< Yowel 3 >

1 “A waɗancan kwanaki da kuma a wancan lokaci, sa’ad da zan maido da arzikin Yahuda da Urushalima,
Car voici, en ces jours-là et en ce temps-là auquel je ferai retourner ceux qui auront été emmenés captifs de Juda et de Jérusalem,
2 zan tattara dukan al’ummai in kuma kawo su Kwarin Yehoshafat Can zan yi musu shari’a game da gādona, mutanena Isra’ila, gama sun warwatsar da mutanena a cikin al’ummai sun kuma raba ƙasata.
J'assemblerai toutes les nations, et les ferai descendre en la vallée de Josaphat, et là j'entrerai en jugement avec eux, à cause de mon peuple, et de mon héritage d'Israël, lequel ils ont dispersé parmi les nations, et parce qu'ils ont partagé entre eux mon pays;
3 Sun jefa ƙuri’a a kan mutanena suna kuma sayar da yara maza don karuwanci, sun sayar da’yan matan domin ruwan inabi wanda za su sha.
Et qu'ils ont jeté le sort sur mon peuple; et qu'ils ont donné un enfant pour une prostituée, et ont vendu la jeune fille pour du vin, qu'ils ont bu.
4 “Yanzu mene ne damuwarku da ni, ya Taya da Sidon da kuma dukan mazaunan yankunan Filistiya? Kuna ƙoƙari ku sāka mini don abin da na yi ne? In kuna sāka mini ne, to, da gaggawa zan mayar muku da sakayya a kanku.
Et qu'ai-je aussi affaire de vous, Tyr et Sidon, et de vous, toutes les limites de la Palestine, me rendrez-vous ma récompense, ou me voulez-vous irriter? Je vous rendrai promptement et sans délai votre récompense sur votre tête.
5 Gama kun kwashe azurfata da zinariyata kun kuma washe dukiyata mafi kyau kun kai cikin haikalinku.
Car vous avez pris mon argent et mon or, et avez emporté dans vos temples mes choses les plus précieuses, et les meilleures.
6 Kun sayar da mutanen Yahuda da na Urushalima ga mutanen Hellenawa, don ku aika da su nesa da ƙasarsu.
Et vous avez vendu les enfants de Juda, et les enfants de Jérusalem aux enfants des Grecs, afin de les éloigner de leur contrée.
7 “Duba, zan dawo da su daga wuraren da kuka sayar da su, in kuma yi muku abin da kuka yi musu.
Voici, je les ferai lever du lieu auquel [ils ont été transportés après que] vous les avez vendus; et je ferai retourner votre récompense sur votre tête.
8 Zan sayar da’ya’yanku maza da mata ga mutanen Yahuda, su kuma za su sayar da su ga mutanen Sabenawa, al’umma da take nesa da ku.” Ubangiji ya faɗa.
Je vendrai donc vos fils et vos filles entre les mains des enfants de Juda, et ils les vendront à ceux de Séba, [qui les transporteront] vers une nation éloignée; car l'Eternel a parlé.
9 Ku yi shelar wannan ga al’ummai. Ku yi shirin yaƙi! Ku tā da jarumawa! Bari mayaƙa su ja kusa su kai hari.
Publiez ceci parmi les nations: Préparez la guerre; réveillez les hommes forts, que tous les gens de guerre s'approchent, et qu'ils montent.
10 Ku bubbuge garemaninku su zama takuba da kuma laujenku su zama māsu. Bari raunana su ce, “Ni mai ƙarfi ne!”
Forgez des épées de vos hoyaux, et des javelines de vos serpes; et que le faible dise: Je suis fort.
11 Ku gaggauta, dukanku al’ummai daga kowane ɓangare, ku tattaru a can. Ka sauko da mayaƙanka, ya Ubangiji!
Amassez-vous, et venez, toutes nations d'alentour, et soyez assemblées; l'Eternel abattra là tes hommes forts.
12 “Bari a tā da dukan al’ummai; bari su kutsa zuwa Kwarin Yehoshafat gama a can zan zauna in shari’anta dukan al’ummai daga kowane ɓangare.
Que les nations se réveillent, et qu'elles montent à la vallée de Josaphat; car je serai assis là pour juger toutes les nations d'alentour.
13 Ku fito da lauje, gama girbi ya nuna. Ku zo, ku tattaka inabin, gama wurin matsewar ruwan inabi ya cika randunan tarawa kuma sun cika har suna zuba, muguntarsu da girma take!”
Mettez la faucille, car la moisson est mûre; venez, et descendez, car le pressoir est plein: les cuves regorgent, car leur malice est grande.
14 Dubun dubbai suna a cikin kwarin yanke shawara! Gama ranar Ubangiji ta yi kusa a cikin kwarin yanke shawara.
Peuples, peuples, à la vallée de décision; car la journée de l'Eternel est proche dans la vallée de décision.
15 Za a duhunta rana da wata, taurari kuma ba za su ba da haske ba.
Le soleil et la lune ont été obscurcis, et les étoiles ont retiré leur lueur.
16 Ubangiji zai yi ruri daga Sihiyona tsawa kuma daga Urushalima; duniya da sararin sama za su yi rawan jiki. Amma Ubangiji zai zama mafakar mutanensa, mafaka ga mutanensa Isra’ila.
Et l'Eternel rugira de Sion, et fera ouïr sa voix de Jérusalem, et les Cieux et la terre seront ébranlés, et l'Eternel [sera] un asile à son peuple, et la force des enfants d'Israël.
17 “Sa’an nan za ku san cewa ni, Ubangiji Allahnku, ina zaune a Sihiyona, dutsena mai tsarki. Urushalima za tă zama mai tsarki; baƙi ba za su ƙara mamaye ta ba.
Et vous saurez que je suis l'Eternel votre Dieu, qui habite en Sion, la montagne de ma sainteté; et Jérusalem ne sera que sainteté, et les étrangers n'y passeront plus.
18 “A wannan rana duwatsu za su ɗiga da sabon ruwan inabi, tuddai kuma za su malmalo madara; dukan rafuffukan Yahuda za su yi ta gudano da ruwa. Maɓulɓula kuma za tă fito daga gidan Ubangiji haka ma ruwa a kwarin itatuwan ƙirya.
Et il arrivera en ce jour-là que les montagnes distilleront le moût, et que les coteaux se fondront en lait, les eaux courront dans tous les ruisseaux de Juda, et il sortira une fontaine de la maison de l'Eternel, et elle arrosera la vallée de Sittim.
19 Amma Masar za tă zama kango, Edom kuma hamada marar amfani, saboda kama-karyar da aka yi wa mutanen Yahuda, a ƙasar da aka zub da jinin marasa laifi.
L'Egypte sera en désolation, et l'Idumée en désert de désolation, à cause de la violence faite aux enfants de Juda, desquels ils ont répandu le sang innocent dans leur pays.
20 Za a zauna a Yahuda har abada Urushalima kuma daga tsara zuwa tsara.
Mais la Judée sera habitée éternellement, et Jérusalem d'âge en âge.
21 Alhakin jininsu, wanda ban gafarta ba, zan gafarta.”
Et je nettoierai leur sang que je n'avais point nettoyé; car l'Eternel habite en Sion.

< Yowel 3 >