< Firistoci 17 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
Yahweh spoke to Moses, saying,
2 “Yi magana da Haruna da’ya’yansa maza da kuma dukan Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji ya umarta.
“Speak to Aaron and to his sons, and to all the people of Israel. Tell them what Yahweh has commanded:
3 Duk mutumin Isra’ilan da ya yanka sa, ɗan rago ko akuya a sansani ko waje da shi
'Any man from Israel who kills an ox, lamb, or goat in the camp, or who kills it outside the camp, in order to sacrifice it—
4 a maimakon kawo shi a matsayin hadaya ga Ubangiji a gaban tabanakul na Ubangiji, za a ɗauki wannan mutum a matsayi mai laifin zub da jini, ya zub da jini, kuma dole a raba shi da mutanensa.
if he does not bring it to the entrance of the tent of meeting to offer it as a sacrifice to Yahweh before his tabernacle, that man is guilty of bloodshed. He has shed blood, and that man must be cut off from among his people.
5 Wannan ya zama haka saboda Isra’ilawa su kawo wa Ubangiji hadayun da suke yi a filaye. Dole su kawo su ga firist, wato, ga Ubangiji, a ƙofar Tentin Sujada, su miƙa su a matsayin hadayun salama.
The purpose of this command is so that the people of Israel will bring their sacrifices to Yahweh at the entrance to the tent of meeting, to the priest to be sacrificed as fellowship offerings to Yahweh, instead of offering sacrifices in an open field.
6 Firist zai yayyafa jinin a bagaden Ubangiji, a ƙofar Tentin Sujada, yă kuma ƙone kitsen kamar ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji.
The priest will sprinkle the blood on Yahweh's altar at the entrance to the tent of meeting; he will burn the fat for it to produce a sweet aroma for Yahweh.
7 Kada kuma su ƙara yin hadayunsu ga gumaka masu siffar bunsurai waɗanda suka bauta wa. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla a gare su wa tsararraki masu zuwa.’
The people must no longer offer their sacrifices to goat idols, for which they act as prostitutes. This will be a permanent statute for them throughout their people's generations.'
8 “Faɗa musu, ‘Duk wani mutumin Isra’ila ko wani baƙon da yake zama a cikinsu wanda ya miƙa hadaya ta ƙonawa ko sadaka
You must say to them, 'Any man of Israel, or any foreigner who lives among them, who offers a burnt offering or sacrifice
9 kuma bai kawo shi a ƙofar Tentin Sujada don yă miƙa shi ga Ubangiji ba, dole a raba wannan mutum da mutanensa.
and does not bring it to the entrance of the tent of meeting in order to sacrifice it to Yahweh, that man must be cut off from his people.
10 “‘Duk mutumin Isra’ila ko baƙon da yake zama a cikinsu wanda ya ci wani jini, zan yi gāba da wannan mutum wanda ya ci jinin, za a kuma raba shi da mutanensa.
If any person of the house of Israel, or any foreigner who lives among them consumes any blood, I will set my face against that person who consumes blood and I will cut him off from among his people.
11 Gama ran halitta yana a cikin jinin, kuma na ba da shi gare ku don kafara a kan bagade, jini ne yake kafara saboda ran mutum.
For the life of an animal is in its blood. I have given its blood to you to make atonement on the altar for your lives, because it is the blood that makes atonement, for it is the blood that atones for the life.
12 Saboda haka na ce wa Isra’ilawa, “Babu waninku da zai ci jini, babu wani baƙon da yake zama a cikinku da zai ci jini.”
Therefore I said to the people of Israel that no one among you must eat blood, neither may any foreigner who lives among you eat blood.
13 “‘Duk wani mutumin Isra’ila ko baƙon da yake zama a cikinku wanda ya ji wa wani dabba ko tsuntsu wanda ake ci ciwo, dole yă tsiyaye jinin yă rufe shi da ƙasa,
Anyone of the people of Israel, or any of the foreigners who live among them, who hunts and kills an animal or bird that may be eaten, that person must pour out its blood and cover the blood with earth.
14 domin ran kowace halitta yana cikin jini. Shi ya sa na ce wa Isra’ilawa, “Kada ku ci jinin wani halitta, domin ran kowace halitta yana cikin jinin; duk wanda ya ci shi dole a fid da shi.”
For the life of each creature is its blood. That is why I said to the people of Israel, “You must not eat the blood of any creature, for the life of every living creature is its blood. Whoever eats it must be cut off.”
15 “‘Kowa, ko haifaffe ɗan ƙasa ko baƙo, da ya ci wani abin da aka sami a mace, ko naman jeji ya yayyage, dole yă wanke rigunansa, yă kuma yi wanka, zai kuma ƙazantu har yamma; sa’an nan zai tsarkake.
Every person who eats an animal that has died or that has been torn by wild animals, whether that person is native born or a foreigner living among you, he must wash his clothes and bathe himself in water, and he will be unclean until the evening. Then he will be clean.
16 Amma in bai wanke rigunansa ya kuma yi wanka ba, alhaki zai kasance a kansa.’”
But if he does not wash his clothes or bathe his body, then he must carry his guilt.'”

< Firistoci 17 >