< Luka 4 >

1 Yesu kuwa cike da Ruhu Mai Tsarki, ya dawo daga Urdun, Ruhu kuma ya kai shi cikin hamada,
And Jesus being full of the Holy Spirit, returned from Jordan, and was led by the Spirit into the wilderness,
2 inda kwana arba’in, Iblis ya gwada shi. Bai ci kome ba a cikin kwanakin nan, a ƙarshensu kuwa ya ji yunwa.
Being forty days tempted by the devil. And in those days he ate nothing; and when they were ended, he was afterward hungry.
3 Iblis ya ce masa, “In kai Ɗan Allah ne, ka faɗa wa wannan dutse yă zama burodi.”
And the devil said to him, If thou art the Son of God, command this stone that it be made bread.
4 Yesu ya amsa ya ce, “A rubuce yake, ‘Ba da abinci kaɗai mutum zai rayu ba.’”
And Jesus answered him, saying, It is written, That man shall not live by bread alone, but by every word of God.
5 Iblis ya kai shi can kan wani wuri mai tsawo, ya nunnuna masa a ƙyiftawar ido dukan mulkokin duniya.
And the devil taking him up upon a high mountain, showed to him all the kingdoms of the world in a moment of time.
6 Ya ce masa, “Zan ba ka dukan ikonsu da darajarsu, gama ni aka danƙa wa, kuma zan bai wa duk wanda na ga dama.
And the devil said to him, All this power will I give thee, and the glory of them: for that is delivered to me, and to whomsoever I will, I give it.
7 Saboda haka in ka yi mini sujada, dukan wannan zai zama naka.”
If thou therefore wilt worship me, all shall be thine.
8 Yesu ya amsa ya ce, “A rubuce yake, ‘Ka yi wa Ubangiji Allahnka sujada, kuma shi kaɗai za ka bauta wa.’”
And Jesus answered and said to him, Get thee behind me, Satan: for it is written, Thou shalt worship the Lord thy God, and him only shalt thou serve.
9 Sai Iblis, ya kai shi Urushalima ya sa ya tsaya a kan wuri mafi tsayi na haikali ya ce, “In kai Ɗan Allah ne, ka yi tsalle daga nan zuwa ƙasa.
And he brought him to Jerusalem, and set him on a pinnacle of the temple, and said to him, If thou art the son of God, cast thyself down from hence.
10 Gama a rubuce yake, “‘Zai umarci mala’ikunsa game da kai, su kiyaye ka da kyau;
For it is written, He will give his angels charge over thee, to keep thee:
11 za su tallafe ka da hannuwansu, don kada ka buga ƙafarka a kan dutse.’”
And in [their] hands they will bear thee up, lest at any time thou dash thy foot against a stone.
12 Yesu ya amsa ya ce, “An ce, ‘Kada ka gwada Ubangiji Allahnka.’”
And Jesus answering, said to him, It is said, Thou shalt not tempt the Lord thy God.
13 Da Iblis ya gama dukan wannan gwajin, ya bar shi sai lokacin da wata dama ta samu.
And when the devil had ended all the temptation, he departed from him for a season.
14 Yesu ya koma Galili cikin ikon Ruhu. Labarinsa kuwa ya bazu ko’ina a ƙauyuka.
And Jesus returned in the power of the spirit into Galilee: and there went out a fame of him through all the surrounding region.
15 Ya yi ta koyarwa a majami’unsu, kowa kuwa ya yabe shi.
And he taught in their synagogues, being glorified by all.
16 Ya tafi Nazaret, inda aka yi renonsa. A ranar Asabbaci kuma, ya shiga majami’a kamar yadda ya saba. Sai ya miƙe don yă yi karatu.
And he came to Nazareth, where he had been brought up: and, as his custom was, he went into the synagogue on the sabbath, and stood up to read.
17 Aka kuwa ba shi naɗaɗɗen littafin annabi Ishaya. Da ya buɗe, sai ya sami wurin da aka rubuta,
And there was delivered to him the book of the prophet Isaiah. And when he had opened the book, he found the place where it was written,
18 “Ruhun Ubangiji yana kaina, domin ya shafe ni, in yi wa matalauta wa’azin bishara. Ya aiko ni in yi shelar’yanci ga’yan kurkuku, in kuma buɗe idanun makafi, in ba da’yanci ga waɗanda aka danne.
The spirit of the Lord [is] upon me, because he hath anointed me to preach the gospel to the poor; he hath sent me to heal the broken-hearted, to preach deliverance to the captives, and recovering of sight to the blind, to set at liberty them that are bruised,
19 In yi shelar shekarar tagomashin Ubangiji.”
To preach the acceptable year of the Lord.
20 Sai ya naɗe naɗaɗɗen littafin ya mayar wa mai hidimar, ya kuma zauna. Dukan idanun waɗanda suke a majami’ar, suka koma a kansa.
And he closed the book, and he gave [it] again to the minister, and sat down. And the eyes of all them that were in the synagogue were fastened on him.
21 Sai ya fara ce musu, “A yau, Nassin nan, ya cika a kunnenku.”
And he began to say to them, This day is this scripture fulfilled in your ears.
22 Duk suka yabe shi, suka yi mamakin kalmomin alheri da suke fitowa daga bakinsa. Suka yi tambaya, suna cewa, “Anya, wannan ba ɗan Yusuf ba ne?”
And all bore him testimony, and wondered at the gracious words which proceeded out of his mouth. And they said, Is not this Joseph's son?
23 Yesu ya ce musu, “Tabbatacce, na san za ku faɗa mini karin maganan nan, ‘Likita, warkar da kanka! Ka kuma yi abin da muka ji ka yi a Kafarnahum, a nan garinka.’”
And he said to them, Ye will surely say to me this proverb, Physician, heal thyself: whatever we have heard done in Capernaum, do also here in thy country.
24 Ya ci gaba, da ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, babu annabin da ake yarda da shi a garinsa.
And he said, Verily I say to you, No prophet is accepted in his own country.
25 Ina tabbatar muku a zamanin Iliya, akwai gwauraye da yawa a Isra’ila, sa’ad da aka rufe sararin sama har shekara uku da rabi, aka kuma yi yunwa mai tsanani ko’ina a ƙasar.
But I tell you in truth, many widows were in Israel in the days of Elijah, when the heaven was shut three years and six months when great famine was throughout all the land:
26 Duk da haka, ba a aiki Iliya ga ko ɗaya a cikinsu ba. Sai dai zuwa ga wata gwauruwa da take a Zarefat, a yankin Sidon.
But to none of them was Elijah sent, save to Sarepta, [a city] of Sidon, to a woman [that was] a widow.
27 Akwai kuma mutane da yawa a Isra’ila masu kuturta a zamanin annabi Elisha, amma ba ko ɗayansu da aka tsarkake sai Na’aman mutumin Suriyan nan kaɗai.”
And many lepers were in Israel in the time of Elisha the prophet; and none of them was cleansed, saving Naaman the Syrian.
28 Dukan mutanen da suke cikin majami’a suka fusata ƙwarai da jin wannan.
And all they in the synagogue, when they heard these things, were filled with wrath,
29 Suka tashi, suka fitar da Yesu bayan gari, suka kai shi goshin tudun da aka gina garin, don su ture shi ƙasa,
And rose up, and thrust him out of the city, and led him to the brow of the hill on which their city was built, that they might cast him down headlong.
30 amma sai ya bi ta tsakiyar taron ya yi tafiyarsa.
But he passing through the midst of them, went away,
31 Sai ya tafi Kafarnahum, wani gari a Galili, a ranar Asabbaci kuma, ya fara koya wa mutane.
And came down to Capernaum, a city of Galilee, and taught them on the sabbath-days.
32 Suka yi ta mamakin koyarwarsa, domin saƙonsa yana da iko.
And they were astonished at his doctrine: for his word was with power.
33 A cikin majami’ar, akwai wani mutum mai aljani, wani mugun ruhu. Mutumin ya ɗaga murya da ƙarfi ya ce,
And in the synagogue there was a man who had a spirit of an unclean demon; and he cried out with a loud voice,
34 “Wayyo! Ina ruwanka da mu, Yesu Banazare? Ka zo ne don ka hallaka mu? Na san wane ne kai, Mai Tsarki na Allah!”
Saying, Let [us] alone; what have we to do with thee, Jesus of Nazareth? art thou come to destroy us? I know thee who thou art, the Holy One of God.
35 Yesu ya tsawata masa da ƙarfin cewa, “Yi shiru! Ka fita daga cikinsa!” Sai aljanin ya fyaɗa mutumin da ƙasa a gabansu duka, sa’an nan ya fita, ya bar shi ba wani rauni.
And Jesus rebuked him, saying, Hold thy peace, and come out of him. And when the demon had thrown him in the midst, he came out of him, and hurt him not.
36 Dukan mutanen suka yi mamaki, suka ce wa junansu, “Wace irin koyarwa ce haka? Da ƙarfi da iko, yana ba wa mugayen ruhohin umarni suna kuma fita!”
And they were all amazed, and spoke among themselves, saying, What a word [is] this! for with authority and power he commandeth the unclean spirits, and they come out.
37 Labarinsa kuwa ya bazu ko’ina a cikin ƙasar.
And the fame of him went out into every place of the surrounding country.
38 Yesu ya fita daga majami’ar, ya tafi gidan Siman. Surukar Siman kuwa tana fama da zazzaɓi mai tsanani, sai suka roƙi Yesu yă taimake ta.
And he arose out of the synagogue, and entered into Simon's house. And the mother of Simon's wife was taken with a violent fever; and they besought him for her.
39 Sai ya sunkuya kusa da ita, ya kuma tsawata wa zazzaɓin, sai zazzaɓin ya sāke ta. Nan take ta tashi, ta yi musu hidima.
And he stood over her, and rebuked the fever; and it left her: and immediately she arose and ministered to them.
40 Rana tana fāɗuwa, sai mutane suka yi ta kawo wa Yesu dukan waɗanda suke da cuta iri-iri, sai ya ɗibiya wa kowannensu hannuwansa, ya warkar da su.
Now when the sun was setting, all they that had any sick with divers diseases, brought them to him: and he laid his hands on every one of them, and healed them.
41 Bugu da ƙari, aljanu suka fiffita daga cikin mutane da yawa suna ihu suna cewa, “Kai Ɗan Allah ne!” Amma ya kwaɓe su, ya hana su magana, don sun san cewa shi ne Kiristi.
And demons also came out of many, crying out, and saying, Thou art Christ the Son of God. And he rebuking [them], suffered them not to speak: for they knew that he was Christ.
42 Da gari yana wayewa, sai Yesu ya je inda ba kowa. Mutane suka yi ta nemansa, da suka zo inda yake, sai suka yi ƙoƙari su hana shi barinsu.
And when it was day, he departed, and went into a desert place; and the people sought him, and came to him, and stayed him, that he should not depart from them.
43 Amma ya ce, “Dole in yi wa’azin bisharar mulkin Allah ga sauran garuruwa, saboda wannan ne aka aiko ni.”
And he said to them, I must preach the kingdom of God to other cities also, for therefore am I sent.
44 Sai ya dinga yin wa’azi a majami’un Yahudiya.
And he preached in the synagogues of Galilee.

< Luka 4 >