< Mattiyu 17 >
1 Bayan kwana shida, sai Yesu ya ɗauki Bitrus, Yaƙub da Yohanna ɗan’uwan Yaƙub, ya kai su kan wani dutse mai tsawo, su kaɗai.
And after six days, Jeshu took Kipha, and Jakub, and Juchanon his brother, and led them to a high mountain by themselves.
2 A can aka sāke kamanninsa a gabansu. Fuskarsa ta haskaka kamar rana, tufafinsa kuwa suka zama fari fat suna walƙiya.
And Jeshu was changed before them; and his countenance shone like the sun, and his vestments were resplendent as the light.
3 Nan take sai ga Musa da Iliya suka bayyana a gabansu, suna magana da Yesu.
And there were seen with them Musha and Elia talking with him.
4 Sai Bitrus ya ce wa Yesu, “Ubangiji, ya yi kyau da muke nan. In kana so, sai in kafa bukkoki uku, ɗaya dominka, ɗaya domin Musa, ɗaya kuma domin Iliya.”
Then answered Kipha, and said to Jeshu, My Lord, it is good for us to be here; and if thou art willing, we will make here three tabernacles; one for thee, and one for Musha, and one for Elia.
5 Yayinda yake cikin magana, sai wani girgije mai haske ya rufe su, sai wata murya daga cikin girgijen ta ce, “Wannan Ɗana ne, wanda nake ƙauna; wanda kuma nake jin daɗinsa ƙwarai. Ku saurare shi!”
But while he spake, behold, a bright cloud overspread them, and the voice was from the cloud, saying, This is my Son, the Beloved, in whom I have delighted: to him attend.
6 Sa’ad da almajiran suka ji haka, sai suka fāɗi ƙasa rubda ciki, a firgice.
And when the disciples heard, they fell upon their faces and feared greatly.
7 Amma Yesu ya zo ya taɓa su ya ce, “Ku tashi, kada ku ji tsoro.”
And Jeshu approached them and touched them, and said, Arise, fear not.
8 Da suka ɗaga kai, ba su ga kowa ba sai Yesu kaɗai.
And they lifted up their eyes and saw no man, except Jeshu by himself.
9 Suna cikin gangarowa daga dutsen ke nan, sai Yesu ya umarce su cewa, “Kada ku faɗa wa kowa abin da kuka gani, sai bayan an tā da Ɗan Mutum daga matattu.”
And while they were descending from the mountain, Jeshu charged them, and said to them, Before no man declare this vision, until the Son of man be risen from the dead.
10 Almajiran suka tambaye shi suka ce, “To, me ya sa malaman dokoki suke cewa, dole sai Iliya ya fara zuwa?”
And the disciples asked and said to him, Why therefore say the scribes that Elia must come first?
11 Yesu ya amsa ya ce, “Tabbatacce, Iliya zai zo, zai kuma gyara dukan abubuwa.
Jeshu answered and said to them, Elia cometh first that he may fulfil every thing;
12 Amma ina faɗa muku, Iliya ya riga ya zo, ba su kuwa gane shi ba, amma suka yi masa duk abin da suka ga dama. Haka ma Ɗan Mutum zai sha wahala a hannunsu.”
but I say to you, that, behold, Elia hath come, but they knew him not, and have done to him as they would. So also is the Son of man to suffer from them.
13 Sa’an nan almajiran suka gane cewa yana musu zancen Yohanna Mai Baftisma ne.
Then understood the disciples that concerning Juchanon the Baptizer he spake to them.
14 Da suka isa wajen taron, sai wani mutum ya zo ya durƙusa a gabansa.
AND when they came to the multitude, a man approached him and kneeled upon his knees, and said to him,
15 Ya ce, “Ubangiji, ka yi wa ɗana jinƙai. Yana da farfaɗiya yana kuma shan wahala ƙwarai. Ya sha fāɗuwa cikin wuta ko ruwa.
My Lord, have mercy on me! my son is lunatic and grievously afflicted; for often he falleth into the fire and often into the water.
16 Na kuma kawo shi wurin almajiranka, amma ba su iya warkar da shi ba.”
And I brought him to thy disciples, but they could not heal him.
17 Yesu ya amsa ya ce, “Ya ku zamani marasa bangaskiya da kuma masu taurinkai, har yaushe zan kasance tare da ku? Har yaushe kuma zan yi haƙuri da ku? Kawo mini yaron a nan.”
Jeshu answered and said, O unbelieving and perverse generation! how long shall I be with you, how long shall I bear with you? Bring him hither to me.
18 Yesu ya tsawata wa aljanin, ya kuwa rabu da yaron, nan take yaron ya warke.
And Jeshu rebuked him, and the demon went forth from him, and the youth was healed from that hour.
19 Sa’an nan almajiran suka zo wurin Yesu a ɓoye suka tambaye shi suka ce, “Me ya sa ba mu iya fitar da aljanin ba?”
Then came the disciples to Jeshu by himself, and said to him, Why were we not able to heal him?
20 Ya amsa ya ce, “Saboda kuna da ƙarancin bangaskiya sosai. Gaskiya nake gaya muku, in kuna da bangaskiyar da take ƙanƙanuwa kamar ƙwayar mustad, za ku iya ce wa wannan dutse, ‘Matsa daga nan zuwa can,’ zai kuwa matsa. Babu abin da zai gagare ku.”
Jeshu saith to them, Because of your unbelief; for assuredly I tell you, if there were in you faith as a grain of mustard, you should say to this mountain, Pass hence, and it would pass away; and nothing should overcome you.
But this kind goeth not forth but by fasting and by prayer.
22 Da suka taru a Galili, sai ya ce musu, “Za a bashe Ɗan Mutum, a hannun mutane.
WHEN they had returned into Galila, Jeshu said to them, It is coming that the Son of man shall be delivered into the hands of men,
23 Za su kashe shi, a rana ta uku kuma za a tashe shi.” Almajiran kuwa suka cika da baƙin ciki.
and they shall kill him; and in the third day he shall arise. And it grieved them exceedingly.
24 Bayan Yesu da almajiransa suka isa Kafarnahum, sai masu karɓan harajin rabin shekel suka zo wurin Bitrus suka ce, “Malaminku ba ya biyan harajin haikali ne?”
And when they came to Kapher-nachum, they who took the two zuzis, the head-silver, approached Kipha and said to him, Your master, doth he not give his two zuzeen?
25 Ya amsa ya ce “I, yana biya.” Da Bitrus ya shiga gida, Yesu ne ya fara magana. Ya ce masa, “Me ka gani, Siman? Daga wurin wane ne sarakunan duniya suke karɓar kuɗin shiga da kuma haraji, daga wurin’ya’yansu ne ko kuwa daga wurin waɗansu?”
He saith to them, Yes. And when Kipha entered the house, Jeshu anticipated him, and said to him, How doth it appear to thee, Shemun? the kings of the earth, from whom do they take custom and headsilver, from their children, or from aliens?
26 Bitrus ya amsa ya ce, “Daga wurin waɗansu.” Yesu ya ce masa, “Wato, an ɗauke wa’ya’yan ke nan.
Shemun saith to him, From aliens: Jeshu saith to him, Then the children are free.
27 Amma don kada mu ɓata musu rai, ka je tafki ka jefa ƙugiyarka. Ka ɗauki kifin da ka fara kama; ka buɗe bakinsa, za ka sami shekel guda. Ka kawo ka ba su, harajina da naka ke nan.”
But that we may not offend them, go to the sea, and cast the hook; and the fish that first cometh up, open his mouth; and thou shalt find a stater, that take and present for me and thee.