< Luka 6 >

1 A wata ranar Asabbaci, Yesu yana bi ta gonakin hatsi, sai almajiran suka fara kakkarya kan hatsi suna murjewa a hannuwansu suna ci.
And it came to pass on the second sabbath after the first, that he went through corn-fields; and his disciples plucked the ears of corn, and ate, rubbing [them] in [their] hands.
2 Sai waɗansu Farisiyawa suka ce, “Me ya sa kuke yin abin da doka ta hana yi a ranar Asabbaci?”
And certain of the Pharisees said to them, Why do ye that which it is not lawful to do on the sabbath-days?
3 Yesu ya amsa musu ya ce, “Ashe, ba ku taɓa karanta abin da Dawuda ya yi, sa’ad da shi da abokan tafiyarsa suka ji yunwa ba?
And Jesus answering them, said, Have ye not read so much as this, what David did, when himself was hungry, and they who were with him;
4 Ya shiga gidan Allah, ya ɗauki keɓaɓɓen burodi, sa’an nan ya ci abin da firistoci kaɗai sukan ci bisa ga doka. Ya kuma ba wa abokan tafiyarsa?”
How he went into the house of God, and took and ate the show-bread, and gave also to them that were with him, which it is not lawful to eat but for the priests alone?
5 Sai Yesu ya ce musu, “Ai, Ɗan Mutum ne Ubangijin Asabbaci.”
And he said to them, That the Son of man is Lord also of the sabbath.
6 A wata ranar Asabbaci kuma, Yesu ya shiga majami’a yana koyarwa. To, a nan kuwa akwai wani mutumin da hannun damansa ya shanye.
And it came to pass also on another sabbath, that he entered into the synagogue, and taught: and there was a man whose right hand was withered:
7 Farisiyawa da malaman dokoki suka zuba wa Yesu ido, su ga ko zai warkar a ranar Asabbaci, don su sami dalilin zarginsa.
And the scribes and Pharisees watched him, [to see] whether he would heal on the sabbath; that they might find an accusation against him.
8 Amma Yesu ya san abin da suke tunani. Sai ya ce wa mutumin mai shanyayyen hannun, “Tashi ka tsaya a gaban kowa.” Sai ya tashi ya tsaya.
But he knew their thoughts, and said to the man who had the withered hand, Rise, and stand forth in the midst. And he arose, and stood forth.
9 Yesu ya ce musu, “Ina tambayarku, me ya kamata a yi bisa ga doka, a ranar Asabbaci, a aikata alheri ko a aikata mugunta, a ceci rai, ko a hallaka shi?”
Then said Jesus to them, I will ask you one thing; Is it lawful on the sabbath-days to do good, or to do evil? to save life, or to destroy [it]?
10 Sai ya kalle su duka, sa’an nan ya ce wa mutumin, “Miƙo hannunka.” Sai ya miƙe, hannunsa kuwa ya koma lafiyayye.
And looking around upon them all, he said to the man, Stretch forth thy hand. And he did so: and his hand was restored whole as the other.
11 Amma Farisiyawa da malaman Doka suka fusata, suka fara tattauna da junansu a kan abin da za su yi wa Yesu.
And they were filled with madness; and communed one with another what they might do to Jesus.
12 Wata rana, a cikin kwanakin nan, Yesu ya je wani dutse domin yă yi addu’a, ya kuma kwana yana addu’a ga Allah.
And it came to pass in those days, that he went out to a mountain to pray, and continued all night in prayer to God.
13 Da gari ya waye, sai ya kira almajiransa zuwa wurinsa, ya zaɓi guda goma sha biyu daga cikinsu, waɗanda ya kira su, Manzanni.
And when it was day, he called [to him] his disciples: and of them he chose twelve, whom also he named Apostles;
14 Siman (wanda ya kira Bitrus), ɗan’uwansa Andarawus, Yaƙub, Yohanna, Filibus, Bartolomeyu,
Simon (whom he also named Peter) and Andrew his brother, James and John, and Philip and Bartholomew,
15 Mattiyu, Toma, Yaƙub ɗan Alfayus, Siman wanda ake kira Zilot,
Matthew and Thomas, James the [son] of Alpheus, and Simon called Zelotes,
16 Yahuda ɗan Yaƙub, da kuma Yahuda Iskariyot, wanda ya bashe Yesu.
And Judas [the brother] of James, and Judas Iscariot, who also was the traitor.
17 Sai ya sauko tare da su, ya tsaya a wani fili. A can, akwai taro mai yawa na almajiransa, da kuma mutane masu yawan gaske daga ko’ina a Yahudiya, Urushalima da kuma Taya da Sidon da suke bakin teku,
And he came down with them, and stood in the plain; and the company of his disciples, and a great multitude of people out of all Judea and Jerusalem, and from the sea-coast of Tyre and Sidon, who came to hear him, and to be healed of their diseases;
18 waɗanda suka zo domin su ji shi, a kuma warkar da cututtukansu. Waɗanda suke fama da mugayen ruhohi kuwa aka warkar da su.
And they that were afflicted with unclean spirits: and they were healed.
19 Kuma dukan mutane suka yi ƙoƙari su taɓa shi, domin iko yana fitowa daga gare shi, ya kuwa warkar da su duka.
And the whole multitude sought to touch him; for there went virtue out of him, and healed [them] all.
20 Da ya dubi almajiransa, sai ya ce, “Masu albarka ne ku da kuke matalauta, gama mulkin Allah naku ne.
And he lifted up his eyes on his disciples, and said, Blessed [are ye] poor: for yours is the kingdom of God.
21 Masu albarka ne ku da kuke jin yunwa yanzu, gama za ku ƙoshi. Masu albarka ne ku da kuke kuka yanzu, gama za ku yi dariya.
Blessed [are] ye that hunger now: for ye shall be filled. Blessed [are ye] that weep now: for ye shall laugh.
22 Masu albarka ne sa’ad da mutane suka ƙi ku, suka ware ku, suka zage ku, suna ce da ku mugaye, saboda Ɗan Mutum.
Blessed are ye when men shall hate you, and when they shall separate you [from their company], and shall reproach [you], and cast out your name as evil, on account of the son of man.
23 “Ku yi farin ciki a wannan rana, ku kuma yi tsalle don murna, saboda ladarku yana da yawa a sama. Gama haka kakanninsu suka yi wa annabawa.
Rejoice ye in that day, and leap for joy: for behold, your reward [is] great in heaven: for in the like manner did their fathers to the prophets.
24 “Amma kaitonku da kuke da arziki, gama kun riga kun sami ta’aziyyarku.
But woe to you that are rich! for ye have received your consolation.
25 Kaitonku da kuke ƙosassu yanzu, gama za ku zauna da yunwa. Kaitonku da kuke dariya yanzu, gama za ku yi makoki da kuka.
Woe to you that are full! for ye shall hunger. Woe to you that laugh now! for ye shall mourn and weep.
26 Kaitonku sa’ad da dukan mutane suna magana mai kyau a kanku, gama haka kakanninsu suka yi da annabawan ƙarya.
Woe to you, when all men shall speak well of you! for so did their fathers to the false prophets.
27 “Amma ina faɗa muku, ku da kuke ji na, ku ƙaunaci abokan gābanku, ku yi wa masu ƙinku alheri.
But I say to you who hear, Love your enemies, do good to them who hate you,
28 Ku albarkaci waɗanda suke la’anta ku, ku kuma yi wa waɗanda suke wulaƙanta ku addu’a.
Bless them that curse you, and pray for them who despitefully use you.
29 In wani ya mare ka a wannan kumatu, juya masa ɗayan ma, in wani ya ƙwace maka babban riga, kada ma ka hana masa’yar cikin ma.
And to him that smiteth thee on the [one] cheek, offer also the other; and him that taketh away thy cloke, forbid not [to take thy] coat also.
30 Duk wanda ya roƙe ka abu, ka ba shi. In kuma wani ya yi maka ƙwace, kada ka nema yă mayar maka.
Give to every man that asketh of thee; and of him that taketh away thy goods, ask [them] not again.
31 Ka yi wa waɗansu abin da kai kake so su yi maka.
And as ye would that men should do to you, do ye also to them likewise.
32 “In kana ƙaunar masu ƙaunarka ne kawai, ina ribar wannan? Ko masu zunubi ma suna ƙaunar waɗanda suke ƙaunarsu.
For if ye love them who love you, what thanks have ye? for sinners also love those that love them.
33 In kuma kana yin alheri ga masu yi maka ne kaɗai, ina ribar wannan? Ko masu zunubi ma suna yin haka.
And if ye do good to them who do good to you, what thanks have ye? for sinners also do even the same.
34 In kana ba da bashi ga mutanen da za su iya biyan ka ne kawai, ina ribar wannan? Ko masu zunubi ma, suna ba da bashi ga masu zunubi, da fata za a biya su tsab.
And if ye lend [to them] from whom ye hope to receive, what thanks have ye? for sinners also lend to sinners, to receive as much in return.
35 Amma, ku ƙaunaci abokan gābanku, ku kuma yi musu alheri, ku ba su bashi, ba da sa zuciya sai an biya ku ba. Ta yin haka ne kawai, za ku sami lada mai yawa, ku kuma zama’ya’yan Mafi Ɗaukaka, gama shi mai alheri ne ga marasa godiya da mugaye.
But love ye your enemies, and do good, and lend, hoping for nothing again; and your reward shall be great, and ye shall be the children of the Highest: for he is kind to the unthankful and [to] the evil.
36 Ku zama masu jinƙai, kamar yadda Ubanku mai jinƙai ne.
Be ye therefore merciful, as your Father also is merciful.
37 “Kada ku ɗora wa wani, ku ma ba za a ɗora muku ba. Kada ku yanke wa wani hukunci, ku ma ba za a yanke muku ba. Ku gafarta, ku ma za a gafarta muku.
Judge not, and ye shall not be judged: condemn not, and ye shall not be condemned: forgive, and ye shall be forgiven:
38 Ku bayar, ku ma sai a ba ku mudu a cike, a danƙare, har yă yi tozo, yana zuba, za a juye muku a hannun riga. Mudun da kuka auna da shi, da shi za a auna muku.”
Give, and it shall be given to you; good measure, pressed down, and shaken together, and running over, shall men give into your bosom. For with the same measure that ye give [to others], it shall be measured to you again.
39 Ya kuma faɗa musu wannan misali cewa, “Makaho yana iya jagoran makaho ne? Ba sai dukansu biyu su fāɗa a rami ba?
And he spoke a parable to them; Can the blind lead the blind? will they not both fall into the ditch?
40 Ɗalibi bai fi malaminsa ba, sai dai kowane ɗalibi wanda ya sami cikakkiyar koyarwa, zai zama kamar malaminsa.
The disciple is not above his master: but every one that is perfect, shall be as his master.
41 “Don me kake duban ɗan tsinke da yake idon ɗan’uwanka, amma ba ka kula da gungumen da yake a naka ido ba?
And why beholdest thou the mote that is in thy brother's eye, but perceivest not the beam that is in thy own eye?
42 Yaya za ka ce wa ɗan’uwanka, ‘Ɗan’uwa, bari in cire maka ɗan tsinke da yake idonka,’ alhali kuwa, kai kanka ka kāsa ganin gungumen da yake a naka ido? Kai munafuki! Ka fara cire gungumen daga idonka, sa’an nan za ka iya gani sosai, ka kuma cire ɗan tsinken da yake a idon ɗan’uwanka.”
Either how canst thou say to thy brother, Brother, let me pull out the mote that is in thy eye, when thou thyself beholdest not the beam that is in thy own eye? Thou hypocrite, cast out first the beam out of thy own eye, and then shalt thou see clearly to pull out the mote that is in thy brother's eye.
43 “Ba itace mai kyau da yake ba da munanan’ya’ya. Mummunan itace kuma ba ya ba da’ya’ya masu kyau.
For a good tree bringeth not forth corrupt fruit; neither doth a corrupt tree bring forth good fruit.
44 Kowane itace da irin’ya’yansa ne ake saninsa. Mutane ba sa tsinke’ya’yan ɓaure daga ƙaya, ko kuwa’ya’yan inabi daga sarƙaƙƙiya.
For every tree is known by its own fruit: for from thorns men do not gather figs, nor from a bramble bush do they gather grapes.
45 Mutumin nagari yakan nuna abubuwa nagari daga cikin nagarta da yake a ɓoye a zuciyarsa, mugun mutum kuwa yakan nuna mugayen abubuwa daga muguntar da take a ɓoye a zuciyarsa. Gama baki yakan faɗa abin da ya cika zuciya ne.”
A good man out of the good treasure of his heart, bringeth forth that which is good; and an evil man out of the evil treasure of his heart, bringeth forth that which is evil: for from the abundance of the heart his mouth speaketh.
46 “Don me kuke ce da ni, ‘Ubangiji, Ubangiji,’ amma ba kwa yin abin da na faɗa?
And why call ye me Lord, Lord, and do not the things which I say?
47 Zan nuna muku kwatancin mutumin da yakan zo wurina, yă ji kalmomina, yă kuma aikata.
Whoever cometh to me, and heareth my sayings, and doeth them, I will show you to whom he is like.
48 Yana kama da mutumin da ya gina gida, wanda ya haƙa ƙasa da zurfi, sa’an nan ya kafa tushen ginin a kan dutse. Da ambaliyar ruwa ta taso, ƙarfin ruwa kuwa ya buga gidan, wannan bai jijjiga shi ba, domin an yi masa tushen gini na ainihi.
He is like a man who built a house, and digged deep, and laid the foundation on a rock: and when the flood arose, the stream beat vehemently upon that house, and could not shake it: for it was founded upon a rock.
49 Amma wanda yakan ji kalmomina, ba ya kuma aikata su, yana kama da mutumin da ya gina gida a ƙasa, ba tare da ya kafa tushen gini ba. A sa’ad da ƙarfin ruwa ya buga gidan, sai gidan yă rushe, mummunar rushewa kuwa.”
But he that heareth, and doeth not, is like a man that, without a foundation, built a house on the earth, against which the stream beat vehemently, and immediately it fell, and the ruin of that house was great.

< Luka 6 >