< Yoshuwa 11 >

1 Sa’ad da Yabin sarkin Hazor ya ji wannan, sai ya aika saƙo zuwa wurin Yobab sarkin Madon, da sarkin Shimron, da Akshaf,
Quando Jabin, rei de Hazor, soube disso, enviou a Jobab rei de Madon, ao rei de Shimron, ao rei de Achshaph,
2 ya kuma aika zuwa ga sarakunan arewa waɗanda suke kan tuddai da kuma waɗanda suke cikin Araba a kudancin Kinneret da cikin filayen kwari, da cikin Nafot Dor a yamma;
e aos reis que estavam ao norte, no país das colinas, no Arabah ao sul de Chinneroth, na planície, e nas alturas de Dor no oeste,
3 ya kuma aika zuwa ga Kan’aniyawa a gabas da yamma; da kuma zuwa ga Amoriyawa, Hittiyawa da Ferizziyawa, da Yebusiyawa da suke kan tuddai; da kuma Hiwiyawa masu zama a gindin dutsen Hermon a yankin Mizfa.
para o Canaanita no leste e no oeste, o Amorita, o Hittita, o Perizzite, o Jebusita na região montanhosa, e o Hivita sob Hermon na terra de Mizpah.
4 Suka fito da dukan rundunansu da keken yaƙi masu yawan gaske, babbar runduna, yawansu ya yi kamar yashin bakin teku.
Eles saíram, eles e todos os seus exércitos com eles, muitas pessoas, mesmo como a areia que está na costa do mar em multidão, com muitos cavalos e carruagens.
5 Duk sarakunan nan suka haɗa mayaƙansu tare, suka kafa sansani a bakin Ruwayen Meron don su yi yaƙi da Isra’ilawa.
Todos estes reis se reuniram; e vieram e acamparam juntos nas águas de Merom, para lutar com Israel.
6 Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Kada ka ji tsoronsu, domin war haka gobe zan ba da dukansu a hannun Isra’ilawa, za su kuwa karkashe su. Za ku gurgunta dawakansu, ku kuma ƙone keken yaƙinsu.”
Yahweh disse a Josué: “Não tenha medo por causa deles; pois amanhã, a esta hora, eu os entregarei todos mortos antes de Israel. Você vai prender os cavalos deles e queimar suas carruagens com fogo”.
7 Sai Yoshuwa da dukan mayaƙan suka auka musu a bakin Ruwayen Meron.
Então Josué veio de repente, com todos os guerreiros, contra eles pelas águas de Merom, e os atacou.
8 Ubangiji kuwa ya ba Isra’ilawa nasara a kan su, suka ci su da yaƙi, suka fafare su har zuwa Sidon Babba, zuwa Misrefot Mayim, har zuwa Kwarin Mizfa a gabas, ba wanda suka bari da rai.
Yahweh os entregou nas mãos de Israel, e eles os atacaram, e os perseguiram até o grande Sidon, e até Misrephoth Maim, e até o vale de Mizpah para o leste. Eles os atingiram até não deixarem mais ninguém.
9 Yoshuwa ya yi musu yadda Ubangiji ya umarta, ya gurgunta dawakansu, ya kuma ƙone keken yaƙinsu.
Josué fez com eles como Yahweh lhe disse. Ele enforcou seus cavalos e queimou suas carruagens com fogo.
10 A lokacin nan Yoshuwa ya koma da baya ya ci Hazor da yaƙi, ya kuma kashe sarkinta da takobi. (Hazor ce babbar masarautan ƙasashen nan.)
Josué voltou atrás naquela época, pegou Hazor e golpeou seu rei com a espada; pois Hazor costumava ser a cabeça de todos aqueles reinos.
11 Suka karkashe duk mazaunan ƙasar da takobi, ba su bar wani mai numfashi ba, suka kuma ƙona Hazor.
Eles atingiram todas as almas que estavam nele com o fio da espada, destruindo-as completamente. Não restava ninguém que respirava. Ele queimou Hazor com fogo.
12 Yoshuwa ya ƙwace masarautun nan duka ya kuma kashe sarakunansu da takobi, ya hallakar da su ƙaƙaf kamar yadda Musa bawan Ubangiji ya umarta.
Josué capturou todas as cidades daqueles reis, com seus reis, e os atingiu com o fio da espada, e os destruiu totalmente, como ordenou Moisés, servo de Javé.
13 Duk da haka Isra’ilawa ba su ƙone biranen da suke kan tuddai ba, sai Hazor kaɗai Yoshuwa ya ƙone.
Mas quanto às cidades que estavam em seus montes, Israel não queimou nenhuma delas, exceto Hazor apenas. Josué queimou isso.
14 Isra’ilawa suka kwashi ganima da dabbobi na waɗannan birane, amma suka karkashe mutanen duka da takobi, ba su bar wani mai numfashi ba.
Os filhos de Israel tomaram todas as pilhagens destas cidades, com o gado, como pilhagem para si mesmos; mas todos os homens que atingiram com o fio da espada, até que os destruíram. Eles não deixaram ninguém que respirasse.
15 Yadda Ubangiji ya umarci bawansa Musa, haka Musa ya umarci Yoshuwa, shi kuwa ya yi duk abin da Ubangiji ya umarci Musa.
Como Yahweh ordenou a Moisés, seu servo, assim Moisés ordenou a Josué. Josué o fez. Ele não deixou nada por fazer de tudo o que Iavé ordenou a Moisés.
16 Saboda haka Yoshuwa ya cinye ƙasar duka da yaƙi, dukan Negeb, duka yankin Goshen, filayen kwari na yamma, Araba da tuddai na Isra’ila da kwarinta.
Então Josué capturou toda aquela terra, a região montanhosa, todo o Sul, toda a terra de Gósen, a planície, o Arabah, a região montanhosa de Israel, e a planície do mesmo,
17 Daga Dutsen Halak wanda ya miƙe zuwa wajajen Seyir, zuwa Ba’al-Gad a Kwarin Lebanon ƙasa da Dutsen Hermon. Ya kama sarakunansu ya karkashe su.
do Monte Halak, que vai até Seir, até Baal Gad, no vale do Líbano sob o Monte Hermon. Ele pegou todos os seus reis, golpeou-os, e os matou.
18 Yoshuwa ya daɗe yana yaƙi da dukan waɗannan sarakuna.
Josué fez guerra por muito tempo com todos esses reis.
19 Sai Hiwiyawa kaɗai waɗanda suke zama a Gibeyon, sauran ba ko birni ɗaya da ta yi yarjejjeniya ta salama da Isra’ilawa, Isra’ilawa kuwa suka ci dukansu da yaƙi.
Não havia uma cidade que fizesse as pazes com os filhos de Israel, exceto os hivitas, os habitantes de Gibeon. Eles levaram todos em batalha.
20 Gama Ubangiji ne ya taurare zukatansu waɗannan sarakuna suka yi yaƙi da Isra’ilawa don yă hallaka su gaba ɗaya, yă gamar da su ba jinƙai, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
Pois era de Javé para endurecer seus corações, para vir contra Israel em batalha, para que ele pudesse destruí-los totalmente, para que eles não tivessem nenhum favor, mas para que ele os destruísse, como Javé ordenou a Moisés.
21 A lokacin nan Yoshuwa ya je ya hallaka Anakawa daga ƙasar tudu. Daga Hebron, Debir da Anab. Daga dukan ƙasar tuddai na Yahuda, da kuma dukan ƙasar tudu ta Isra’ila, Yoshuwa ya hallaka su duka da garuruwansu.
Josué veio naquela época, e cortou os Anakim da região montanhosa, de Hebron, de Debir, de Anab, e de toda a região montanhosa de Judá, e de toda a região montanhosa de Israel. Josué os destruiu totalmente com suas cidades.
22 Ba a bar waɗansu Anakawa a harabar Isra’ila ba; sai dai a Gaza, Gat da Ashdod ne aka samu waɗanda suka ragu da rai.
Não restava nenhum dos Anakim na terra dos filhos de Israel. Somente em Gaza, em Gate, e em Ashdod, alguns ficaram.
23 Yoshuwa kuwa ya ƙwace dukan ƙasar yadda Ubangiji ya umarci Musa, ya ba da ita ta zama ƙasar gādo ga Isra’ilawa, kabila-kabila. Ta haka ƙasar ta huta daga yaƙi.
Então Josué tomou a terra inteira, de acordo com tudo o que Javé falou a Moisés; e Josué a deu em herança a Israel de acordo com suas divisões por suas tribos. Então a terra teve descanso da guerra.

< Yoshuwa 11 >