< Yoshuwa 16 >

1 Rabon da aka ba wa Yusuf ya fara tun daga Urdun kusa da Yeriko, gabas da ruwan Yeriko, sai ya miƙe zuwa jeji, ya haura har zuwa cikin ƙasar tudu na Betel.
La frontera para el reparto a los descendientes de José iba desde el Jordán cerca de Jericó, luego al este de las fuentes de Jericó y a través del desierto desde Jericó hasta la región montañosa de Betel.
2 Ya ci gaba daga Betel (wato, Luz), ya zarce zuwa sashen Arkitawa na Atarot,
Desde Betel (o Luz) continuaba hasta el límite de Atarot el arquita.
3 ya sauka zuwa yammancin bakin iyakar Yalfetiyawa har zuwa yankin Bet-Horon wanda yake cikin kwari. Ya zarce kuma zuwa Gezer, ya gangara ya yi ƙarshe a Bahar Rum.
Luego descendía hacia el oeste hasta el límite de los jafletitas y el límite de la parte baja de Bet-horón, hasta Gezer, y luego hasta el mar.
4 Wannan ne yankin da aka ba wa Manasse da Efraim zuriyar Yusuf gādonsu.
Esta fue la asignación que recibieron los descendientes de José, Efraín y Manasés.
5 Yankin Efraim ke nan bisa ga iyalansu. Iyakar ƙasarsu ta gādo ta kama daga Atarot Addar a gabas zuwa Bet-Horon,
Este fue el territorio asignado a la tribu de Efraín, por familias. El límite de su asignación iba desde Atarot-addar, en el este, hasta la parte alta de Bet-horón
6 ta wuce zuwa Bahar Rum. Daga Mikmetat a arewa kuwa iyakar ta karkata gabas zuwa Ta’anat Shilo, ta wuce zuwa Yanowa a gabas.
y luego hasta el mar. Desde Micmetat, en el norte, el límite giraba hacia el este, pasando por Tanat-Siló, al este de Janoa.
7 Sai ta gangara daga Yanowa zuwa Atarot da Na’ara, ta bi ta Yeriko, ta kuma fito ta Urdun.
Desde Janoa bajaba hasta Atarot y Nará, luego tocaba Jericó y terminaba en el Jordán.
8 Daga Taffuwa kuma iyakar ta bi yamma zuwa kwazazzaban Kana, ta ƙarasa a Bahar Rum. Wannan shi ne gādon mutanen Efraim bisa ga iyalansu.
Desde Tapúaj, el límite corría hacia el oeste hasta el arroyo de Caná y luego salía al mar. Esta era la tierra asignada a la tribu de Efraín, por familias.
9 Gādon ya kuma haɗa da dukan garuruwa da ƙauyuka waɗanda aka keɓe wa mutanen Efraim daga cikin gādon mutanen Manasse.
También se le asignaron a la tribu de Efraín algunas ciudades con sus aldeas que estaban en la tierra asignada a la tribu de Manasés.
10 Ba su kori Kan’aniyawan da suke zama a Gezer ba, don haka Kan’aniyawa suna zama tare da mutanen Efraim har wa yau; amma Kan’aniyawa suka zama masu yin aikin dole.
Sin embargo, no expulsaron a los cananeos que vivían en Gezer, por lo que los cananeos viven en medio de la tribu de Efraín hasta el día de hoy, pero sometidos a trabajos forzados.

< Yoshuwa 16 >