< Markus 5 >
1 Suka ƙetare tafkin suka je yankin Gerasenawa.
Ayant passé la mer, ils arrivèrent au pays des Géraséniens.
2 Da Yesu ya sauka daga jirgin ruwa, sai wani mutum mai mugun ruhu ya fito daga kaburbura, ya tarye shi.
Et comme Jésus sortait de la barque, tout à coup vint à lui, du milieu des sépulcres, un homme possédé d’un esprit impur.
3 Wannan mutumin ya mai da kaburbura gidansa. Kuma ba wanda ya iya daure shi, ko da sarƙa ma.
Il avait sa demeure dans les sépulcres; et nul ne pouvait plus le tenir attaché, même avec une chaîne.
4 Gama an sha daure shi hannu da ƙafa da sarƙa, amma yakan tsintsinke sarƙar, yă kuma karye ƙarafan da suke ƙafafunsa. Ba wanda yake da ƙarfin da zai iya yă riƙe shi.
Car on l’avait souvent chargé de liens aux pieds et de chaînes, et il avait brisé les chaînes et rompu ses liens, de sorte que personne ne pouvait en être maître.
5 Dare da rana, sai yă dinga kuka yana ƙuƙƙuje jikinsa da duwatsu a cikin kaburbura da kan tuddai.
Sans cesse, le jour et la nuit, il errait au milieu des sépulcres et sur les montagnes, criant et se meurtrissant avec des pierres.
6 Da ya hangi Yesu daga nesa, sai ya ruga da gudu, ya zo ya durƙusa a gabansa.
Ayant aperçu Jésus de loin, il accourut, se prosterna devant lui,
7 Ya yi ihu da babbar murya ya ce, “Ina ruwanka da ni Yesu, Ɗan Allah Mafi Ɗaukaka? Ka rantse da Allah cewa ba za ka ba ni azaba ba!”
et, ayant poussé un cri, il dit d’une voix forte: « Qu’as-tu à faire avec moi, Jésus, fils du Dieu très haut? Je t’adjure au nom de Dieu, ne me tourmente pas. »
8 Gama Yesu ya riga ya ce masa, “Ka fita daga jikin mutumin nan, kai mugun ruhu!”
Car Jésus lui disait: « Esprit impur, sors de cet homme. »
9 Sai Yesu ya tambaye shi ya ce, “Mene ne sunanka?” Sai ya amsa ya ce, “Sunana Lejiyon, wato, ‘Tuli,’ domin muna da yawa.”
Et il lui demanda: « Quel est ton nom? » Et il lui dit: « Mon nom est Légion, car nous sommes nombreux. »
10 Sai ya yi ta roƙon Yesu, kada yă kore su daga wurin.
Et il le priait instamment de ne pas les envoyer hors de ce pays.
11 A kan tudun da yake nan kusa kuwa, akwai wani babban garken aladu, suna kiwo.
Or, il y avait là, le long de la montagne, un grand troupeau de porcs qui paissaient.
12 Sai aljanun suka roƙi Yesu, suka ce, “Tura mu cikin aladun nan, ka bari mu shiga cikinsu.”
Et les démons suppliaient Jésus, disant: « Envoies-nous dans ces pourceaux, afin que nous y entrions. »
13 Ya kuwa yarda musu, sai mugayen ruhohin suka fita suka shiga cikin aladun. Garken kuwa, yana da kusan aladu dubu biyu, suka gangara daga kan tudun zuwa cikin tafkin, suka nutse.
Il le leur permit aussitôt, et les esprits impurs, sortant du possédé, entrèrent dans les pourceaux, et le troupeau, qui était d’environ deux mille, se précipita des pentes escarpées dans la mer et s’y noya.
14 Masu kiwon aladun kuwa suka ruga da gudu zuwa cikin gari da ƙauyuka, suka ba da wannan labari. Sai mutanen suka fito, domin su ga abin da ya faru.
Ceux qui les gardaient s’enfuirent, et répandirent la nouvelle dans la ville et dans les campagnes. Les gens allèrent voir ce qui était arrivé;
15 Da suka kai wajen Yesu, sai suka ga mutumin da dā yake da tulin aljanun yana zaune a wurin, sanye da tufafi kuma cikin hankalinsa, sai suka ji tsoro.
ils vinrent à Jésus, et virent le démoniaque, celui qui avait eu la légion, assis, vêtu, et sain d’esprit, et ils furent saisis de frayeur.
16 Waɗanda suka ga abin da ya faru, suka ba da labarin abin da ya faru da mai aljanun, da kuma aladun.
Et ceux qui en avaient été témoins leur ayant raconté ce qui était arrivé au possédé et aux pourceaux,
17 Sai mutane suka fara roƙon Yesu yă bar yankinsu.
ils se mirent à prier Jésus de s’éloigner de leurs frontières.
18 Yesu yana kan shiga cikin jirgin ruwa ke nan, sai mutumin da dā yake da aljanun ya roƙa yă bi shi.
Comme Jésus montait dans la barque, celui qui avait été possédé lui demanda la permission de le suivre.
19 Yesu bai yardar masa ba, amma ya ce, “Ka tafi gida wurin iyalinka, ka gaya musu babban alherin da Ubangiji ya yi maka, da yadda ya yi maka jinƙai.”
Jésus ne le lui permit pas, mais il lui dit: « Va dans ta maison, auprès des tiens, et raconte-leur tout ce que le Seigneur a fait pour toi, et comment il a eu pitié de toi. »
20 Sai mutumin ya tafi, ya yi ta ba da labari a cikin Dekafolis a kan babban alherin da Yesu ya yi masa. Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
Il s’en alla, et se mit à publier dans la Décapole tout ce que Jésus avait fait pour lui: et tous étaient dans l’admiration.
21 Da Yesu ya sāke ƙetarewa cikin jirgin ruwa zuwa ɗaya hayen tafkin, sai taro mai yawa ya taru kewaye da shi yayinda yake a bakin tafkin.
Jésus ayant de nouveau traversé la mer dans la barque, comme il était près du rivage, une grande foule s’assembla autour de lui.
22 Sai ɗaya a cikin masu mulkin majami’a, wanda ake kira Yayirus ya zo wurin. Da ganin Yesu, sai ya durƙusa a gabansa,
Alors vint un des chefs de la synagogue, nommé Jaïre, qui en le voyant, se jeta à ses pieds,
23 ya roƙe shi da gaske ya ce, “Ƙaramar diyata tana bakin mutuwa. In ka yarda, ka zo ka ɗibiya hannunka a kanta, domin ta warke, ta kuma rayu.”
et le pria avec instance, disant: « Ma fille est à l’extrémité; viens, impose ta main sur elle, afin qu’elle soit guérie et qu’elle vive. »
24 Sai Yesu ya tafi tare da shi. Babban taron kuma ya bi shi, suna ta matsinsa a kowane gefe.
Et il s’en alla avec lui, et une grande multitude le suivait et le pressait.
25 A can kuwa akwai wata mace, wadda ta yi shekaru goma sha biyu tana zub da jini.
Or il y avait une femme affligée d’un flux de sang depuis douze années;
26 Ta kuma sha wahala ƙwarai a hannun likitoci da yawa, har ta kashe duk abin da take da shi, amma maimakon samun sauƙi, sai ciwon ya ƙara muni.
elle avait beaucoup souffert de plusieurs médecins, et dépensé tout son bien, et loin d’avoir éprouvé quelque soulagement, elle avait vu son mal empirer.
27 Da ta ji labarin Yesu, sai ta zo ta bayansa, a cikin taron, ta taɓa rigarsa,
Ayant entendu parler de Jésus, elle vint dans la foule et toucha par derrière son manteau.
28 domin ta yi tunani cewa, “Ko da rigunarsa ma na taɓa, zan warke.”
Car elle disait: « Si je touche seulement ses vêtements, je serai guérie. »
29 Nan da take, zub da jininta ya tsaya, sai ta ji a jikinta ta rabu da shan wahalarta.
Aussitôt le flux de sang s’arrêta et elle sentit en son corps qu’elle était guérie de son infirmité.
30 Nan da nan Yesu ya gane cewa, iko ya fita daga gare shi. Sai ya juya a cikin taron ya yi tambaya, “Wa ya taɓa rigata?”
Au même moment, Jésus connut en lui-même qu’une force était sortie de lui, et, se retournant au milieu de la foule, il dit: « Qui a touché mes vêtements? »
31 Sai almajiransa suka ce, “Kana ganin mutane suna matsinka, duk da haka kana tambaya, ‘Wa ya taɓa ni?’”
Ses disciples lui dirent: « Tu vois la foule qui te presse de tous côtés, et tu demandes: Qui m’a touché? »
32 Amma Yesu ya ci gaba da dubawa don yă ga wa ya taɓa shi.
Et il regardait autour de lui pour voir celle qui l’avait touché.
33 Matar, da yake ta san abin da ya faru da ita, sai ta zo ta durƙusa a gabansa, da tsoro da rawan jiki, ta kuma gaya masa dukan abin da ya faru.
Cette femme, tremblante de crainte, sachant ce qui s’était passé en elle, vint se jeter à ses pieds, et lui dit toute la vérité.
34 Sai ya ce mata, “Diyata, bangaskiyarki ta warkar da ke. Ki sauka lafiya, kin kuma rabu da dukan wahalarki.”
Jésus lui dit: « Ma fille, ta foi t’a sauvée; va en paix, et sois guérie de ton infirmité. »
35 Yayinda Yesu yana cikin magana, sai waɗansu mutane daga gidan Yayirus, mai mulkin majami’a, suka zo suka ce, “Diyarka ta rasu. Kada ma ka wahal da Malam.”
Il parlait encore, lorsqu’on vint de la maison du chef de synagogue lui dire: « Ta fille est morte, pourquoi fatiguer davantage le Maître? »
36 Yesu bai kula da abin da suka faɗa ba, sai ya ce wa mai mulkin majami’ar, “Kada ka ji tsoro, ka gaskata kawai.”
Mais Jésus entendant la parole qui venait d’être proférée, dit au chef de synagogue: « Ne crains rien, crois seulement. »
37 Bai bar kowa ya bi shi ba, sai Bitrus, Yaƙub da Yohanna ɗan’uwan Yaƙub.
Et il ne permit à personne de l’accompagner, si ce n’est à Pierre, à Jacques et à Jean, frère de Jacques.
38 Da suka iso gidan mai mulkin majami’ar, sai Yesu ya ga ana hayaniya, mutane suna kuka da kururuwa.
On arrive à la maison du chef de synagogue, et là il voit une troupe confuse de gens qui pleurent et poussent de grands cris.
39 Sai ya shiga ciki, ya ce musu, “Mene ne dalilin wannan hayaniya da kuka? Yarinyar ba mutuwa ne ta yi ba, barci take yi.”
Il entre et leur dit: « Pourquoi tout ce bruit et ces pleurs? L’enfant n’est pas morte, mais elle dort. »
40 Sai suka yi masa dariya. Bayan ya fitar da su duk waje, sai ya ɗauki mahaifin da mahaifiyar yarinyar tare da almajiran da suke tare da shi, suka shiga inda yarinyar take.
Et ils se moquaient de lui. Mais lui, les ayant tous fait sortir, prit avec lui le père et la mère de l’enfant, et les disciples qui l’accompagnaient, et entra dans le lieu où l’enfant était couchée.
41 Sai ya kama hannunta ya ce mata, “Talita kum!” (Wato, “Ƙaramar yarinya, na ce miki, tashi!”).
Et lui prenant la main, il lui dit: « Talitha qoumi, » c’est-à-dire: « Jeune fille, lève-toi, je te le dis. »
42 Nan da nan, sai yarinyar ta tashi ta yi tafiya (shekarunta goma sha biyu ne). Saboda wannan, suka yi mamaki ƙwarai.
Aussitôt la jeune fille se leva et se mit à marcher, car elle avait douze ans; et ils furent frappés de stupeur.
43 Sai ya ba da umarni mai tsanani, kada kowa yă san kome game da wannan. Sai ya ce musu, su ba ta wani abu tă ci.
Et Jésus leur défendit fortement d’en rien faire savoir à personne; puis il dit de donner à manger à la jeune fille.