< Luka 1 >

1 Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
Seeing, indeed, that, many, had taken in hand to re-arrange for themselves a narrative, concerning the facts which have been fully confirmed amongst us, —
2 kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
according as they who from the beginning became eye-witnesses and attendants of the Word delivered them unto us,
3 Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
it seemed good, even to me, having closely traced from the outset all things accurately, to write unto thee, in order, most excellent Theophilus:
4 don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
that, as touching the matters which thou hadst been taught by word of mouth, thou mightest obtain full knowledge, of the certainty.
5 A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
It came to pass, in the days of Herod, king of Judaea, that there was a certain priest, by name Zachariah, of the daily course of Abia; and that he had a wife of the daughters of Aaron, and, her name, was Elizabeth.
6 Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
Now they were both righteous before God, walking in all the commandments and righteous appointments of the Lord, blameless;
7 Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
and they had no child, inasmuch as Elizabeth was barren, and, both, had become, advanced in their days.
8 Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
But it came to pass, as he was doing priestly service in the order of his daily course, before God,
9 sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
according to the custom of his priesthood, it fell to his lot to offer incense, entering into the Temple of the Lord;
10 Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
and, all the throng of the people, was praying outside, at the hour of the incense offering.
11 Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
And there appeared unto him a messenger of the Lord, standing on the right hand of the altar of incense;
12 Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
and Zachariah was troubled when he beheld, and, fear, fell upon him.
13 Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
But the messenger said unto him—Do not fear, Zachariah! Inasmuch as thy supplication hath been hearkened to, —and, thy wife Elizabeth, shall bring forth a son to thee, and thou shalt call his name, John;
14 Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
And there shall be joy to thee and exulting, and, many, over his birth, shall rejoice;
15 gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
For he shall be great before the Lord, and, wine and strong drink, in nowise may he drink, and, with Holy Spirit, shall he be filled, already, from his mother’s womb;
16 Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
And, many of the Sons of Israel, shall he turn towards the Lord their God;
17 Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
And, he, shall go before him, in the spirit and power of Elijah, —To turn the hearts of fathers unto children, and the unyielding, into the prudence of the righteous, and to prepare, for the Lord, a people made ready.
18 Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
And Zachariah said unto the messenger—Whereby, shall I know this? for, I, am, aged, and, my wife, advanced in her days.
19 Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
And the messenger, answering, said unto him—I, am Gabriel, —he that standeth near before God; and have been sent forth to speak unto thee, and to deliver the joyful message unto thee, as touching these things.
20 Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
And lo! thou shalt be silent, and not able to speak until the day when these things shall come to pass; because thou didst not believe in my words, —the which shall be fulfilled for their season.
21 Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
And the people were expecting Zachariah, and began to marvel that he should tarry in the Temple;
22 Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
and when he came forth he was not able to speak unto them, and they perceived that, a vision, he had seen in the Temple, —and, he, continued making signs unto them, and remained dumb.
23 Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
And it came to pass, when the days of his public ministration were fulfilled, that he departed unto his house.
24 Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
And, after these days, Elizabeth his wife conceived, and she disguised herself five months, saying—
25 Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
Thus, for me, hath the Lord wrought, —in the days in which he looked upon me, to take away my reproach among men.
26 A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
Now, in the sixth month, was the messenger Gabriel sent forth from God, into a city of Galilee, the name of which was Nazareth, —
27 gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
unto a virgin, betrothed to a man whose name was Joseph, of the house of David; and, the name of the virgin, was, Mary;
28 Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
and entering in unto her, he said—Joy to thee, favoured one! The Lord, be with thee!
29 Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
And, she, at the word, was greatly troubled, and began to deliberate, of what kind, this salutation, might be.
30 Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
And the messenger said unto her—Do not fear, Mary, for thou hast found favour with God, —
31 Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
And lo! thou shalt conceive in thy womb, and bring forth a son, and shalt call his name, Jesus:
32 Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
the same, shall be great, and, Son of the Most High, shall be called, and the Lord God, will give unto him, the throne of David his father, —
33 zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
And he shall reign over the house of Jacob, unto the ages, and, of his kingdom, there shall be, no end. (aiōn g165)
34 Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
But Mary said unto the messenger—How, shall this thing be, seeing that, a man, I know not?
35 Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
And answering, the messenger said unto her—The Holy Spirit, shall come upon thee, and, the power of the Most High, shall overshadow thee; wherefore, even that which is to be born, Holy, shall be called, Son of God.
36 ’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
And lo! Elizabeth thy kinswoman, even she, hath conceived a son in, her old-age; —and, this month, is, the sixth, to her, the so-called barren one;
37 Gama ba abin da zai gagari Allah.”
Because no declaration from God, shall be void of power.
38 Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
And Mary said—Lo! the handmaid of the Lord! Might it come to pass unto me, according to thy declaration. And the messenger departed from her.
39 A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
And Mary, arising, in these days, journeyed into the hill country with haste, into a city of Judah, —
40 inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
and entered into the house of Zachariah, and saluted Elizabeth.
41 Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
And it came to pass that, as Elizabeth heard the salutation of Mary, the babe leapt in her womb, and Elizabeth was filled with Holy Spirit, —
42 Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
and lifted up her voice with loud exclamation, and said—Blessed, art thou among women, and, blessed, is the fruit of thy womb;
43 Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
And, whence, to me is, this, That the mother of my Lord should come, unto me?
44 Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
For lo! as the sound of thy salutation came into mine ears, the babe in my womb, leapt in exultation.
45 Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
And, happy, is she who hath believed, that there shall be a perfecting of the things which have been spoken to her from the Lord!
46 Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
And Mary said—My soul doth magnify the Lord,
47 ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
And my spirit hath exulted upon God my saviour;
48 gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
Because he hath looked upon the humbling of his handmaid; for lo! from the present time, all the generations, will pronounce me happy.
49 gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
Because he that is mighty hath done for me great things, and, holy, is his name;
50 Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
And his mercy is unto generations and generations, to them who revere him;
51 Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
He hath wrought strength with his arm, He hath scattered men arrogant in the intention of their heart;
52 Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
He hath deposed potentates from thrones, and uplifted the lowly;
53 Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
The hungry, hath he filled with good things, and, the wealthy, hath he sent empty away;
54 Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
He hath laid hold of Israel his servant, to be mindful of mercies:
55 ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
According as he spake unto our fathers, —To Abraham, and to his seed, —Unto times age-abiding. (aiōn g165)
56 Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
And Mary abode with her about three months, and returned unto her house.
57 Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
And, to Elizabeth, was the time fulfilled, that she should be bringing forth, —and she gave birth to a son.
58 Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
And her neighbours and kinsfolk heard, that the Lord had magnified his mercy with her, and they were rejoicing with her.
59 A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
And it came to pass, on the eighth day, that they came to circumcise the child, and were calling it, after the name of its father, Zachariah.
60 amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
And his mother, answering, said—Nay! but he shall be called, John.
61 Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
And they said unto her—There is, no one from among thy kindred, who is called by this name!
62 Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
And they began making signs unto his father, as to what he might be wishing it to be called.
63 Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
And, asking for a small tablet, he wrote, saying—John, is his name! and they marvelled all.
64 Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
And his mouth was opened instantly, and his tongue [loosed], and he began to speak, blessing, God.
65 Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
And fear came upon all the neighbours themselves; and, throughout all the hill-country of Judaea, were all these matters being much talked of;
66 Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
and all who heard laid [them] up in their hearts, saying—What then shall his child be? for, even the hand of the Lord, was with him.
67 Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
And, Zachariah his father, was filled with Holy Spirit, and prophesied, saying: —
68 “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
Blessed, be the Lord, the God of Israel! Because he hath visited and wrought redemption for his people,
69 Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
And hath raised up a horn of salvation for us, In the house of David his servant:
70 (yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
According as he hath spoken by mouth of his holy ancient prophets, — (aiōn g165)
71 cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
Of salvation from among our foes, and out of the hand of all them that hate us:
72 don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
To perform mercy with our fathers, and to be mindful of his holy covenant, —
73 rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
The oath which he sware unto Abraham our father, To grant us,
74 don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
without fear, from the hand of enemies rescued, to be rendering divine service unto him,
75 cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
in lovingkindness and righteousness before him, all our days.
76 “Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
And, even thou, child, prophet of the Most High, shalt be called, —for thou shall march on before the Lord, to prepare his ways,
77 don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
Giving a knowledge of salvation unto his people, by a remission of their sins.
78 saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
Because of the yearning compassion of the mercy of our God, wherein shall visit us a day-dawn from on high, —
79 don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
To shine on them who, in the darkness and shade of death, are sitting, to guide our feet into a way of peace.
80 Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.
And, the child, went on growing, and being strengthened in spirit, and was in the deserts, until the day he was pointed out unto Israel.

< Luka 1 >