< Mattiyu 24 >

1 Yesu ya bar haikali ke nan, yana cikin tafiya sai almajiransa suka zo wurinsa don su ja hankalinsa ga gine-ginen haikali.
Jeesus väljus templist ja sammus edasi. Jüngrid aga astusid tema juurde, et talle templi hooneid näidata.
2 Sai Yesu ya ce, “Kun ga duk waɗannan abubuwa? Gaskiya nake gaya muku, ba wani dutse a nan da za a bari a kan wani; duk za a rushe.”
„Eks te näe seda kõike?“küsis Jeesus. „Tõesti, ma ütlen teile, ei jäeta siin kivi kivi peale, mida maha ei kistaks!“
3 Da Yesu yana zaune a Dutsen Zaitun, almajiran suka zo wurinsa a ɓoye. Suka ce, “Gaya mana, yaushe ne wannan zai faru, mece ce alamar zuwanka da kuma ta ƙarshen zamani?” (aiōn g165)
Kui Jeesus istus Õlimäel, astusid jüngrid tema juurde ja küsisid omavahel olles: „Ütle meile, millal see kõik tuleb ja mis on sinu tulemise ja selle ajastu lõpu tunnustäht?“ (aiōn g165)
4 Yesu ya amsa, “Ku lura fa, kada wani yă ruɗe ku.
Jeesus vastas neile: „Vaadake, et keegi teid ei eksitaks!
5 Gama mutane da yawa za su zo cikin sunana, suna cewa, ‘Ni ne Kiristi,’ za su kuwa ruɗi mutane da yawa.
Sest paljud tulevad minu nimel, öeldes: „Mina olen Messias!“ja eksitavad paljusid.
6 Za ku ji labarin yaƙe-yaƙe da kuma jita-jitarsu, sai dai ku lura kada hankalinku yă tashi. Dole irin waɗannan abubuwa su faru, amma ƙarshen tukuna.
Aga kui te kuulete sõdadest ja kuulujutte sõjast, siis ärge heituge. Sest need asjad peavad sündima, kuid see ei ole veel lõpp.
7 Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki yă tasar wa mulki. Za a yi yunwa da girgizar ƙasa a wurare dabam-dabam.
Sest rahvas tõuseb rahva vastu ja kuningriik kuningriigi vastu ning paljudes paikades on maavärinaid ja näljahäda.
8 Dukan waɗannan fa, mafarin azabar naƙudar haihuwa ne.
See kõik on aga sünnitusvalude algus.
9 “Sa’an nan za a bashe ku don a tsananta muku a kuma kashe ku, dukan al’ummai za su ƙi ku saboda ni.
Siis antakse teid viletsusse ja teid tapetakse ja te saate kõigi rahvaste vihaaluseks minu nime pärast.
10 A wannan lokaci, da yawa za su juya daga bangaskiya, su ci amana su kuma ƙi juna,
Sellel ajal taganevad paljud usust ning reedavad ja vihkavad üksteist.
11 annabawan ƙarya da yawa za su firfito su kuma ruɗi mutane da yawa.
Palju valeprohveteid tõuseb esile ja need eksitavad paljusid.
12 Saboda ƙaruwar mugunta, ƙaunar yawanci za tă yi sanyi,
Ja et ülekohus kasvab, jahtub paljude armastus.
13 amma duk wanda ya tsaya da ƙarfi har ƙarshe, zai sami ceto.
Aga kes peab vastu lõpuni, see pääseb.
14 Za a kuma yi wa’azin wannan bisharar mulki a cikin dukan duniya, yă zama shaida ga dukan al’ummai, sa’an nan ƙarshen yă zo.
Ja seda Kuningriigi evangeeliumi kuulutatakse kogu maailmas, tunnistuseks kõigile rahvastele, ja siis saabub lõpp.
15 “Saboda haka sa’ad da kuka ga ‘abin ƙyama mai kawo hallaka,’wanda annabi Daniyel ya yi magana a kai, yana tsaye a tsattsarkan wuri (mai karatu yă gane),
Kui te siis näete pühas paigas seismas hävituse koletist, millest on rääkinud prohvet Taaniel – et lugeja mõistaks! –,
16 to, sai waɗanda suke cikin Yahudiya, su gudu zuwa cikin duwatsu.
siis need, kes on Juudamaal, põgenegu mägedesse.
17 Kada wani da yake a kan rufin gidansa, yă sauko don ɗaukar wani abu a gida.
Kes on katusel, ärgu tulgu alla oma majast midagi võtma,
18 Kada wani da yake gona kuma yă komo don ɗaukar rigarsa.
ja kes on põllul, ärgu pöördugu tagasi võtma oma kuube!
19 Kaiton mata masu ciki da mata masu renon’ya’ya a waɗancan kwanakin!
Häda neile, kes on lapseootel, ja neile, kes imetavad sellel ajal!
20 Ku yi addu’a, kada gudunku yă zama a lokacin sanyi ko a ranar Asabbaci.
Palvetage, et teie põgenemine ei juhtuks talvel ega hingamispäeval!
21 Gama a lokacin za a yi wata matsananciyar wahala, wadda ba a taɓa yi ba tun farkon duniya har ya zuwa yanzu ba kuwa za a ƙara yi ba.
Sest siis on nii suur ahistus, mille sarnast pole olnud maailma algusest kuni praeguse ajani ega tule enam iial.
22 “Da ba don an taƙaita kwanakin nan ba, da babu wani da zai tsira, amma saboda zaɓaɓɓun nan, za a taƙaita kwanakin.
Ja kui neid päevi ei lühendataks, siis ei pääseks ükski. Kuid Jumala valitute pärast lühendatakse neid päevi.
23 A lokacin in wani ya ce muku, ‘Duba, ga Kiristi nan!’ Ko, ‘Ga shi can!’ Kada ku gaskata.
Kui siis keegi teile ütleb: „Näe, Messias on siin!“või „Ta on seal!“, siis ärge uskuge!
24 Gama Kiristi masu yawa na ƙarya, da annabawan ƙarya za su firfito, su kuma aikata manyan alamu da ayyukan banmamaki don su ruɗi har da zaɓaɓɓu ma in zai yiwu.
Sest tõuseb valemessiaid ja valeprohveteid ja need teevad suuri tunnustähti ja imesid, et eksitada, kui võimalik, isegi valituid.
25 Ga shi, na faɗa muku tun da wuri.
Vaata, mina olen teid ette hoiatanud!
26 “Saboda haka in wani ya ce muku, ‘Ga shi can a hamada,’ kada ku fita; ko, ‘Ga shi nan a ɗakunan ciki,’ kada ku gaskata.
Kui keegi teile siis ütleb: „Ta on seal, kõrbes!“, ärge siis minge välja; või: „Ta on siin, salakambris!“, siis ärge uskuge!
27 Gama kamar yadda walƙiya take wulgawa walai daga gabas zuwa yamma, haka dawowar Ɗan Mutum zai kasance.
Sest otsekui välk sähvatab idast ja paistab läände, nõnda on Inimese Poja tulemine.
28 Duk inda mushe yake, can ungulai za su taru.
Kus iganes on korjus, sinna kogunevad raisakotkad.
29 “Nan da nan bayan tsabar wahalan nan “‘sai a duhunta rana, wata kuma ba zai ba da haskensa ba; taurari kuma za su fāffāɗi daga sararin sama, za a kuma girgiza abubuwan sararin sama.’
Kohe pärast selle aja viletsust „pimeneb päike ja kuu ei anna oma valgust, tähed kukuvad taevast ja taeva vägesid kõigutatakse“.
30 “A sa’an nan ne alamar dawowar Ɗan Mutum zai bayyana a sararin sama, dukan al’umman duniya kuwa za su yi kuka. Za su ga Ɗan Mutum yana zuwa kan gizagizan sararin sama, da iko da kuma ɗaukaka mai girma.
Siis saab nähtavaks Inimese Poja tunnustäht taevas; ja siis tõstavad hädakisa maa peal kõik rahvad, kui nad näevad Inimese Poega tulemas taeva pilvede peal väe ja suure kirkusega.
31 Zai kuwa aiki mala’ikunsa su busa ƙaho mai ƙara sosai, za su kuwa tattaro zaɓaɓɓunsa daga kusurwoyi huɗun nan, daga wannan bangon duniya zuwa wancan.
Ja tema läkitab oma inglid valju pasunahäälega ja need koguvad kokku tema valitud nelja tuule poolt, igast taevakaarest.
32 “Yanzu fa, sai ku koyi wannan darasi daga itacen ɓaure. Da zarar rassansa suka yi taushi ganyayensa kuma suka toho, kun san damina ta kusa.
Ent õppige viigipuult! Kui selle okstele tärkavad võrsed ja ajavad lehti, siis te teate, et suvi on lähedal.
33 Haka kuma, sa’ad da kun ga dukan waɗannan abubuwa, ku sani ya yi kusan zuwa, yana ma dab da bakin ƙofa.
Nõnda ka teie, kui te näete kõike seda sündimas, siis teadke, et tema on lähedal, ukselävel.
34 Gaskiya nake gaya muku, wannan zamani ba zai shuɗe ba sai dukan abubuwan nan sun faru.
Tõesti, ma ütlen teile, see sugupõlv ei kao, kuni kõik see on sündinud.
35 Sama da ƙasa za su shuɗe, amma maganata ba za tă taɓa shuɗe ba.
Taevas ja maa kaovad, kuid minu sõnad ei kao iial.
36 “Babu wanda ya san wannan rana ko sa’a, ko mala’ikun da suke sama ma, ko Ɗan, sai dai Uban kaɗai.
Ent seda päeva ja tundi ei tea keegi, ei inglid taevas ega Poeg, vaid Isa üksi.
37 Kamar yadda ya faru a zamanin Nuhu, haka zai zama a dawowar Ɗan Mutum.
Sest nii nagu olid Noa päevad, nii on ka Inimese Poja tulemine.
38 Gama a kwanaki kafin ruwan tsufana, mutane sun yi ta ci, sun kuma yi ta sha, suna aure, suna kuma aurarwa, har zuwa ranar da Nuhu ya shiga jirgi;
Neil päevil enne veeuputust inimesed sõid ja jõid, võtsid naisi ja läksid mehele selle päevani, mil Noa läks laeva.
39 ba su kuwa san abin da yake faruwa ba sai da ruwan tsufana ya zo ya share su tas. Haka zai zama a dawowar Ɗan Mutum.
Nad ei teadnud midagi, enne kui tuli veeuputus ja võttis nad kõik ära. Nõnda on ka Inimese Poja tulemine.
40 Maza biyu za su kasance a gona; za a ɗau ɗaya a bar ɗaya.
Siis on kaks põllul – üks võetakse vastu ja teine jäetakse maha.
41 Mata biyu za su kasance suna niƙa; za a ɗau ɗaya a bar ɗaya.
Kaks naist on veskil jahvatamas – üks võetakse vastu ja teine jäetakse maha.
42 “Saboda haka sai ku zauna a faɗake, gama ba ku san a wace rana ce Ubangijinku zai zo ba.
Seepärast valvake, sest teie ei tea, mis tunnil teie Issand tuleb!
43 Ku dai gane wannan, da maigida ya san ko a wane lokaci ne da dare, ɓarawo zai zo, da sai yă zauna a faɗake yă kuma hana a shiga masa gida.
Küllap te mõistate, et kui peremees teaks, millisel öötunnil varas tuleb, siis ta valvaks ega laseks oma majja sisse murda.
44 Saboda haka ku ma, sai ku zauna a faɗake, domin Ɗan Mutum zai zo a sa’ar da ba ku za tă ba.
Seepärast olge ka teie valmis, sest Inimese Poeg tuleb tunnil, mil te ei arvagi!
45 “Wane ne bawan nan mai aminci da kuma mai hikima, wanda maigida ya sa yă lura da bayi a cikin gidansa, yă riƙa ba su abinci a daidai lokaci?
Kes siis on ustav ja arukas sulane, kelle ta isand on seadnud oma majapidamise üle teenijatele õigel ajal toitu andma?
46 Zai zama wa bawan nan da kyau in maigidan ya dawo ya same shi yana yin haka.
Õnnistatud on sulane, kelle ta isand tulles leiab nõnda tegevat!
47 Gaskiya nake gaya muku, zai sa shi yă lura da dukan dukiyarsa.
Tõesti, ma ütlen teile, ta annab tema hoolde kogu oma vara.
48 Amma in wannan bawa mugu ne, ya kuma ce a ransa, ‘Maigidana ba zai dawo da wuri ba.’
Aga kui sulane on halb ja mõtleb: „Mu isanda tulek viibib, “
49 Sa’an nan yă fara dūkan’yan’uwansa bayi, yana ci yana kuma sha tare da mashaya.
ning hakkab peksma kaassulaseid, sööma ja jooma koos purjutajatega,
50 Maigidan wannan bawa zai dawo a ranar da bai yi tsammani ba, a sa’ar kuma da bai sani ba.
siis selle sulase isand tuleb päeval, mil ta ei oota, ja tunnil, mida ta ei tea.
51 Maigidan zai farfasa masa jiki da bulala, yă kuma ba shi wuri tare da munafukai, inda za a yi kuka da cizon haƙora.
Ta raiub sulase tükkideks ja annab talle sama koha silmakirjatsejatega seal, kus on ulgumine ja hammaste kiristamine.

< Mattiyu 24 >

The World is Destroyed by Water
The World is Destroyed by Water