< Luka 24 >

1 Da sassafe a ranar farko ta mako, matan suka je kabarin, da kayan ƙanshin da suka shirya.
Mais le premier jour de la semaine, elles vinrent de grand matin au sépulcre, apportant les parfums qu'elles avaient préparés; et quelques personnes les accompagnaient.
2 Suka iske an riga an gungurar da dutsen daga bakin kabarin.
Et elles trouvèrent que la pierre qui était à l'entrée du sépulcre avait été ôtée.
3 Amma da suka shiga ciki, ba su iske jikin Ubangiji Yesu ba.
Et étant entrées, elles ne trouvèrent point le corps du Seigneur Jésus.
4 Yayinda suna cikin tunani a kan wannan, nan take, ga waɗansu mutum biyu tsaye kusa da su, sanye da kaya masu ƙyalli, kamar walƙiya.
Et comme elles ne savaient qu'en penser, voici, deux hommes se présentèrent à elles, en vêtements étincelants.
5 A cikin tsoro, matan suka fāɗi da fuskokinsu a ƙasa, amma mutanen suka ce musu, “Me ya sa kuke neman mai rai a cikin matattu?
Et comme elles étaient effrayées, et qu'elles baissaient le visage contre terre, ils leur dirent: Pourquoi cherchez-vous parmi les morts celui qui est vivant?
6 Ba ya nan, ya tashi! Ku tuna yadda ya gaya muku tun yana tare da ku a Galili cewa,
Il n'est point ici, mais il est ressuscité. Souvenez-vous de quelle manière il vous a parlé, lorsqu'il était encore en Galilée,
7 ‘Dole a ba da Ɗan Mutum ga hannun masu zunubi, a kuma gicciye shi, a rana ta uku kuma a tashe shi.’”
Disant: Il faut que le Fils de l'homme soit livré entre les mains des méchants, et qu'il soit crucifié, et qu'il ressuscite le troisième jour.
8 Sai suka tuna da maganarsa.
Et elles se souvinrent de ses paroles.
9 Da suka dawo daga kabarin, sai suka faɗa wa Sha Ɗayan nan da sauransu, dukan waɗannan abubuwa.
Et étant revenues du sépulcre, elles racontèrent toutes ces choses aux onze, et à tous les autres.
10 Matan da suka gaya wa manzannin waɗannan abubuwa su ne, Maryamu Magdalin, da Yowanna, da Maryamu uwar Yaƙub, da waɗansu da suke tare da su.
C'était Marie de Magdala, Jeanne, et Marie, mère de Jacques, et les autres qui étaient avec elles, qui dirent ces choses aux apôtres.
11 Amma ba su gaskata matan ba, domin sun ɗauki kalmominsu wani zancen banza ne.
Mais ce qu'elles leur disaient leur parut une rêverie, et ils ne les crurent point.
12 Duk da haka, Bitrus ya tashi a guje zuwa kabarin. Da ya sunkuya, sai ya ga ƙyallayen lilin kaɗai a kwance. Sai ya koma yana tunani a ransa, a kan abin da ya faru.
Toutefois, Pierre se leva et courut au sépulcre, et s'étant baissé, il ne vit que les bandelettes qui étaient à terre; puis il s'en alla, étonné en lui-même de ce qui était arrivé.
13 A wannan rana kuma, biyu daga cikinsu suna tafiya zuwa wani ƙauye, da ake kira Emmawus, da suke kusan mil bakwai daga Urushalima.
Ce jour-là même, deux d'entre eux s'en allaient à un bourg, nommé Emmaüs, qui était éloigné de Jérusalem de soixante stades.
14 Suna magana da juna a kan dukan abubuwan da suka faru.
Et ils s'entretenaient ensemble de tout ce qui était arrivé.
15 Da suna magana, kuma suna tattauna waɗannan abubuwa da junansu, sai Yesu da kansa ya zo yana tafiya tare da su.
Et comme ils s'entretenaient, et qu'ils discutaient, Jésus lui-même, s'étant approché, se mit à marcher avec eux.
16 Amma ba a ba su ikon gane shi ba.
Mais leurs yeux étaient retenus, de sorte qu'ils ne le reconnurent point.
17 Sai ya tambaye, su ya ce, “Mene ne kuke tattaunawa da juna a cikin tafiyarku?” Suka tsaya shiru, da damuwa a fuskarsu.
Et il leur dit: Quels sont ces discours que vous tenez ensemble, chemin faisant, et pourquoi avez-vous le visage triste?
18 Ɗaya daga cikinsu, mai suna Kiliyobas, ya tambaye shi ya ce, “Ashe, kai baƙo ne a Urushalima, da ba ka san abubuwan da suka faru a can, a cikin kwanakin nan ba?”
L'un d'eux, nommé Cléopas, lui répondit: Es-tu le seul étranger à Jérusalem, qui ne sache point les choses qui s'y sont passées ces jours-ci?
19 Sai ya yi tambaya, “Waɗanne abubuwa?” Suka amsa suka ce, “Game da Yesu Banazare. Shi annabi ne, mai iko ne kuma cikin ayyukansa da maganarsa, a gaban Allah da kuma dukan mutane.
Et il leur dit: Et quoi? Ils lui répondirent: Ce qui est arrivé à Jésus de Nazareth, qui était un prophète, puissant en ouvres et en paroles, devant Dieu et devant tout le peuple;
20 Manyan firistoci da masu mulkinmu sun ba da shi a yi masa hukuncin mutuwa, suka kuwa gicciye shi.
Et comment les principaux sacrificateurs et nos magistrats l'ont livré pour être condamné à mort, et l'ont crucifié.
21 Amma da, muna sa zuciya cewa, shi ne wanda zai fanshi Isra’ila. Bugu da ƙari kuma yau kwana uku ke nan tun da wannan abin ya faru.
Pour nous, nous espérions que ce serait lui qui délivrerait Israël, et cependant, voici déjà le troisième jour que ces choses sont arrivées.
22 Har wa yau, waɗansu daga cikin matanmu sun ba mu mamaki. Sun je kabarin da sassafen nan,
Il est vrai que quelques femmes, des nôtres, nous ont fort étonnés; car ayant été de grand matin au sépulcre,
23 amma ba su sami jikinsa ba. Sun dawo sun faɗa mana cewa, sun ga wahayi na mala’iku, da suka ce yana da rai.
Et n'y ayant pas trouvé son corps, elles sont venues en disant que des anges leur ont apparu et leur ont dit qu'il est vivant.
24 Sa’an nan, waɗansu abokanmu suka je kabarin, suka kuma tarar da kome kamar yadda matan suka faɗa, amma shi, ba su gan shi ba.”
Et quelques-uns des nôtres sont allés au sépulcre, et ont trouvé les choses comme les femmes l'avaient dit; mais lui, ils ne l'ont point vu.
25 Sai ya ce musu, “Ashe, ku marasa azanci ne, masu nauyin zuciyar gaskata, da dukan abin da annabawa suka faɗa!
Alors il leur dit: O gens sans intelligence et d'un cœur tardif à croire tout ce que les prophètes ont dit!
26 Ai, dole Kiristi yă sha waɗannan wahalolin, kafin yă shiga ɗaukakarsa.
Ne fallait-il pas que le Christ souffrît ces choses, et qu'il entrât dans sa gloire?
27 Sai ya fara bayyana musu daga Musa da dukan Annabawa, abin da dukan Nassi ya faɗa a kansa.”
Puis, commençant par Moïse et par tous les prophètes, il leur expliquait, dans toutes les Écritures, ce qui le regardait.
28 Da suka yi kusa da ƙauyen da za su, sai Yesu ya yi kamar zai ci gaba.
Ainsi ils approchèrent du bourg où ils allaient, mais Jésus faisait comme s'il voulait aller plus loin.
29 Amma suka matsa masa suka ce, “Sauka wurinmu, don dare ya kusa, rana ta kusa fāɗuwa.” Sai ya sauka wurinsu.
Et ils le contraignirent à s'arrêter, en lui disant: Demeure avec nous; car le soir commence à venir, et le jour est sur son déclin. Il entra donc pour demeurer avec eux.
30 Da ya zauna a tebur tare da su, sai ya ɗauki burodi, ya yi godiya, ya kakkarya ya fara ba su.
Et comme il était à table avec eux, il prit du pain et rendit grâces; puis l'ayant rompu, il le leur donna.
31 Sa’an nan idanunsu suka buɗe, suka gane shi. Sai ya ɓace musu.
Alors leurs yeux s'ouvrirent, et ils le reconnurent; mais il disparut de devant eux.
32 Suka tambayi juna, “Ashe, shi ya sa zukatanmu suka kuna a cikinmu, sa’ad da yake magana da mu a hanya, yana bayyana mana Nassi.”
Et ils se dirent l'un à l'autre: Notre cœur ne brûlait-il pas au-dedans de nous, lorsqu'il nous parlait en chemin, et qu'il nous expliquait les Écritures?
33 Suka tashi nan da nan suka koma Urushalima. A can suka sami Sha Ɗayan nan da waɗanda suke tare da su a wuri ɗaya,
Et se levant à l'heure même, ils retournèrent à Jérusalem; et ils trouvèrent les onze, et ceux qui étaient avec eux, assemblés,
34 suna cewa, “Gaskiya ne! Ubangiji ya tashi, ya kuma bayyana ga Siman”
Qui disaient: Le Seigneur est vraiment ressuscité, et il est apparu à Simon.
35 Sai su biyun nan suka ba da labarin abin da ya faru a hanya, da kuma yadda suka gane Yesu yayinda ya kakkarya burodin.
A leur tour, ils racontèrent ce qui leur était arrivé en chemin, et comment ils l'avaient reconnu lorsqu'il avait rompu le pain.
36 Suna cikin wannan zance, sai ga Yesu da kansa tsaye a tsakiyarsu. Sai ya ce musu, “Salama a gare ku!”
Comme ils tenaient ces discours, Jésus lui-même se présenta au milieu d'eux, et leur dit: La paix soit avec vous.
37 Suka firgita, suka tsorota, suna tsammani fatalwa ce suka gani.
Mais eux, frappés de stupeur et d'épouvante, croyaient voir un esprit.
38 Sai ya ce musu, “Don me kuke damuwa, kuke kuma shakka a zuciyarku?
Et il leur dit: Pourquoi êtes-vous troublés, et pourquoi s'élève-t-il des pensées contraires dans vos cœurs?
39 Ku duba hannuwana da ƙafafuna. Ai, ni ne da kaina! Ku taɓa ni ku ji, ai, fatalwa ba ta da nama da ƙashi, yadda kuke gani nake da su.”
Voyez mes mains et mes pieds, car c'est moi-même. Touchez-moi et regardez-moi; car un esprit n'a ni chair ni os, comme vous voyez que j'ai.
40 Da ya faɗi haka, sai ya nuna musu hannuwansa da ƙafafunsa.
En disant cela, il leur montra ses mains et ses pieds.
41 Kuma har yanzu, suna cikin rashin gaskatawa, saboda murna da mamaki, sai ya tambaye su, “Kuna da abinci a nan?”
Mais comme, dans leur joie, ils ne le croyaient point encore, et qu'ils étaient étonnés, il leur dit: Avez-vous ici quelque chose à manger?
42 Suka ba shi ɗan gasasshen kifi,
Et ils lui présentèrent un morceau de poisson rôti et du miel en rayon.
43 ya karɓa ya ci a gabansu.
Et l'ayant pris il en mangea en leur présence.
44 Ya ce musu, “Wannan shi ne abin da na gaya muku tun ina tare da ku cewa, dole a cika kome da aka rubuta game da ni, a cikin Dokar Musa, da Annabawa, da kuma Zabura.”
Puis il leur dit: C'est là ce que je vous disais lorsque j'étais encore avec vous, qu'il fallait que tout ce qui a été écrit de moi dans la loi de Moïse et dans les prophètes et dans les psaumes, fût accompli.
45 Sai ya wayar da tunaninsu don su fahimci Nassi.
Alors il leur ouvrit l'esprit, pour qu'ils comprissent les Écritures.
46 Ya ce musu, “Wannan shi ne abin da aka rubuta, cewa dole Kiristi yă sha wahala, a rana ta uku kuma yă tashi daga matattu.
Et il leur dit: Ainsi est-il écrit, et ainsi fallait-il que le Christ souffrît, et qu'il ressuscitât des morts le troisième jour,
47 Kuma a cikin sunansa za a yi wa’azin tuba da gafarar zunubai, ga dukan ƙasashe. Za a kuwa fara daga Urushalima.
Et qu'on prêchât en son nom la repentance et la rémission des péchés, parmi toutes les nations, en commençant par Jérusalem.
48 Ku ne shaidun waɗannan abubuwa.
Or, vous êtes les témoins de ces choses; et voici, je vais vous envoyer ce que mon Père a promis.
49 Zan aika muku da abin da Ubana ya yi alkawari. Amma ku dakata a birnin tukuna, sai an rufe ku da iko daga sama.”
Pour vous, demeurez dans la ville de Jérusalem, jusqu'à ce que vous soyez revêtus de la vertu d'en haut.
50 Bayan ya kai su waje kusa da Betani, sai ya ɗaga hannuwansa ya sa musu albarka.
Il les mena ensuite dehors jusqu'à Béthanie; puis, élevant ses mains, il les bénit.
51 Yana cikin sa musu albarka, sai ya rabu da su. Aka ɗauke shi zuwa cikin sama.
Et il arriva, comme il les bénissait, qu'il se sépara d'eux, et fut élevé au ciel.
52 Sai suka yi masa sujada, suka koma Urushalima cike da murna sosai.
Et eux, l'ayant adoré, s'en retournèrent à Jérusalem dans une grande joie.
53 Sai suka ci gaba da zama a cikin haikalin, suna yabon Allah.
Et ils étaient continuellement dans le temple, louant et bénissant Dieu. Amen.

< Luka 24 >