< Luka 23 >

1 Sai dukan majalisa suka tashi, suka kai shi gaban Bilatus.
Puis toute l'assemblée s'étant levée, le mena à Pilate.
2 Suka fara zarginsa suna cewa, “Mun sami wannan mutum yana rikitar da al’ummarmu. Yana hana a biya haraji ga Kaisar. Yana kuma cewa, shi Kiristi ne, sarki kuma.”
Et ils se mirent à l'accuser, en disant: Nous avons trouvé cet homme séduisant la nation et défendant de donner le tribut à César, et se disant le Christ, le roi.
3 Sai Bilatus ya tambayi Yesu ya ce, “Kai ne sarkin Yahudawa?” Yesu ya amsa ya ce, “I, haka yake, kamar yadda ka faɗa.”
Alors Pilate l'interrogea et lui dit: Es-tu le roi des Juifs? Et Jésus lui répondit: Tu le dis.
4 Sai Bilatus ya sanar wa manyan firistoci da taron ya ce, “Ni fa, ban sami wani ainihin abin zargi game wannan mutum nan ba.”
Et Pilate dit aux principaux sacrificateurs et au peuple: Je ne trouve aucun crime en cet homme.
5 Amma suka nace, suna cewa, “Yana tā da hankulan mutane, ko’ina a Yahudiya da koyarwarsa. Ya fara daga Galili, ga shi har ya kai nan.”
Mais ils insistaient, en disant: Il soulève le peuple, enseignant par toute la Judée, ayant commencé depuis la Galilée, jusqu'ici.
6 Da Bilatus ya ji haka, sai ya yi tambaya, “Ko shi mutumin Galili ne?”
Quand Pilate entendit parler de la Galilée, il demanda si cet homme était Galiléen.
7 Da ya ji cewa, Yesu yana ƙarƙashin mulkin Hiridus ne, sai ya aika da shi zuwa wurin Hiridus, don a lokacin Hiridus yana Urushalima.
Et ayant appris qu'il était de la juridiction d'Hérode, il le renvoya à Hérode, qui était aussi à Jérusalem en ces jours-là.
8 Da Hiridus ya ga Yesu, sai ya yi murna ƙwarai, don tun dā ma yana marmari ya gan shi a kan abin da ya ji game da shi. Ya yi fata ya ga Yesu, yă kuma yi waɗansu ayyukan banmamaki.
Quand Hérode vit Jésus, il en eut une grande joie; car il y avait longtemps qu'il souhaitait de le voir, parce qu'il avait entendu dire beaucoup de choses de lui; et il espérait qu'il lui verrait faire quelque miracle.
9 Ya yi masa tambayoyi masu yawa, amma Yesu bai ba shi ko amsa ba.
Il lui fit donc plusieurs questions; mais Jésus ne lui répondit rien.
10 Manyan firistoci da malaman dokoki suna tsaye a wurin, suna kawo zargi masu ƙarfi a kansa.
Et les principaux sacrificateurs et les scribes étaient là qui l'accusaient avec véhémence.
11 Sai Hiridus da sojojinsa suka wulaƙanta shi, suka yi masa ba’a. Sa’an nan, suka sa masa babban riga, suka mai da shi wurin Bilatus.
Mais Hérode, avec les gens de sa garde, le traita avec mépris; et pour se moquer de lui, il le fit vêtir d'un habit éclatant, et le renvoya à Pilate.
12 A ranar, Hiridus da Bilatus suka zama abokan juna, don tun dā ma, su abokan gāba ne.
En ce même jour, Pilate et Hérode devinrent amis; car auparavant ils étaient ennemis.
13 Bilatus ya tara manyan firistoci, da masu mulki, da mutane,
Or, Pilate ayant assemblé les principaux sacrificateurs, et les magistrats, et le peuple, leur dit:
14 ya ce musu, “Kun kawo mini wannan mutum, a matsayin wanda yana zuga mutane su yi tawaye. Na bincike shi a gabanku, ban ga a kan me kuka kawo kararsa ba.
Vous m'avez amené cet homme comme soulevant le peuple; et cependant, l'ayant interrogé en votre présence, je ne l'ai trouvé coupable d'aucun des crimes dont vous l'accusez;
15 Haka ma Hiridus, shi ya sa ya dawo da shi nan wurinmu. Kamar yadda ku ma kun gani, ba abin da mutumin nan ya yi, da ya isa mutuwa.
Ni Hérode non plus; car je vous ai renvoyés vers lui, et voici il n'a rien fait qui soit digne de mort.
16 Saboda haka, zan yi masa bulala, in sāke shi.”
L'ayant donc fait châtier, je le relâcherai.
Or, il était obligé de leur relâcher un prisonnier à chaque fête.
18 Suka yi ihu gaba ɗaya suka ce, “A yi gaba da wannan mutum! A sake mana Barabbas!”
De sorte qu'ils s'écrièrent tous ensemble: Fais mourir celui-ci, et nous relâche Barabbas.
19 (Barabbas yana kurkuku saboda laifin tā da hankali a birnin, da kuma don kisankai.)
Or, Barabbas avait été mis en prison pour une sédition qui s'était faite dans la ville, et pour un meurtre.
20 Sai Bilatus ya sāke yin musu magana don yana so ya saki Yesu.
Pilate leur parla de nouveau, ayant envie de délivrer Jésus.
21 Amma sai suka ci gaba da ihu, suna cewa, “A gicciye shi! A gicciye shi!”
Mais ils s'écrièrent: Crucifie, crucifie-le.
22 Ya sāke ce musu, sau na uku, “Don me? Wane laifi wannan mutum ya yi? Ni dai ban same shi da wani dalilin da ya isa a kashe shi ba. Saboda haka, zan sa a hore shi, sa’an nan in sāke shi.”
Et il leur dit pour la troisième fois: Mais quel mal a-t-il fait? je n'ai rien trouvé en lui qui soit digne de mort. Je le châtierai donc et je le relâcherai.
23 Amma suna ihu, suna nacewa, suna cewa, dole a gicciye shi, har ihunsu ya rinjaye shi.
Mais ils insistaient, demandant à grands cris qu'il fût crucifié; et leurs cris et ceux des principaux sacrificateurs redoublaient.
24 Sai Bilatus ya biya bukatarsu da ya ji roƙonsu.
Alors Pilate prononça que ce qu'ils demandaient fût fait.
25 Ya saki mutumin da aka jefa a kurkuku saboda tā da hankali, da kisankai, shi wanda suka roƙa. Sa’an nan ya ba da Yesu ga nufinsu.
Et il leur relâcha celui qui avait été mis en prison pour sédition et pour meurtre, et qu'ils demandaient; et il abandonna Jésus à leur volonté.
26 Sa’ad da suna tafiya da Yesu, sai wani da ake kira Siman, mutumin Sairin, yana zuwa daga ƙauye. Suka kama shi, suka aza masa gicciyen, suka tilasta shi ya ɗauki gicciyen, ya bi Yesu a baya.
Et comme ils l'emmenaient, ils prirent un certain Simon de Cyrène, qui revenait des champs, et le chargèrent de la croix, pour la porter après Jésus.
27 Mutane da yawa sosai suka bi shi, a cikinsu ma da mata waɗanda suka yi makoki da kuka dominsa.
Et une grande multitude de peuple et de femmes le suivaient, qui se frappaient la poitrine et se lamentaient.
28 Yesu ya juya, ya ce musu, “’Yan matan Urushalima, kada ku yi kuka saboda ni, amma ku yi kuka saboda kanku, da kuma saboda’ya’yanku.
Mais Jésus, se tournant vers elles, leur dit: Filles de Jérusalem, ne pleurez point sur moi, mais pleurez sur vous-mêmes et sur vos enfants;
29 Gama lokaci yana zuwa da za ku ce, ‘Masu albarka ne bakararru, wato, mata marasa haihuwa, da mahaihuwar da ba su taɓa haihuwa ba, da kuma mama da ba su taɓa shayar da nono ba!’
Car des jours viendront où l'on dira: Heureuses les stériles, les seins qui n'ont point enfanté, et les mamelles qui n'ont point allaité!
30 Sa’an nan “‘za su ce wa duwatsu, “Ku fāɗi a kanmu!” Za su ce wa tuddai kuma, “Ku rufe mu!”’
Alors ils se mettront à dire aux montagnes: Tombez sur nous, et aux coteaux: Couvrez-nous.
31 Gama in mutane suna yin waɗannan abubuwa a lokacin da itace na ɗanye, me zai faru in ya bushe?”
Car si l'on fait ces choses au bois vert, que fera-t-on au bois sec?
32 Tare da shi akwai mutum biyu masu laifi, da aka tafi da su don a gicciye.
Et on menait aussi deux malfaiteurs, pour les faire mourir avec lui.
33 Da suka isa wurin da ake kira “Ƙoƙon Kai,” nan suka gicciye shi, tare da masu laifin nan, ɗaya a hannun damansa, ɗayan kuma a hagunsa.
Et quand ils furent arrivés au lieu appelé Calvaire (le Crâne), ils le crucifièrent là, et les malfaiteurs, l'un à droite, et l'autre à gauche.
34 Yesu ya ce, “Ya Uba ka yi musu gafara, don ba su san abin da suke yi ba.” Suka rarraba tufafinsa ta wurin jefa ƙuri’a.
Mais Jésus disait: Père, pardonne-leur, car ils ne savent ce qu'ils font. Puis se partageant ses vêtements, ils les tirèrent au sort.
35 Mutanen suka tsaya suna kallo. Har masu mulki ma suka yi masa ba’a, suna cewa, “Ya ceci waɗansu, to, ya ceci kansa in shi ne Kiristi na Allah, Zaɓaɓɓe.”
Le peuple se tenait là et regardait. Et les principaux se moquaient avec le peuple, en disant: Il a sauvé les autres, qu'il se sauve lui-même, s'il est le Christ, l'élu de Dieu.
36 Sojoji su ma, suka zo suka yi masa ba’a. Suka miƙa masa ruwan tsami.
Les soldats aussi, en s'approchant pour lui présenter du vinaigre,
37 Suka ce, “In kai ne sarkin Yahudawa, ka ceci kanka mana.”
Se moquaient de lui, et disaient: Si tu es le roi des Juifs, sauve-toi toi-même.
38 Bisa da shi kuma akwai rubutun da ya ce, Wannan shi ne Sarkin Yahudawa.
Et il y avait cette inscription au-dessus de sa tête, en grec, en latin et en hébreu: CELUI-CI EST LE ROI DES JUIFS.
39 Ɗaya daga cikin masu laifin da aka gicciye a wurin ya zazzage shi ya ce, “Shin, ba kai ne Kiristi ba? To, ka ceci kanka, ka kuma cece mu mana!”
L'un des malfaiteurs qui étaient pendus l'outrageait aussi, en disant: Si tu es le Christ, sauve-toi toi-même, et nous aussi.
40 Amma ɗayan mai laifi ya kwaɓe shi ya ce, “Ba ka da tsoron Allah ne, wai saboda kana ƙarƙashin hukunci ɗaya tare da shi?
Mais l'autre, le reprenant, lui dit: Ne crains-tu donc point Dieu, car tu es condamné au même supplice?
41 Horonmu, daidai aka yi mana, sakamakon abin da muka yi ne. Amma wannan mutum, bai yi wani laifi ba.”
Et pour nous, c'est avec justice, car nous souffrons ce que nos ouvres méritent; mais celui-ci n'a fait aucun mal.
42 Sai ya ce, “Yesu, ka tuna da ni sa’ad da ka shiga mulkinka.”
Et il disait à Jésus: Seigneur, souviens-toi de moi, quand tu seras entré dans ton règne.
43 Yesu ya amsa, ya ce masa, “Gaskiya nake faɗa maka, yau ɗin nan, za ka kasance tare da ni, a mulkina a sama.”
Et Jésus lui dit: Je te le dis en vérité, tu seras aujourd'hui avec moi dans le paradis.
44 Yanzu kuwa wajen sa’a ta shida ne, kuma duhu ya rufe ko’ina a ƙasar, har zuwa sa’a ta tara,
Il était environ la sixième heure, et il se fit des ténèbres sur toute la terre jusqu'à la neuvième heure.
45 domin rana ta daina haskakawa. Labulen da yake cikin haikali kuma ya yage kashi biyu.
Le soleil s'obscurcit, et le voile du temple se déchira par le milieu.
46 Yesu ya yi kira da babbar murya ya ce, “Ya Uba, na danƙa ruhuna a hannunka.” Da ya faɗi haka, sai ya ja numfashi na ƙarshe.
Et Jésus s'écriant d'une voix forte, dit: Mon Père, je remets mon esprit entre tes mains. Et ayant dit cela, il expira.
47 Da jarumin ya ga abin da ya faru, sai ya yabi Allah ya ce, “Gaskiya, wannan mutum mai adalci ne.”
Le centenier, voyant ce qui était arrivé, donna gloire à Dieu, en disant: Certainement cet homme était juste.
48 Da dukan mutanen da suka taru, domin shaidar waɗannan abubuwa, suka ga abin da ya faru, sai suka buga ƙirjinsu suka tafi.
Et tout le peuple qui s'était assemblé à ce spectacle, voyant les choses qui étaient arrivées, s'en retournait en se frappant la poitrine.
49 Amma dukan mutanen da suka san Yesu, tare da mata da suka bi shi daga Galili, suka tsaya daga nesa suna kallon abubuwan nan.
Et tous ceux de sa connaissance, et les femmes qui l'avaient suivi depuis la Galilée, se tenaient loin, regardant ces choses.
50 Akwai wani mutum mai suna Yusuf, ɗan Majalisa, wanda shi nagari ne, mai adalci,
Or un homme, appelé Joseph, qui était conseiller, homme de bien et juste;
51 shi dā ma bai yarda da shawararsu, da kuma abin da suka yi ba. Shi daga Arimateya ne wani garin Yahudiya. Yana kuma jiran zuwa mulkin Allah.
Qui n'avait point consenti à leur dessein, ni à leurs actes; qui était d'Arimathée, ville de Judée, et qui attendait aussi le règne de Dieu,
52 Sai ya je wurin Bilatus ya roƙa a ba shi jikin Yesu.
Étant venu vers Pilate, lui demanda le corps de Jésus.
53 Sai ya saukar da jikin, ya nannaɗe shi a cikin zanen lilin, ya sa shi a wani kabari da aka fafe a cikin dutse, wadda ba a taɓa sa kowa ba.
Et l'ayant descendu de la croix, il l'enveloppa d'un linceul, et le mit dans un sépulcre taillé dans le roc, où personne n'avait encore été mis.
54 An yi haka ne a Ranar Shirye-shirye, ranar Asabbaci kuma yana dab da farawa.
C'était le jour de la préparation, et le sabbat allait commencer.
55 Matan da suka zo tare da Yesu, daga Galili suka bi Yusuf suka ga kabarin, da kuma yadda aka ajiye jikin.
Et les femmes qui étaient venues de Galilée avec Jésus, ayant suivi Joseph, remarquèrent le sépulcre, et comment le corps de Jésus y fut placé.
56 Sa’an nan, suka koma gida, suka shirya kayan ƙanshi da turare. Amma suka huta a ranar Asabbaci don kiyaye doka.
Et s'en étant retournées, elles préparèrent des aromates et des parfums, et elles se reposèrent le jour du sabbat, selon la loi.

< Luka 23 >