< Mattiyu 25 >

1 “A lokacin mulkin sama zai zama kamar budurwai goma waɗanda suka ɗauki fitilunsu suka fita don su taryi ango.
Siis on taevariik kui kümme neitsit, kes võtsid oma lambid ja läksid peigmehele vastu.
2 Biyar daga cikinsu wawaye ne, biyar kuma masu hikima.
Viis neist olid rumalad ja viis arukad.
3 Wawayen sun ɗauki fitilunsu, sai dai ba su riƙe mai ba.
Rumalad võtsid kaasa küll lambid, kuid ei võtnud õli.
4 Masu hikimar kuwa suka riƙo tulunan mai da fitilunsu.
Arukad võtsid aga lampidele lisaks kaasa õlianumad.
5 Ango ya yi jinkirin zuwa, sai duk suka shiga gyangyaɗi har barci ya kwashe su.
Kui peigmehe tulek viibis, jäid nad kõik uniseks ja uinusid magama.
6 “Can tsakar dare, sai aka ji kira, ana cewa, ‘Ga ango nan! Ku fito, ku tarye shi!’
Keskööl aga kõlas hüüd: „Peigmees tuleb! Minge talle vastu!“
7 “Sai dukan budurwan nan suka farka suka kuna fitilunsu.
Siis ärkasid kõik need neitsid ja hakkasid lampe kohendama.
8 Sai wawayen suka ce wa masu hikimar, ‘Ku ɗan sassam mana manku; fitilunmu suna mutuwa.’
Ja rumalad ütlesid arukatele: „Andke meile osa oma õlist, sest meie lambid kustuvad!“
9 “Su kuwa suka amsa, suka ce, ‘A’a, wataƙila ba zai ishe mu da ku ba. Gara ku je wurin masu sayarwa ku sayo.’
Kuid arukad vastasid: „Ei mingil juhul! Sellest ei jätku meile ja teile! Minge parem kaupmeeste juurde ja ostke enestele ise!“
10 “Amma yayinda suke kan tafiya garin sayen mai, sai ango ya iso. Budurwai da suke a shirye, suka shiga wajen bikin auren tare da shi. Aka kuma kulle ƙofa.
Ent kui nad olid teel õli ostma, tuli peigmees, ja kes olid valmis, sisenesid temaga pulmamajja, ja uks suleti.
11 “An jima can, sai ga sauran sun iso. Suka ce, ‘Ranka yă daɗe! Ranka yă daɗe! Ka buɗe mana ƙofa!’
Hiljem tulid ka need teised neitsid ja ütlesid: „Isand, isand, ava meile!“
12 “Amma ya amsa ya ce, ‘Gaskiya nake gaya muku, ban san ku ba.’
Tema aga vastas neile: „Tõesti, ma ütlen teile, ma ei tunne teid.“
13 “Saboda haka sai ku zauna a faɗake, don ba ku san ranar ko sa’ar ba.
Seepärast valvake, sest te ei tea seda päeva ega tundi!
14 “Har wa yau, za a kwatanta shi da mutumin da zai yi tafiya, wanda ya kira bayinsa ya kuma danƙa musu mallakarsa.
Ja jälle, taevariik on kui mees, kes pidi minema reisile. Ta kutsus oma sulased ja usaldas vara nende hoolde.
15 Ga guda, ya ba shi talenti biyar na kuɗi, ga wani talenti biyu, ga wani kuma talenti ɗaya, kowa bisa ga azancinsa. Sa’an nan ya yi tafiyarsa.
Ühele ta andis viis talenti, teisele kaks ja kolmandale ühe, igaühele tema suutlikkust mööda, ning reisis ära.
16 Mutumin da ya karɓi talenti biyar, nan da nan ya tafi ya yi kasuwanci da su har ya sami ribar talenti biyar.
Kohe läks see, kes oli saanud viis talenti, paigutas need ärisse ja teenis veel viis talenti.
17 Haka ma, wannan mai talenti biyu, shi ma ya yi riba biyu.
Nõndasamuti ka kaks talenti saanu sai teist kaks juurde.
18 Amma mutumin da ya karɓi talenti ɗaya ɗin, ya tafi, ya tona rami, ya ɓoye kuɗin maigidansa.
Aga kes oli saanud ühe, läks ja kaevas maasse augu ning peitis ära oma isanda raha.
19 “Bayan an daɗe, sai maigidan bayin nan ya dawo, ya kuma daidaita lissafi da su.
Pika aja pärast tuli nende sulaste isand tagasi ja päris neilt aru.
20 Mutumin da ya karɓi talenti biyar, ya kawo ƙarin talenti biyar. Ya ce, ‘Maigida, ka danƙa mini talenti biyar. Ga shi, na yi ribar biyar.’
Tema ette astus see, kes oli saanud viis talenti, lisas sellele veel viis talenti ja ütles: „Isand, sa usaldasid mulle viis talenti. Vaata, ma olen teeninud teist viis talenti!“
21 “Maigidansa ya amsa ya ce, ‘Madalla, bawan kirki mai aminci! Ka yi aminci a kan abubuwa kaɗan, zan sa ka lura da abubuwa masu yawa. Zo ka yi farin ciki tare da maigidanka!’
Isand ütles talle: „Hästi tehtud, sa tubli ja ustav sulane! Sa oled olnud ustav pisku üle, ma panen su palju üle. Tule sisse ja saa osa oma isanda rõõmust!“
22 “Mutumin da yake da talenti biyu, shi ma ya zo ya ce, ‘Maigida, ka danƙa mini talenti biyu; ga shi, na yi ribar biyu.’
Tuli ka see, kes oli saanud kaks talenti, ja ütles: „Isand, sa usaldasid mulle kaks talenti. Vaata, ma olen teeninud veel kaks!“
23 “Maigidansa ya amsa ya ce, ‘Madalla, bawan kirki mai aminci! Ka yi aminci a kan abubuwa kaɗan, zan sa ka lura da abubuwa masu yawa. Zo ka yi farin ciki tare da maigidanka!’
Isand ütles tallegi: „Hästi tehtud, sa tubli ja ustav sulane! Sa oled olnud ustav pisku üle, ma panen su palju üle. Tule sisse ja saa osa oma isanda rõõmust!“
24 “Sa’an nan mutumin da ya karɓi talenti ɗaya ya zo. Ya ce, ‘Maigida, na san cewa kai mutum ne mai wuyan sha’ani, kana girbi inda ba ka shuka ba, kana kuma tara inda ba ka yafa iri ba.
Tuli ka see, kes oli saanud ühe talendi. Ta ütles: „Isand, ma tean, et sa oled vali mees. Sa lõikad sealt, kuhu sa ei ole külvanud, ja kogud sealt, kuhu sa ei ole seemet puistanud.
25 Saboda haka na ji tsoro, na je na ɓoye talentinka a ƙasa. Ga abinka.’
Ma kartsin, läksin ja peitsin sinu talendi maa sisse. Vaata, siin on sinu oma!“
26 “Maigidansa ya amsa ya ce, ‘Kai mugun bawa, mai ƙyuya! Ashe, ka san cewa ina girbi inda ban yi shuka ba, ina kuma tarawa inda ban yafa iri ba?
Tema isand aga vastas talle: „Sa halb ja laisk sulane! Sa teadsid, et ma lõikan sealt, kuhu ma ei ole külvanud, ja kogun sealt, kuhu ma ei ole seemet puistanud!
27 To, in haka ne, ai, da ka sa kuɗina a banki, don sa’ad da na dawo da na karɓi abina da riba.
Siis sa oleksid pidanud mu raha panema panka, ja tulles ma oleksin saanud selle tagasi kasuga.
28 “‘Karɓi talentin daga hannunsa ku ba wanda yake da talenti goma.
Seepärast võtke nüüd tema käest talent ära ja andke sellele, kellel on kümme talenti!
29 Gama duk mai abu za a ƙara masa, zai kuma same shi a yawalce. Duk wanda ba shi da shi kuwa, ko ɗan abin da yake da shi ma, sai an karɓe masa.
Sest igaühele, kellel on, antakse, ja tal on rohkem kui küllalt, kellel aga ei ole, selle käest võetakse ära seegi, mis tal on.
30 Ku jefar da banzan bawan nan waje, cikin duhu, inda za a yi kuka da cizon haƙora.’
Ja see vääritu sulane visake välja pimedusse! Seal on ulgumine ja hammaste kiristamine.“
31 “Sa’ad da Ɗan Mutum ya zo cikin ɗaukakarsa, tare da dukan mala’iku, zai zauna a kursiyinsa cikin ɗaukakar sama.
Aga kui Inimese Poeg tuleb oma auhiilguses kõigi inglite saatel, siis ta istub oma auhiilguse troonile.
32 Za a tara dukan al’ummai a gabansa, zai kuma raba mutane dabam-dabam yadda makiyayi yakan ware tumaki daga awaki.
Ja tema ette kogutakse kõik rahvad ja ta eraldab nad üksteisest, nagu karjane eraldab lambad sikkudest,
33 Zai sa tumaki a damansa, awaki kuma a hagunsa.
ja seab lambad oma paremale, sikud aga vasakule käele.
34 “Sa’an nan Sarki zai ce wa waɗanda suke damansa, ‘Ku zo, ku da Ubana ya yi wa albarka; ku karɓi gādonku, mulkin da aka shirya muku tun halittar duniya.
Siis ütleb Kuningas neile, kes on ta paremal käel: „Tulge teie, keda mu Isa on õnnistanud! Võtke vastu oma pärand, Kuningriik, mis teile on valmis pandud maailma loomisest peale!
35 Gama da nake jin yunwa, kun ciyar da ni, da nake jin ƙishirwa, kun ba ni abin sha, da nake baƙunci, kun karɓe ni,
Sest mul oli nälg ja te andsite mulle süüa; mul oli janu ja te andsite mulle juua; ma olin võõras ja te võtsite mu vastu;
36 da nake bukatar tufafi, kun yi mini sutura, da na yi rashin lafiya, kun lura da ni, da nake kurkuku, kun ziyarce ni.’
ma olin alasti ja te riietasite mind; ma olin haige ja te tulite mind vaatama; ma olin vangis ja te tulite minu juurde.“
37 “Sa’an nan masu adalci za su amsa masa, su ce, ‘Ubangiji, yaushe muka gan ka da yunwa muka ciyar da kai, ko da ƙishirwa muka ba ka abin sha?
Siis küsivad õiged temalt: „Issand, millal me nägime sind näljasena ja toitsime sind, või janusena ja jootsime sind?
38 Yaushe kuma muka gan ka baƙo muka karɓe ka, ko cikin bukatar tufafi muka yi maka sutura?
Millal me nägime sind võõrana ja võtsime sind vastu, või alasti ja riietasime sind?
39 Yaushe kuma muka gan ka cikin rashin lafiya ko a kurkuku muka ziyarce ka?’
Millal me nägime sind haigena või vangis ja külastasime sind?“
40 “Sarkin zai amsa ya ce, ‘Gaskiya nake gaya muku, duk abin da kuka yi wa ɗaya daga cikin waɗannan’yan’uwana mafi ƙanƙanta, ni kuka yi wa.’
Ja kuningas vastab neile: „Tõesti, ma ütlen teile, mida te iganes olete teinud kellele tahes mu kõige pisematest vendadest, seda te olete teinud mulle!“
41 “Sa’an nan zai ce wa waɗanda suke a hagunsa, ‘Ku rabu da ni, la’anannu, zuwa cikin madawwamiyar wutar da aka shirya don Iblis da mala’ikunsa. (aiōnios g166)
Siis ütleb ta neile, kes on ta vasakul käel: „Minge ära minu juurest, te neetud, igavesse tulle, mis on pandud valmis kuradile ja tema inglitele! (aiōnios g166)
42 Gama da nake jin yunwa, ba ku ba ni abinci ba, da nake jin ƙishirwa, ba ku ba ni abin sha ba,
Sest mul oli nälg ja te ei andnud mulle süüa; mul oli janu ja te ei andnud mulle juua;
43 da na yi baƙunci, ba ku karɓe ni ba, da nake bukatar tufafi, ba ku yi mini sutura ba, da na yi rashin lafiya kuma ina a kurkuku, ba ku lura da ni ba.’
ma olin võõras ja te ei võtnud mind vastu; ma olin alasti ja te ei riietanud mind; ma olin haige ja vangis ja te ei tulnud mind vaatama.“
44 “Su ma za su amsa, su ce, ‘Ubangiji, yaushe muka gan ka cikin yunwa ko ƙishirwa ko baƙo ko cikin bukatar tufafi ko cikin rashin lafiya ko cikin kurkuku, ba mu taimake ka ba?’
Siis küsivad temalt ka nemad: „Issand, millal me nägime sind näljasena või janusena või võõrana või alasti või haigena või vangis, ega aidanud sind?“
45 “Zai amsa, yă ce, ‘Gaskiya nake gaya muku, duk abin da ba ku yi wa ɗaya daga cikin waɗannan mafi ƙanƙanta ba, ba ku yi mini ba ke nan.’
Siis ta vastab neile: „Tõesti, ma ütlen teile, mida te iganes olete jätnud tegemata kellele tahes mu kõige pisematest vendadest, seda te olete jätnud tegemata minulegi.“
46 “Sa’an nan za su tafi cikin madawwamiyar hukunci, amma masu adalci kuwa za su shiga rai madawwami.” (aiōnios g166)
Ja need lähevad igavesse karistusse, õiged aga igavesse ellu.“ (aiōnios g166)

< Mattiyu 25 >