King Nebuchadnezzar’s [soldiers] had taken from the temple of Yahweh in Jerusalem and put in the temple of Nebuchadnezzar’s gods [in Babylon].
8 Sairus sarkin Farisa ya sa Mitredat ma’aji ya ƙirga su a gaban Sheshbazzar ɗan sarkin Yahuda.
Cyrus commanded Mithredath, the treasurer of [the] Persian [Empire], to count all these items and then give them to Sheshbazzar, the leader of [the group that was going to return to] Judah.
9 Ga lissafin kayan. Manyan kwanonin zinariya guda 30 Manyan kwanonin azurfa guda 1,000 Wuƙaƙe guda 29
This is a list of the items that Cyrus donated: 30 large gold dishes 1,000 large silver dishes 29 silver (censers/incense burning pans)
10 Waɗansu kwanonin zinariya guda 30 Waɗansu kwanonin azurfa guda 410 da waɗansu kayayyaki guda 1,000
30 gold bowls 410 silver bowls 1,000 other items.
11 Dukan kayayyakin zinariya da na azurfa sun kai 5,400. Sheshbazzar ya kawo kayayyakin nan duka tare da shi lokacin da kamammun suka hauro daga Babilon zuwa Urushalima.
All together, there were 5,400 items made of silver or gold, that [were given to] Sheshbazzar [to] take with him when he and the others returned to Jerusalem.

< Ezra 1 >