< Nehemiya 3 >

1 Eliyashib babban firist da’yan’uwansa firistoci suka tashi suka sāke gina Ƙofar Tumaki. Suka tsarkake ta, suka sa ƙofofinta a wurarensu, suka yi ginin har Hasumiyar Ɗari, wadda suka tsarkake, da kuma Hasumiyar Hananel.
Eliasib donc, le grand Sacrificateur se leva, avec ses frères les sacrificateurs, et ils rebâtirent la porte du bercail, laquelle ils sanctifièrent, et ils y posèrent ses portes, et ils la sanctifièrent jusqu'à la tour de Méah, jusqu'à la tour de Hananéël.
2 Mutanen Yeriko kuwa suka kama ginin daga mahaɗin, Zakkur ɗan Imri kuma ya fara ginin biye da su.
Et à son côté rebâtirent les gens de Jérico; et à côté d'eux Zaccur, fils d'Imri, rebâtit.
3 ’Ya’yan Hassenaya ne suka gina Ƙofar Kifi. Suka kafa ginshiƙan, suka kuma sa ƙofofinta, da sakatunta, da kuma sandunan ƙarfenta a wurarensu.
Et les enfants de Sénaa rebâtirent la porte des poissons, laquelle ils planchéièrent, et y mirent ses portes, ses serrures et ses barres.
4 Kusa da su kuma, Meremot ɗan Uriya, ɗan Hakkoz ne ya yi gyare-gyaren. Biye da shi kuma sai Meshullam ɗan Berekiya, ɗan Meshezabel ya yi gyare-gyare. Kusa da shi Zadok ɗan Ba’ana shi ma ya yi gyare-gyare.
Et à leur côté répara Mérémoth, fils d'Urija, fils de Kots; et à leur côté répara Mésullam, fils de Bérecia, fils de Mésézabéël, et à leur côté répara Tsadok, fils de Bahana.
5 Mutanen Tekowa ne suka yi gyare-gyare biye da shi, amma manyan garinsu suka ƙi su sa hannu cikin aikin da shugabanninsu suka bayar.
Et à leur côté réparèrent les Tékohites; mais les plus considérables d'entre eux ne se rangèrent point à l'œuvre de leur Seigneur.
6 Yohiyada ɗan Faseya, da Meshullam ɗan Besodehiya ne suka gyara Ƙofar Yeshana. Suka kafa katakanta, suka sa ƙyamarenta, da sandunan ƙarfe na kulle ƙofofinta.
Et Jéhojadah, fils de Paséah, et Mésullam, fils de Bésodia, réparèrent la porte vieille, laquelle ils planchéièrent, et ils y mirent ses portes, ses serrures et ses barres.
7 Biye da su, mutanen Gibeyon da Mizfa Melatiya na Gibeyon da Yadon Meronot waɗanda suke ƙarƙashin ikon gwamnan Kewayen Kogin Yuferites ne suka yi gyare-gyaren.
Et à leur côté réparèrent Mélatia Gabaonite, et Jadon Méronothite, de Gabaon et de Mitspa, vers le siège du Gouverneur de deçà le fleuve.
8 Uzziyel ɗan Harhahiya, ɗaya daga cikin masu ƙeran zinariya ne ya yi gyare-gyaren sashe na biye; sai Hananiya, ɗaya daga cikin masu yin turare, ya yi gyare-gyaren biye da wannan. Suka gyara Urushalima har zuwa Katanga Mai Faɗi.
Et à côté de ce [siège] répara Huziël, fils de Harhaja, d'[entre] les orfèvres; et à son côté répara Hanania fils de Harakkahim; et ainsi ils relevèrent Jérusalem jusqu'à la muraille large.
9 Refahiya ɗan Hur, mai mulkin rabin yankin Urushalima, ya yi gyare-gyaren sashe na biye.
Et à leur côté répara Réphaja, fils de Hur, capitaine d'un demi-quartier de Jérusalem;
10 Kusa da Refahiya, Yedahiya ɗan Harumaf ya yi gyare-gyaren daga gaban gidansa, sai Hattush ɗan Hashabnehiya ya yi gyare-gyaren biye da shi.
Et à leur côté répara Jédaja, fils de Harumaph, même à l'endroit de sa maison; et à son côté répara Hattus, fils de Hasabnéja.
11 Malkiya ɗan Harim, da Hasshub ɗan Fahat-Mowab ya yi gyare-gyaren wani sashe da kuma Hasumiyar Wurin Gashi.
Et Malkija, fils de Harim, et Hasub, fils de Pahath-Moab, en réparèrent autant, et même la tour des fours.
12 Shallum ɗan Hallohesh, mai mulkin ɗayan rabin yankin Urushalima ya yi gyare-gyaren sashe na biye tare da taimakon’ya’yansa mata.
Et à leur côté Sallum, fils de Lobès, capitaine de [l'autre] demi-quartier de Jérusalem, répara, lui et ses filles.
13 Hanun da mazaunan Zanowa ne suka gyara Ƙofar Kwari. Suka sāke gina ta suka sa ƙofofinta, da sakatunta, da sandunan ƙarfenta a wurarensu. Suka kuma gyara yadi ɗari biyar na katangar har zuwa Ƙofar Juji.
Et Hanun et les habitants de Zanoah réparèrent la porte de la vallée, ils la rebâtirent, et mirent ses portes, ses serrures, et ses barres, et [ils bâtirent] mille coudées de muraille, jusqu'à la porte de la fiente,
14 Malkiya ɗan Rekab mai mulkin yankin Bet-Hakkerem ne ya yi gyare-gyaren Ƙofar Juji. Ya sāke gina ta ya kuma sa sakatunta, da sanduna ƙarfenta a wurarensu.
Et Malkija, fils de Réchab, capitaine du quartier de Beth-Kérem, répara la porte de la fiente; il la rebâtit, et mit ses portes, ses serrures et ses barres.
15 Shallum ɗan Kol-Hoze mai mulkin Mizfa ne ya yi gyare-gyaren Ƙofar Maɓuɓɓuga. Ya sāke gina ta, ya yi mata jinƙa yana sa ƙofofinta, da sakatunta, da kuma sandunan ƙarfenta a wurarensu. Ya kuma gyara katangar tafkin Silowam, ta Lambun Sarki, har zuwa matakalan da suka gangara daga Birnin Dawuda.
Et Sallum, fils de Col-Hoze, capitaine du quartier de Mitspa, répara la porte de la fontaine; il la rebâtit, et la couvrit, et mit ses portes, ses serrures, et ses barres; et [il répara aussi] la muraille de l'étang de Sélah, tirant vers le jardin du Roi, et jusqu'aux degrés qui descendent de la Cité de David.
16 Gaba da shi, Nehemiya ɗan Azbuk, mai mulkin rabin yankin Bet-Zur ne ya yi gyare-gyaren har zuwa kusa da kaburburan Dawuda, har zuwa haƙaƙƙen tafki da kuma Gidan Jarumawa.
Après lui répara Néhémie, fils d'Hazbuk, capitaine du demi-quartier de Beth-Tsur, jusqu'à l'endroit des sépulcres de David, et jusqu'à l'étang qui avait été refait, et jusqu'à la maison des forts.
17 Biye da shi, Lawiyawa a ƙarƙashin Rehum ɗan Bani ne suka yi gyare-gyaren. Kusa da su, Hashabiya mai mulkin rabin yankin Keyila ne ya yi gyare-gyaren don yankinsa.
Après lui réparèrent les Lévites, Néhum, fils de Bani; et à son côté répara Hasabja, capitaine du demi-quartier de Kéhila, pour ceux de son quartier.
18 Biye da shi,’yan’uwansu Lawiyawa ne a ƙarƙashin Binnuyi ɗan Henadad, mai mulkin ɗayan rabin yankin Keyila suka yi gyare-gyaren.
Après lui réparèrent leurs frères, [savoir], Bavvaï, fils de Hénadad, capitaine de [l'autre] demi-quartier de Kéhila.
19 Biye da su, Ezer ɗan Yeshuwa, mai mulkin Mizfa, ya yi gyara wani sashe, daga inda yake fuskantar hawan gidan makamai har zuwa kusurwa.
Et à son côté Héser, fils de Jésuah, capitaine de Mitspa, en répara autant, à l'endroit par où l'on monte à l'arsenal de l'encoignûre.
20 Biye da shi, Baruk ɗan Zakkai da ƙwazo ya gyara wani sashe, daga kusurwa zuwa mashigin gidan Eliyashib babban firist.
Après lui Baruch, fils de Zaccaï, prit courage, et en répara autant, depuis l'encoignûre jusqu'à l'entrée de la maison d'Eliasib, grand Sacrificateur.
21 Biye da shi, Meremot ɗan Uriya, ɗan Hakkoz, ya yi gyaran wani sashe, daga mashigin gidan Eliyashib zuwa ƙarshensa.
Après lui Mérémoth, fils d'Urija, fils de Kots, en répara autant, depuis l'entrée de la maison d'Eliasib, jusqu'au bout de la maison d'Eliasib.
22 Firistoci daga kewayen yankin ne suka yi gyare-gyaren biye da shi.
Et après lui réparèrent les Sacrificateurs, habitants de la campagne.
23 Can gaba da su, Benyamin da Hasshub ne suka yi gyare-gyaren a gaban gidansu, biye da su kuwa, Azariya ɗan Ma’asehiya, ɗan Ananiya ne ya yi gyare-gyaren kusa da gidansa.
Après eux, Benjamin et Hasub réparèrent à l'endroit de leur maison. Après lesquels, Hazaria, fils de Mahaséja, fils d'Hanania, répara auprès de sa maison.
24 Biye da shi, Binnuyi ɗan Henadad ya yi gyaran wani sashe, daga gidan Azariya zuwa kusurwa,
Après lui, Binnuï, fils de Henadad, en répara autant, depuis la maison d'Hazaria, jusqu'à l'encoignûre, même jusqu'au coin.
25 sai Falal ɗan Uzai ya yi aiki ɗaura da kusurwa da kuma doguwar hasumiya daga fadar da take bisa kusa da shirayin masu tsaro. Biye da shi, Fedahiya ɗan Farosh
[Et] Palal, fils d'Uzaï, depuis l'endroit de l'encoignûre, et de la tour, qui sort de la haute maison du Roi, qui est auprès du parvis de la prison. Après lui Pédaja, fils de Parhos.
26 da masu hidimar haikali da suke zama a tudun Ofel ne suka yi gyare-gyaren har zuwa wani wuri ɗaura da Ƙofar Ruwa wajen gabas da kuma doguwar hasumiya.
Et les Néthiniens, qui demeuraient en Hophel, [réparèrent] vers l'Orient, jusqu'à l'endroit de la porte des eaux, et vers la tour qui sort en dehors.
27 Biye da su, mutanen Tekowa suka yi gyaran wani sashe, daga babbar doguwar hasumiya zuwa katangar Ofel.
Après eux, les Tékohites en réparèrent autant, depuis l'endroit de la grande tour qui sort en dehors, jusqu'à la muraille d'Hophel.
28 Daga Ƙofar Doki, firistoci ne suka yi gyare-gyaren, kowanne a gaban gidansa.
Et les Sacrificateurs réparèrent depuis le dessus de la porte des chevaux, chacun à l'endroit de sa maison.
29 Biye da su, Zadok ɗan Immer ya yi gyare-gyaren ɗaura da gidansa. Biye da shi, Shemahiya ɗan Shekaniya, mai tsaron Ƙofar Gabas ya yi gyare-gyare.
Après eux Tsadok, fils d'Immer, répara à l'endroit de sa maison. Et après lui répara Sémahia, fils de Sécania, garde de la porte Orientale.
30 Biye da shi, Hananiya ɗan Shelemiya, da Hanun, ɗa na shida na Zalaf, suka gyara wani sashe. Biye da su, Meshullam ɗan Berekiya ya yi gyare-gyaren ɗaura da wurin zamansa.
Après lui Hanania, fils de Sélemia, et Hanun le sixième fils de Tsalaph, en réparèrent autant. Après eux, Mésullam, fils de Bérécia, répara à l'endroit de sa chambre.
31 Biye da shi, Malkiya, ɗaya daga cikin masu ƙera zinariya ya yi gyare-gyaren har zuwa gidan masu hidimar haikali da kuma’yan kasuwa, ɗaura da Ƙofar Bincike, har zuwa ɗakin da yake bisa kusurwar.
Après lui Malkija, fils de Tsoreph, répara jusqu'à la maison des Néthiniens, et des revendeurs, et l'endroit de la porte de Miphkad, et jusqu'à la montée du coin.
32 Maƙeran zinariya da’yan kasuwa suka gyara wani sashi tsakanin ɗakin da yake bisa kusurwa da Ƙofar Tumaki.
Et les orfèvres et les revendeurs réparèrent entre la montée du coin et la porte du bercail.

< Nehemiya 3 >