< Mahukunta 1 >

1 Bayan da Yoshuwa ya rasu, Isra’ilawa suka tambayi Ubangiji suka ce, “Wane ne zai fara tafiya don yă yaƙi Kan’aniyawa dominmu?”
Or il arriva qu'après la mort de Josué les enfants d'Israël consultèrent l'Eternel, en disant: Qui de nous montera le premier contre les Cananéens pour leur faire la guerre?
2 Sai Ubangiji ya ce, “Yahuda zai tafi. Na riga na ba da ƙasar a hannunsu.”
Et l'Eternel répondit: Juda montera; voici, j'ai livré le pays entre ses mains.
3 Sa’an nan mutane Yahuda suka ce wa mutanen Simeyon “Ku zo tare da mu a yankin da aka ba mu rabon mu don mu yaƙi Kan’aniyawa. Mu ma mu bi ku wurin naku.” Saboda haka mutanen Simeyon suka tafi tare da su.
Et Juda dit à Siméon son frère: Monte avec moi en mon partage, et nous ferons la guerre aux Cananéens; et j'irai aussi avec toi en ton partage. Ainsi Siméon alla avec lui.
4 Sa’ad da Yahuda ya fāɗa musu, Ubangiji kuwa ya ba da Kan’aniyawa da Ferizziyawa a hannunsu, suka kuwa kashe mutum dubu goma a Bezek.
Juda donc monta, et l'Eternel livra les Cananéens et les Phérésiens entre leurs mains; et ils battirent en Bézec dix mille hommes.
5 A can suka iske Adoni-Bezek, suka yaƙe shi, suka fatattaki Kan’aniyawa da Ferizziyawa.
Or ayant trouvé Adoni-bézec en Bézec, ils combattirent contre lui, et frappèrent les Cananéens et les Phérésiens.
6 Sai Adoni-Bezek ya gudu, amma suka bi shi suka kama shi, suka yayyanka manyan yatsotsinsa na hannu da na ƙafa.
Et Adoni-bézec s'enfuit, mais ils le poursuivirent; et l'ayant pris, ils lui coupèrent les pouces de ses mains et de ses pieds.
7 Sa’an nan Adoni-Bezek ya ce, “Sarakuna saba’in waɗanda aka yayyanka manyan yatsotsinsu na hannu da na ƙafa, sun yi kalan abinci a ƙarƙashin teburina. Ga shi yanzu Allah ya rama abin da na yi musu.” Suka zo da shi Urushalima, a can kuwa ya mutu.
Alors Adoni-bézec dit: Soixante et dix Rois, dont les pouces des mains et des pieds avaient été coupés, ont recueilli [du pain] sous ma table; comme j'ai fait, Dieu m'a ainsi rendu; et ayant été amené à Jérusalem, il y mourut.
8 Mutanen Yahuda suka yaƙi Urushalima ita ma suka ci ta. Suka karkashe mutanen birnin suka cinna mata wuta.
Or les enfants de Juda avaient fait la guerre contre Jérusalem, et l'avaient prise, et ils avaient fait passer [ses habitants] au tranchant de l'épée, et mis la ville en feu.
9 Bayan wannan, mutanen Yahuda suka gangara suka yaƙi Kan’aniyawan da suke zaune a ƙasar tudu, Negeb, da gindin tuddai a yammanci.
Puis les enfants de Juda étaient descendus pour faire la guerre aux Cananéens, qui habitaient dans les montagnes, et au Midi, et dans la plaine.
10 Suka ci gaba suka yaƙi Kan’aniyawan da suke zaune a Hebron (wadda dā ake kira Kiriyat Arba) suka kuma ci Sheshai, Ahiman da Talmai da yaƙi.
Juda donc s'en était allé contre les Cananéens qui habitaient à Hébron; or le nom d'Hébron était auparavant Kirjath-Arbah; et il avait frappé Sesaï, Ahiman et Talmaï.
11 Daga nan kuma suka ci gaba suka yaƙi mutanen da suke zaune a Debir (da ake kira a dā Kiriyat Sefer).
Et de là il était allé contre les habitants de Débir, le nom de laquelle était auparavant Kirjath-sépher.
12 Sai Kaleb ya ce, “Duk wanda ya fāɗa wa Kiriyat Sefer ya kuma ci ta da yaƙi, zan ba shi’yata Aksa yă aura.”
Et Caleb avait dit: Qui frappera Kirjath-sépher et la prendra, je lui donnerai ma fille Hacsa pour femme.
13 Sai Otniyel ɗan Kenaz, ƙanen Kaleb ya ci birnin, saboda haka Kaleb ya ba shi’yarsa Aksa ya aura.
Et Hothniël, fils de Kénas, frère puîné de Caleb, la prit; et [Caleb] lui donna sa fille Hacsa pour femme.
14 Wata rana da ta zo wurin Otniyel, sai ta zuga shi yă roƙi mahaifinta fili. Sa’ad da ta sauko daga jakinta, sai Kaleb ya ce mata, “Me zan yi miki?”
Et il arriva que comme elle s'en allait, elle l'incita à demander à son père un champ; puis elle descendit impétueusement de dessus son âne; et Caleb lui dit: Qu'as-tu?
15 Sai ta ce, “Ka yi mini alheri na musamman. Da yake ka ba ni ƙasa a Negeb, to, sai ka ba ni maɓulɓulan ruwa kuma.” Sai Kaleb ya ba ta maɓulɓulan bisa da kuma na ƙasa.
Et elle lui répondit: Donne-moi un présent; puisque tu m'as donné une terre sèche, donne-moi aussi des sources d'eaux. Et Caleb lui donna les fontaines [du quartier] de dessus, et les fontaines [du quartier] de dessous.
16 Zuriyar surukin Musa, Keniyawa, suka haura daga Birnin dabino tare da mutanen Yahuda don su zauna cikin mutanen Hamadan Yahuda a cikin Negeb kusa da Arad.
Or les enfants du Kénien, beau-père de Moïse, étaient montés de la ville des palmes avec les enfants de Juda, au désert de Juda, qui est au Midi de Harad; parce qu'ils avaient marché et demeuré avec le peuple.
17 Sa’an nan mutanen Yahuda suka tafi tare da’yan’uwansu mutanen Simeyon suka fāɗa wa Kan’aniyawan da suke zaune cikin Zefat, suka kuwa hallaka birnin gaba ɗaya. Saboda haka aka kira wurin Horma.
Puis Juda s'en alla avec Siméon son frère, et ils frappèrent les Cananéens qui habitaient à Tsephath, et la détruisirent à la façon de l'interdit, c'est pourquoi on appela la ville du nom de Horma.
18 Mutanen Yahuda kuma suka ci Gaza, Ashkelon, da Ekron, kowace birni tare da yankinsa.
Juda prit aussi Gaza avec ses confins; Askelon avec ses confins; et Hékron avec ses confins.
19 Ubangiji kuwa yana tare da mutane Yahuda. Suka mallaki ƙasar tudu, amma ba su iya suka kori mutanen daga filaye ba, domin suna da keken yaƙin ƙarfe.
Et l'Eternel fut avec Juda, et ils dépossédèrent [les habitants] de la montagne: mais ils ne dépossédèrent point les habitants de la vallée, parce qu'ils avaient des chariots de fer.
20 Yadda Musa ya yi alkawari, sai aka ba Kaleb Hebron, wanda ya kori daga cikinta’ya’ya maza uku na Anak.
Et on donna, selon que Moïse l'avait dit, Hébron à Caleb; qui en déposséda les trois fils de Hanak.
21 Ko da yake mutanen Benyamin sun kāsa su kori Yebusiyawa, waɗanda suke zaune a Urushalima; har yă zuwa yau, Yebusiyawa suna zaune a can tare da mutanen Benyamin.
Quant aux enfants de Benjamin, ils ne dépossédèrent point le Jébusien qui habitait à Jérusalem; c'est pourquoi le Jébusien a habité avec les enfants de Benjamin à Jérusalem jusqu'à ce jour.
22 To, gidan Yusuf suka auka wa Betel, Ubangiji kuwa yana tare da su.
Ceux aussi de la maison de Joseph montèrent contre Bethel, et l'Eternel fut avec eux.
23 Sa’ad da suka aike mutane don su leƙi asirin Betel (da dā ake kira Luz),
Et ceux de la maison de Joseph firent reconnaître Bethel, dont le nom était auparavant, Luz.
24 ’yan leƙen asirin suka ga wani ya fito daga birnin sai suka ce masa, “Ka nuna mana yadda za mu shiga birnin, mu kuwa za mu yi maka alheri.”
Et les espions virent un homme qui sortait de la ville, auquel ils dirent: Nous te prions de nous montrer un endroit par où l'on puisse entrer dans la ville, et nous te ferons grâce.
25 Saboda haka ya nuna musu, suka kuwa hallaka birnin, suka bar mutumin da dukan iyalinsa da rai.
Il leur montra donc un endroit par où l'on pouvait entrer dans la ville, et ils la firent passer au tranchant de l'épée; mais ils laissèrent aller cet homme-là, et toute sa famille.
26 Sa’an nan ya tafi ƙasar Hittiyawa, inda ya gina birni ya kuma kira shi Luz, haka ake kira birnin har wa yau.
Puis cet homme s'en étant allé au pays des Héthiens, y bâtit une ville, et l'appela Luz, qui est son nom jusqu'à ce jour.
27 Amma Manasse ba su kori mutane Bet-Sheyan ko Ta’anak ko Dor ko Ibileyam ko Megiddo tare da ƙauyukansu ba, gama Kan’aniyawa sun dāge su zauna a wannan ƙasa.
Manassé aussi ne déposséda point [les habitants] de Beth-séan, ni des villes de son ressort, ni [les habitants] de Tahanac, ni des villes de son ressort; ni les habitants de Dor, ni des villes de son ressort; ni les habitants de Jibléham, ni des villes de son ressort, ni les habitants de Meguiddo, ni des villes de son ressort; et les Cananéens osèrent encore habiter en ce pays-là.
28 Sa’ad da Isra’ila ta yi ƙarfi, sai suka tilasta Kan’aniyawa yin aikin gandu amma ba su kore su gaba ɗaya ba.
Il est vrai qu'il arriva que quand Israël fut devenu plus fort, il rendît les Cananéens tributaires; mais il ne les déposséda pas entièrement.
29 Haka Efraim ma bai kori Kan’aniyawa da suke zaune a Gezer ba, amma Kan’aniyawa suka ci gaba da zama tare da su.
Ephraïm aussi ne déposséda point les Cananéens qui habitaient à Guézer; mais les Cananéens habitèrent avec lui à Guézer.
30 Haka kuma Zebulun bai kori Kan’aniyawa da suke zaune a Kitron da Nahalol, waɗanda suka rage a cikinsu ba; sai dai sun sa su aikin gandu.
Zabulon ne déposséda point les habitants de Kitron, ni les habitants de Nahalol; mais les Cananéens habitèrent avec lui, et lui furent tributaires.
31 Haka Asher ma bai kori waɗanda suke zama a Akko ko Sidon ko Ahlab ko Akzib ko Helba ko Afik ko kuma Rehob ba,
Aser ne déposséda point les habitants de Hacco, ni les habitants de Sidon, ni d'Ahlab, ni d'Aczib, ni d'Helba, ni d'Aphik, ni de Rehob.
32 kuma saboda wannan ne mutanen Asher suke zaune cikin mazaunan ƙasar Kan’aniyawa.
Mais ceux d'Aser habitèrent parmi les Cananéens habitants du pays; car ils ne les dépossédèrent point.
33 Haka kuma Naftali bai kori waɗanda suke zaune a Bet-Shemesh ko Bet-Anat; amma mutanen Naftali su ma suna zama a ciki Kan’aniyawa mazaunan ƙasar, waɗanda suke zaune a Bet-Shemesh da Bet-Anat kuwa suka zama masu yi musu aikin gandu.
Nephthali ne déposséda point les habitants de Beth-sémes, ni les habitants de Beth-hanath, mais il habita parmi les Cananéens habitants du pays; et les habitants de Beth-sémes, et de Beth-hanath lui furent tributaires.
34 Amoriyawa suka matsa wa mutanen Dan a ƙasar tudu, ba su yarda musu su gangaro zuwa filaye ba.
Et les Amorrhéens tinrent les enfants de Dan fort resserrés dans la montagne, et ils ne souffraient point qu'ils descendissent dans la vallée.
35 Su Amoriyawa kuma suka dāge su zauna a Dutsen-Heres, Aiyalon, da Sha’albim. Amma yayinda mutanen Yusuf suka ƙara ƙarfi, sai suka su yin musu aikin gandu.
Et ces Amorrhéens-là osèrent encore habiter à Har-Hérés, à Ajalon, et à Sahalbim; mais la main de la maison de Joseph étant devenue plus forte, ils furent rendus tributaires.
36 Iyakar Amoriyawa kuwa daga Mashigin Kunama zuwa Sela da kuma zuwa gaba.
Or la contrée des Amorrhéens [était] depuis la montée de Hakrabbim, depuis la roche, et au-dessus.

< Mahukunta 1 >