< Yoshuwa 13 >

1 Sa’ad da Yoshuwa ya tsufa, Ubangiji ya ce masa, “Ka tsufa ƙwarai, ga shi kuma akwai sauran ƙasa mai fāɗi da ba ku riga kun mallaka ba.
Or quand Josué fut devenu vieux, fort avancé en âge, l'Eternel lui dit: Tu es devenu vieux, fort avancé en âge, et il reste encore un fort grand pays à posséder.
2 “Ga ƙasar da ta rage, “dukan yankunan Filistiyawa da na Geshurawa.
C'est ici le pays qui demeure de reste, toutes les contrées des Philistins, et tout Guésuri.
3 Daga Kogin Shihor a gabashin Masar zuwa sashen Ekron a arewa, dukan wannan ƙasa ana lissafta ta a cikin ƙasar Kan’aniyawa, ko da yake tana a sashen da sarakuna biyar na Filistiyawa na Gaza, Ashdod, Ashkeloniyawa, Gat da Ekron; na Awwiyawa.
Depuis Sihor, qui est au devant de l'Egypte, même jusqu'aux frontières de Hekron vers le Septentrion; cela est réputé des Cananéens; [savoir] les cinq gouvernements des Philistins, qui sont celui de Gaza, celui d'Asdod, celui d'Askélon, celui de Gath, et celui de Hekron, et les Hauviens.
4 Daga wajen kudu kuma, dukan ƙasar Kan’aniyawa ce. Iyakarta a arewa ta fara daga Ara ta Sidoniyawa har zuwa Afek, ta zarce har zuwa iyakar Amoriyawa;
Du côté du Midi tout le pays des Cananéens, et Méhara qui est aux Sidoniens, jusques vers Aphek, jusqu'aux frontières des Amorrhéens.
5 da ƙasar Gebaliyawa; da dukan Lebanon wajen gabas daga Ba’al-Gad a gindin Dutsen Hermon zuwa Lebo Hamat.
Le pays aussi qui appartient aux Guibliens, et tout le Liban; vers le soleil levant, depuis Bahal-Gad, sous la montagne de Hermon, jusqu'à l'entrée de Hamath.
6 “Dukan mazauna kan yankunan tuddai daga Lebanon zuwa Misrefot Mayim, wato, dukan Sidoniyawa, ni da kaina zan kore su a gaban Isra’ilawa. Ka tabbata ka raba wa Isra’ilawa ƙasar ta zama gādonsu kamar yadda na umarce ka,
Tous les habitants de la montagne depuis le Liban jusqu'aux eaux de Masréphoth; tous les Sidoniens; je les chasserai moi-même de devant les enfants d'Israël; fais seulement qu'on en jette [les lots], afin qu'elle soit à Israël en héritage, comme je te l'ai commandé.
7 ka raba ta tă zama gādo wa kabilu tara da kuma rabin kabilar Manasse.”
Maintenant donc divise ce pays en héritage aux neuf Tribus, et à la moitié de la Tribu de Manassé;
8 Rabin kabilar Manasse, mutanen Ruben da mutanen Gad suka karɓi rabonsu na gādo wanda Musa ya ba su a gabashin Urdun. Abin da Musa bawan Ubangiji ya ba su ke nan.
Avec laquelle les Rubénites et les Gadites ont pris leur héritage; lequel Moïse leur a donné au delà du Jourdain vers l'Orient, selon que Moïse serviteur de l'Eternel le leur a donné;
9 Wannan ya tashi daga Arower a gefen kwarin Arnon, da kuma daga garin da yake tsakiyar kwarin, ya kuma haɗa da ƙasar da take tudun Medeba har zuwa Dibon,
Depuis Haroher, qui est sur le bord du torrent d'Arnon, et la ville qui [est] au milieu du torrent, et tout le plat pays de Médéba, jusqu'à Dibon.
10 da dukan garuruwan Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulkin Heshbon, har zuwa iyakar Ammonawa.
Et toutes les villes de Sihon, Roi des Amorrhéens, qui régnait à Hesbon, jusqu'aux limites des enfants de Hammon;
11 Haɗe da Gileyad, inda mutanen Geshur da Ma’aka suke. Dukan Dutsen Hermon, da dukan Bashan har zuwa Saleka,
Et Galaad, et les limites des Guésuriens et des Mahacathiens, et toute la montagne de Hermon, et tout Basan jusqu'à Salca;
12 wato, dukan masarautar Og a Bashan, wanda ya yi mulkin Ashtarot da Edireyi, yana cikin waɗanda suke na ƙarshe da ba a kashe ba a cikin Refahiyawa. Musa ya ci su da yaƙi, ya ƙwace ƙasarsu.
Tout le Royaume de Hog en Basan, lequel Hog régnait à Hastaroth, et à Edréhi, [et] était demeuré de reste des Réphaïms, lesquels [Rois] Moïse défit, et les déposséda.
13 Amma Isra’ilawa ba su kori mutanen Geshur da Ma’aka ba, saboda haka suka ci gaba da zama cikin Isra’ilawa har wa yau.
(Or les enfants d'Israël ne dépossédèrent point les Guésuriens et les Mahacathiens; mais les Guésuriens et les Mahacathiens ont habité parmi Israël jusqu'à ce jour.)
14 Kabilar Lawiyawa ne kaɗai Musa bai ba ta gādo ba, gama hadayun ƙonawa da ake miƙa wa Ubangiji, Allah na Isra’ila ne gādonsu, kamar yadda ya yi musu alkawari.
Seulement il ne donna point d'héritage à la Tribu de Lévi; les sacrifices de l'Eternel, le Dieu d'Israël, faits par feu étant son héritage, comme il lui [en] avait parlé.
15 Ga abin da Musa ya ba kabilar Ruben bisa ga iyalansu.
Moïse donc donna un héritage à la Tribu des enfants de Ruben selon leurs familles.
16 Abin da ya kama daga Arower a gefen kwarin Arnon, da kuma daga garin da yake tsakiyar kwarin, da dukan ƙasar tudu kusa da Medeba
Et leurs bornes furent depuis Haroher qui est sur le bord du torrent d'Arnon, et la ville qui est au milieu du torrent, et tout le plat pays qui est près de Médéba.
17 zuwa Heshbon, da dukan garuruwan kan tudu, haɗe da Dibon, Bamot Ba’al, Bet-Ba’al-Meyon,
Hesbon et toutes ses villes, qui étaient au plat pays; Dibon, et Bamoth-Bahal, et Beth-Bahal-mehon.
18 Yahza, Kedemot, Mefa’at,
Et Jahatsa, et Kédémoth, et Méphahath.
19 Kiriyatayim, Sibma, Zeret Shahar kan tudu cikin kwari,
Et Kirjathajim, et Sibma, et Tseretsahar en la montagne de la vallée.
20 Bet-Feyor, gangaren Fisga da Bet-Yeshimot,
Et Beth-Péhor, et Asdoth de Pisga, et Beth-jesimoth.
21 dukan garuruwan da suke kan tudu da dukan masarautar Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulki a Heshbon. Musa ya yi nasara da shi, da shugabannin Midiyawa, wato, Ewi, Rekem, Zur, Hur, da Reba, sarakunan Sihon, waɗanda suka zauna a ƙasar.
Et toutes les villes du plat pays, et tout le Royaume de Sihon, Roi des Amorrhéens qui régnait à Hesbon; lequel Moïse défit, avec les principaux de Madian, Evi, Rekem, Tsur, Hur, et Rébah, Princes relevant de Sihon, [et] habitant au pays.
22 Ƙari a kan waɗanda aka kashe a yaƙi, Isra’ilawa suka kashe Bala’am ɗan Beyor da takobi don yana duba.
Les enfants d'Israël firent passer aussi par l'épée Balaam fils de Béhor, le devin, avec les autres qui y furent tués.
23 Gefen Urdun shi ne iyakar mutanen Ruben. Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne gādon mutanen Ruben, bisa ga iyalansu.
Et les bornes des enfants de Ruben furent le Jourdain, et sa borne. Tel fut l'héritage des enfants de Ruben selon leurs familles, [savoir] ces villes-là, et leurs villages.
24 Ga abin da Musa ya ba kabilar Gad, bisa ga iyalansu.
Moïse donna aussi [un héritage] à la Tribu de Gad pour les enfants de Gad, selon leurs familles.
25 Yankin ƙasarsu ya ƙunshi Yazer, da dukan garuruwan Gileyad, da rabin ƙasar Ammonawa har zuwa Arower kusa da Rabba,
Et leur pays fut Jahzer, et toutes les villes de Galaad, et la moitié du pays des enfants de Hammon, jusqu'à Haroher, qui est vis-à-vis de Rabba.
26 da kuma daga Heshbon zuwa Ramat Mizfa da Betonim, da kuma daga Mahanayim zuwa sashen Debir,
Et depuis Hesbon jusqu'à Ramath-mitspé, et Bétonim, et depuis Mahanajim jusqu'aux frontières de Débir.
27 kuma a cikin kwari, Bet-Haram, Bet-Nimra, Sukkot da Zafon da kuma sauran masarautar Sihon sarkin Heshbon (gabashin Urdun, abin da ya kama har zuwa ƙarshen Tekun Kinneret).
Et dans la vallée, Beth-haram, et Beth-nimra, et Succoth, et Tsaphon; le reste du Royaume de Sihon Roi de Hesbon, le Jourdain, et sa borne, jusqu'au bout de la mer de Kinnereth, au delà du Jourdain, vers l'Orient.
28 Waɗannan garuruwan da ƙauyukansu duka, gādon mutanen Gad ne, bisa ga iyalansu.
Tel fut l'héritage des enfants de Gad, selon leurs familles; [savoir] ces villes-là et leurs villages.
29 Ga abin da Musa ya ba rabin kabilar Manasse, wato, wa rabin zuriyar Manasse, bisa ga iyalansu.
Moïse aussi donna à la moitié de la Tribu de Manassé [un héritage], qui est demeuré à la moitié de la Tribu des enfants de Manassé, selon leurs familles.
30 Abin da ya miƙe daga Mahanayim haɗe da dukan Bashan, da gefen masarautar Og sarkin Bashan, da dukan garuruwan Yayir guda sittin da suke a Bashan,
Leur pays fut depuis Mahanajim, tout Basan, [et] tout le Royaume de Hog, Roi de Basan, et tous les bourgs de Jaïr qui sont en Basan, soixante villes.
31 da rabin Gileyad, da Ashtarot, Edireyi (biranen sarki Og a Bashan). Wannan shi ne rabon da zuriyar Makir ɗan Manasse suka samu, domin rabin’ya’yan Makir maza, bisa ga iyalansu.
Et la moitié de Galaad, et Hastaroth, et Edréhi, villes du Royaume de Hog en Basan, furent aux enfants de Makir, fils de Manassé, [savoir] à la moitié des enfants de Makir, selon leurs familles.
32 Waɗannan su ne rabon gādon da Musa ya yi lokacin da suke cikin filayen Mowab a hayin gabashin Urdun kusa da Yeriko.
Ce sont là [les pays] que Moïse [étant] dans les campagnes de Moab avait partagés en héritage, de ce qui était au delà du Jourdain de Jérico, vers l'Orient.
33 Amma Musa bai ba kabilar Lawiyawa gādo ba; Ubangiji, Allah na Isra’ila, shi ne gādonsu kamar yadda ya yi musu alkawari.
Or Moïse ne donna point d'héritage à la Tribu de Lévi; [car] l'Eternel le Dieu d'Israël est leur héritage, comme il leur en a parlé.

< Yoshuwa 13 >