< Markus 8 >

1 A kwanakin nan wani taro mai girma ya taru. Tun da yake ba su da abin da za su ci, sai Yesu ya kira almajiransa ya ce,
In those days, when there was a very large crowd that had nothing to eat, Jesus called his disciples over and said to them,
2 “Ina jin tausayin mutanen nan, kwanansu uku ke nan tare da ni, kuma ba su da abin da za su ci.
“I have compassion on the crowd because they have stayed with me now for three days and have nothing to eat.
3 In na sallame su gida da yunwa, za su kāsa a hanya, don waɗansu daga cikinsu sun zo daga nesa.”
If I send them away to their homes without having eaten, they will faint on the way, for some of them have come from far away.”
4 Almajiransa suka amsa suka ce, “Amma a ina, a wannan wurin da ba kowa, wani zai iya samun isashen burodi, don a ciyar da su?”
His disciples answered him, “How can anyone feed these people with bread here in the wilderness?”
5 Sai Yesu ya yi tambaya ya ce, “Burodi guda nawa kuke da su?” Suka ce, “Bakwai.”
He asked them, “How many loaves do you have?” They said, “Seven.”
6 Sai ya gaya wa taron su zazzauna a ƙasa. Bayan ya ɗauki burodin nan bakwai, ya yi godiya, sai ya kakkarya, ya ba wa almajiransa su rarraba wa mutanen, suka kuwa yi haka.
So he commanded the crowd to sit down on the ground, and taking the seven loaves, he gave thanks, broke them, and gave them to his disciples to distribute, and they set them before the crowd.
7 Suna kuma da ƙananan kifaye kaɗan, ya ba da godiya dominsu, ya kuma ce wa almajiran su rarraba musu.
They also had a few small fish. After blessing the fish, Jesus told the disciples to set them before the crowd as well.
8 Mutanen suka ci, suka ƙoshi. Daga baya, almajiran suka tattara gutsattsarin da suka rage cike da kwanduna bakwai.
The people ate and were filled, and the disciples picked up what was left over of the broken pieces, seven baskets full.
9 Wajen maza dubu huɗu ne suka kasance. Da ya sallame su,
There were about four thousand men who had eaten. After sending them away,
10 sai ya shiga jirgin ruwa tare da almajiransa, suka tafi yankin Dalmanuta.
Jesus immediately got into the boat with his disciples and went to the district of Dalmanutha.
11 Farisiyawa suka zo suka fara yin wa Yesu tambayoyi. Don su gwada shi, sai suka nemi yă nuna musu wata alama daga sama.
Then the Pharisees came and began to argue with Jesus, asking him for a sign from heaven, to test him.
12 Sai ya ja numfashi mai zurfi ya ce, “Don me wannan zamani yake neman ganin abin banmamaki? Gaskiya nake gaya muku, ba wata alamar da za a ba su.”
Sighing deeply in his spirit, he said, “Why does this generation ask for a sign? Truly I say to you, no sign will be given to this generation.”
13 Sai ya bar su, ya koma cikin jirgin ruwan, suka ƙetare zuwa ɗaya hayin.
Then he left them, got into the boat again, and went away to the other side of the sea.
14 Almajiran suka manta su riƙe burodi, sai dai guda ɗaya da suke da shi a cikin jirgin ruwan.
Now the disciples had forgotten to bring bread, and they had nothing with them in the boat except for one loaf.
15 Yesu ya gargaɗe su ya ce, “Ku yi hankali, ku kuma lura da yistin Farisiyawa da na Hiridus.”
Then Jesus gave them strict orders, saying, “Watch out! Beware of the leaven of the Pharisees and the leaven of Herod.”
16 Suka tattauna wannan da juna, suna cewa, “Don ba mu da burodi ne.”
So they discussed this with one another, saying, “He must have said this because we have no bread.”
17 Da ya gane abin da suke tattaunawa, sai Yesu ya tambaye su ya ce, “Don me kuke zancen rashin burodi? Har yanzu ba ku gane ko fahimta ba? Zukatanku sun taurare ne?
Aware of this, Jesus said to them, “Why are you discussing the fact that you have no bread? Do you not yet perceive or understand? Are your hearts still hardened?
18 Kuna da idanu, amma kun kāsa gani, kuna da kunnuwa, amma kun kāsa ji? Ba ku tuna ba?
Having eyes do you not see, and having ears do you not hear? Do you not remember?
19 Da na kakkarya burodi guda biyar wa mutane dubu biyar, kwanduna nawa kuka kwashe cike da gutsattsarin?” Suka amsa, “Sha biyu.”
When I broke the five loaves for the five thousand, how many baskets full of broken pieces did you pick up?” They said to him, “Twelve.”
20 “Da na kuma kakkarya burodin nan bakwai wa mutum dubu huɗu, kwanduna nawa kuka kwashe cike da gutsattsarin?” Suka ce, “Bakwai.”
“And when I broke the seven loaves for the four thousand, how many baskets full of broken pieces did you pick up?” They said, “Seven.”
21 Ya ce musu, “Har yanzu ba ku fahimta ba?”
Then he said to them, “How is it that you do not understand?”
22 Suka iso Betsaida, sai waɗansu mutane suka kawo wani makaho, suka roƙi Yesu yă taɓa shi.
When Jesus came to Bethsaida, some people brought to him a blind man and begged Jesus to touch him.
23 Yesu ya kama hannun makahon ya kai shi bayan ƙauyen. Bayan ya tofa miyau a idanun mutumin, ya kuma ɗibiya masa hannuwansa, sai ya tambaye shi ya ce, “Kana iya ganin wani abu?”
So he took the blind man by the hand and led him out of the village. Then he spit on the man's eyes, laid his hands on him, and asked him if he saw anything.
24 Sai ya ɗaga kai ya ce, “Ina ganin mutane, suna kama da itatuwa da suke tafiya.”
The man looked up and said, “I can see people, but they look like trees walking around.”
25 Yesu ya sāke ɗibiya hannuwansa a idanun mutumin, sai idanunsa suka buɗe, ya sami gani, ya kuma ga kome sarai.
So Jesus put his hands on the man's eyes again and had him look up. Then the man's sight was restored, and he saw everyone clearly.
26 Yesu ya sallame shi gida ya ce, “Kada ka shiga cikin ƙauyen.”
And Jesus sent him away to his house, saying, “Do not go into the village or tell anyone in the village what has happened.”
27 Yesu da almajiransa suka tafi ƙauyukan da suke kewaye da Kaisariya Filibbi. A hanya ya tambaye su ya ce, “Wa, mutane suke ce da ni?”
Then Jesus went on to the villages of Caesarea Philippi along with his disciples. On the way he asked his disciples, “Who do people say that I am?”
28 Suka amsa, suka ce, “Waɗansu suna cewa, Yohanna Mai Baftisma, waɗansu Iliya, waɗansu kuma har wa yau sun ce, ɗaya daga cikin annabawa.”
They answered, “Some say John the Baptist, others say Elijah, and others say that yoʋ are one of the prophets.”
29 Sai ya yi tambaya ya ce, “Amma ku fa, wa kuke ce da ni?” Bitrus ya amsa ya ce, “Kai ne Kiristi.”
He said to them, “But who do you say that I am?” Peter answered him, “Yoʋ are the Christ.”
30 Yesu ya gargaɗe su kada su gaya wa kowa kome a kansa.
And Jesus warned them not to tell anyone about him.
31 Sai ya fara koya musu cewa, dole Ɗan Mutum yă sha wahaloli da yawa, dattawa, manyan firistoci da malaman dokoki kuma su ƙi shi. Dole kuma a kashe shi, bayan kwana uku kuma, yă tashi.
Then he began to teach them that the Son of Man must suffer many things and be rejected by the elders, the chief priests, and the scribes, and that he must be killed and after three days rise again.
32 Ya yi wannan zance a sarari. Sai Bitrus ya jawo shi gefe, ya fara tsawata masa.
He was stating the matter plainly, so Peter took him aside and began to rebuke him.
33 Amma da Yesu ya juya ya dubi almajiransa, sai ya tsawata wa Bitrus ya ce, “Tashi daga nan Shaiɗan! Ba ka da al’amuran Allah a zuciyarka, sai na mutane.”
But turning around and looking at his disciples, he rebuked Peter, saying, “Get behind me, Satan! For yoʋ are not thinking about the things of God, but the things of men.”
34 Sai ya kira taron wurinsa tare da almajiransa ya ce, “Duk wanda zai bi ni, dole yă ƙi kansa, yă ɗauki gicciyensa yă bi ni.
Then he called the crowd over, along with his disciples, and said to them, “If anyone wants to be one of my disciples, he must deny himself, take up his cross, and follow me.
35 Domin duk mai son ceton ransa zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa saboda ni, da kuma bishara, zai same shi.
For whoever wants to save his life will lose it, but whoever loses his life for my sake and for the sake of the gospel will save it.
36 Me mutum zai amfana, in ya ribato duniya duka a bakin ransa?
For what will it benefit a person if he gains the whole world but forfeits his soul?
37 Ko kuma, me mutum zai bayar a musayar ransa?
Or what can a person give in exchange for his soul?
38 Duk wanda ya ji kunyata, da na kalmomina a wannan zamani na fasikanci da zunubi, Ɗan Mutum ma zai ji kunyarsa lokacin da ya shiga cikin ɗaukakar Ubansa, tare da tsarkakan mala’iku.”
If anyone is ashamed of me and my words in this adulterous and sinful generation, the Son of Man will also be ashamed of him when he comes in the glory of his Father with the holy angels.”

< Markus 8 >