< Markus 4 >

1 Har wa yau, Yesu ya fara koyarwa a bakin tafki. Domin taron da yake kewaye da shi mai girma ne sosai, sai ya shiga cikin jirgin ruwa, ya zauna a ciki a tafkin, dukan mutanen kuwa suna a gaɓar ruwan.
Jésus se mit de nouveau à enseigner au bord de la mer. Une si grande foule s’assembla auprès de lui, qu’il monta et s’assit dans la barque, sur la mer, et toute la foule était à terre le long du rivage.
2 Ya koya musu abubuwa da yawa da misalai. A koyarwarsa kuwa ya ce,
Et il leur enseignait beaucoup de choses en paraboles, et il leur disait dans son enseignement:
3 “Ku saurara! Wani manomi ya fita don yă shuka irinsa.
« Écoutez! Le semeur sortit pour semer.
4 Da yana yafa irin, sai waɗansu suka fāɗi a kan hanya, tsuntsaye suka zo suka cinye su.
Et comme il semait, des [grains] tombèrent le long du chemin, et les oiseaux vinrent et les mangèrent.
5 Waɗansu suka fāɗi a wuri mai duwatsu inda babu ƙasa sosai. Nan da nan, suka tsira domin ƙasar ba zurfi.
D’autres tombèrent sur un sol pierreux, où ils n’avaient pas beaucoup de terre; ils levèrent aussitôt, parce que la terre était peu profonde.
6 Amma da rana ta taso, sai tsire-tsiren suka ƙone, suka yanƙwane, domin ba su da saiwa.
Mais le soleil s’étant levé, la plante, frappée de ses feux et n’ayant pas de racine, sécha.
7 Waɗansu irin suka fāɗi a cikin ƙaya. Da suka yi girma sai ƙaya suka shaƙe su, har ya sa ba su yi ƙwaya ba.
D’autres grains tombèrent parmi les épines; et les épines montèrent et les étouffèrent, et ils ne donnèrent pas de fruit.
8 Har yanzu, waɗansu irin suka fāɗi a ƙasa mai kyau. Suka tsira, suka yi girma, suka ba da amfani, suka yi riɓi talatin-talatin, waɗansu sittin-sittin, waɗansu kuma ɗari-ɗari.”
D’autres tombèrent dans la bonne terre; montant et croissant, ils donnèrent leur fruit et rapportèrent l’un trente pour un, l’autre soixante et l’autre cent. »
9 Sai Yesu ya ce, “Duk mai kunnen ji, yă ji.”
Et il ajouta: « Que celui qui a des oreilles, entende bien. »
10 Lokacin da yake shi kaɗai, Sha Biyun, da kuma waɗanda suke kewaye da shi, suka tambaye shi game da misalan.
Lorsqu’il se trouva seul, ceux qui l’entouraient, avec les Douze, l’interrogèrent sur la parabole.
11 Sai ya ce musu, “An ba ku sanin asirin mulkin Allah. Amma ga waɗanda suke waje kuwa, kome sai da misalai.
Il leur dit: « À vous il a été donné de connaître le mystère du royaume de Dieu; mais pour eux, qui sont dehors, tout est annoncé en paraboles,
12 Saboda, “‘ko sun dinga duba, ba za su taɓa gane ba, kuma ko su dinga ji, ba za su taɓa fahimta ba, in ba haka ba, mai yiwuwa, su tuba, a gafarta musu!’”
afin qu’en regardant de leurs yeux ils ne voient pas, qu’en entendant de leurs oreilles ils ne comprennent pas: de peur qu’ils ne se convertissent et n’obtiennent le pardon de leurs péchés. »
13 Sai Yesu ya ce musu, “Ba ku fahimci wannan misali ba? Yaya za ku fahimci wani misali ke nan?
Il ajouta: « Vous ne comprenez pas cette parabole? Comment donc entendrez-vous toutes les paraboles?
14 Manomi yakan shuka maganar Allah.
Le semeur sème la parole.
15 Waɗansu mutane suna kama da irin da ya fāɗi a kan hanya, inda akan shuka maganar Allah. Da jin maganar, nan da nan sai Shaiɗan yă zo yă ɗauke maganar da aka shuka a zuciyarsu.
Ceux qui sont sur le chemin, ce sont les hommes en qui on sème la parole, et ils ne l’ont pas plus tôt entendue, que Satan vient et enlève la parole semée dans leurs cœurs.
16 Waɗansu suna kama da irin da aka shuka a wurare masu duwatsu, sukan ji maganar Allah, sukan kuma karɓe ta nan da nan da farin ciki.
Pareillement, ceux qui reçoivent la semence en un sol pierreux, ce sont ceux qui, dès qu’ils entendent la parole, la reçoivent avec joie;
17 Amma da yake ba su da saiwa, ba sa daɗewa. Da wahala ko tsanani ya tashi saboda maganar, nan da nan, sai su ja da baya.
mais il n’y a pas en eux de racines; ils sont inconstants: que survienne la tribulation ou la persécution à cause de la parole, ils succombent aussitôt.
18 Har yanzu, waɗansu kamar irin da aka shuka cikin ƙaya, sukan ji maganar,
Ceux qui reçoivent la semence dans les épines, ce sont ceux qui écoutent la parole;
19 amma damuwar wannan duniya, da son dukiya, da kuma kwaɗayin waɗansu abubuwa, sukan shiga, su shaƙe maganar, har su mai da ita marar amfani. (aiōn g165)
mais les sollicitudes du monde, et la séduction des richesses, et les autres convoitises entrant dans leurs cœurs, étouffent la parole, et elle ne porte pas de fruit. (aiōn g165)
20 Waɗansu mutane kuwa suna kama da irin da aka shuka a ƙasa mai kyau, sukan ji maganar Allah, su kuma karɓa, sa’an nan kuma su fid da amfani riɓi talatin-talatin, ko sittin-sittin, ko ɗari-ɗari.”
Enfin ceux où la semence tombe en bonne terre, ce sont ceux qui entendent la parole et la reçoivent, et produisent du fruit, trente, soixante, et cent pour un. »
21 Sai ya ce musu, “Ko kukan kawo fitila ku rufe ta da murfi ko kuma ku sa ta a ƙarƙashin gado ne? Ba kukan sa ta a kan wurin ajiye fitila ba?
Il leur dit encore: « Apporte-t-on la lampe pour la mettre sous le boisseau ou sous le lit? N’est-ce pas pour la mettre sur le chandelier?
22 Duk abin da yake a ɓoye, dole za a fallasa shi. Duk abin da kuma yake a rufe, dole za a fitar da shi a fili.
Car il n’y a rien de caché qui ne doive être révélé, rien ne se fait en secret qui ne doive venir au jour.
23 Duk mai kunnen ji, bari yă ji.”
Si quelqu’un a des oreilles, qu’il entende bien. »
24 Ya ci gaba da cewa, “Ku lura da abin da kuke ji da kyau. Mudun da ka auna da shi, da shi za a auna maka, har ma a ƙara.
Et il ajouta: « Prenez garde à ce que vous entendez. Selon la mesure avec laquelle vous aurez mesuré, on vous mesurera, et on y ajoutera encore pour vous.
25 Duk wanda yake da shi, za a ƙara masa, duk wanda kuma ba shi da shi, ko abin da yake da shi ma, za a karɓe daga gare shi.”
Car on donnera à celui qui a déjà, et à celui qui n’a pas, même ce qu’il a, lui sera ôté. »
26 Ya sāke cewa, “Mulkin Allah yana kama da haka. Wani mutum ya yafa iri a gona.
Il dit encore: « Il en est du royaume de Dieu comme d’un homme qui jette en terre de la semence.
27 A kwana a tashi har irin yă tsiro, yă yi girma, bai kuwa santa yadda aka yi ba.
Il dort et il se lève, la nuit et le jour, et la semence germe et croît, sans qu’il sache comment.
28 Ƙasar da kanta takan ba da ƙwaya, da farko takan fid da ƙara, sa’an nan ta fid da kai, sa’an nan kan yă fid da ƙwaya.
Car la terre produit d’elle-même du fruit: d’abord de l’herbe, puis un épi, et l’épi ensuite s’emplit de froment.
29 Da ƙwayan ya nuna, sai yă sa lauje yă yanka, domin lokacin girbi ya yi.”
Et quand le fruit est mûr, aussitôt on y met la faucille, parce que c’est le temps de la moisson. »
30 Ya kuma ce, “Da me za mu kwatanta mulkin Allah, ko kuwa da wane misali za mu bayyana shi?
Il dit encore: « À quoi comparerons-nous le royaume de Dieu? ou par quelle parabole le représenterons-nous?
31 Yana kama da ƙwayar mustad, wadda ita ce ƙwaya mafi ƙanƙanta da akan shuka a gona.
Il est semblable à un grain de sénevé qui, lorsqu’on le sème en terre, est la plus petite de toutes les semences qu’il y ait sur la terre;
32 Duk da haka, in aka shuka ƙwayar, sai tă yi girma, tă zama mafi girma a itatuwan lambu. Har itacen yă kasance da manyan rassa, inda tsuntsayen sararin sama sukan iya huta a inuwarsa.”
et lorsqu’on l’a semé, il monte et devient plus grand que toutes les plantes potagères, et il étend si loin ses rameaux, que les oiseaux du ciel peuvent s’abriter sous son ombre. »
33 Da misalai da yawa irin waɗannan, Yesu ya yi magana da su, daidai yadda za su iya fahimta.
Il les enseignait ainsi par diverses paraboles, selon qu’ils étaient capables de l’entendre.
34 Ba abin da ya faɗa musu, da ba da misali ba. Amma lokacin da yake shi kaɗai tare da almajiransa, sai yă bayyana kome.
Il ne leur parlait pas sans paraboles, mais, en particulier, il expliquait tout à ses disciples.
35 A wannan rana, da yamma, sai ya ce wa almajiransa, “Mu ƙetare zuwa wancan hayi.”
Ce jour-là, sur le soir, il leur dit: « Passons à l’autre bord. »
36 Da suka bar taron, sai suka tafi tare da shi yadda yake, a cikin jirgin ruwa. Akwai waɗansu jiragen ruwa kuma tare da shi.
Ayant renvoyé la foule, ils prirent avec eux Jésus, tel qu’il était, dans la barque, et d’autres petites barques l’accompagnaient.
37 Sai babban hadari mai iska ya tashi, raƙuman ruwa suna ta bugun jirgin ruwan, har jirgin ruwan ya kusa yă cika da ruwa.
Alors il s’éleva un tourbillon de vent impétueux qui poussait les flots contre la barque, de sorte que déjà elle s’emplissait d’eau.
38 Yesu kuwa yana can baya, yana barci a kan katifa. Sai almajiran suka tashe shi suka ce masa, “Malam, ba ka kula ba ko mu nutse?”
Lui cependant était à la poupe, dormant sur le coussin; ils le réveillèrent et lui dirent: « Maître, n’avez-vous pas de souci que nous périssions? »
39 Sai ya farka ya tsawata wa iskar, ya ce wa raƙuman ruwan, “Shiru! Ku natsu!” Sai iskar ta kwanta, kome kuma ya yi tsit.
Jésus étant réveillé tança le vent, et dit à la mer: « Tais-toi, calme-toi. » Et le vent s’apaisa, et il se fit un grand calme.
40 Sai ya ce wa almajiransa, “Don me kuke tsoro haka? Har yanzu ba ku da bangaskiya ne?”
Et il leur dit: « Pourquoi êtes-vous effrayés? N’avez-vous pas encore la foi?
41 Suka tsorata, suka ce wa juna, “Wane ne wannan? Har iska da raƙuman ruwa ma suna masa biyayya!”
» Et ils furent saisis d’une grande crainte, et ils se disaient l’un à l’autre: « Qui donc est celui-ci, que le vent et la mer lui obéissent? »

< Markus 4 >