< Hosiya 13 >

1 Sa’ad da Efraim ya yi magana, mutane sun yi rawan jiki; an girmama shi a cikin Isra’ila. Amma sai ya zama mai laifi na yin wa Ba’al sujada, ya kuwa mutu.
Si-tôt qu'Ephraïm eut parlé, on trembla; il avait élevé le [Royaume] en Israël, mais il s'est rendu coupable par Bahal, et il est mort.
2 Yanzu sai yin zunubi a kai a kai suke; suna yin gumaka wa kansu daga azurfansu, da wayo suna sarrafa siffofi, dukansu aikin masu aikin hannu ne. Ana magana waɗannan mutane cewa, “Suna miƙa hadayar mutum su kuma sumbaci gumakan maruƙa.”
Et maintenant ils continuent à pécher, et ils se sont fait de leur argent une image de fonte, selon leur intelligence, des idoles qui ne sont qu'ouvrage d'ouvriers, [mais] desquelles [pourtant] ils disent aux hommes qui sacrifient: qu'on baise les veaux.
3 Saboda haka za su zama kamar hazon safiya, kamar raɓar safen da yakan kakkaɓe, kamar ƙaiƙayin da ake tankaɗe daga masussuka, kamar hayaƙin da yake fita daga taga.
C'est pourquoi ils seront comme la nuée du matin, et comme la rosée du matin, laquelle s'en va; comme la balle qui est emportée hors de l'aire par le tourbillon; et comme la fumée sortant de la cheminée.
4 “Amma ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar. Ba za ku yarda da wani Allah ba sai ni, ba wani Mai Ceto in ban da ni.
Et moi je suis l'Eternel ton Dieu dès le pays d Egypte, et tu ne devrais reconnaître d'autre dieu que moi; aussi il n'y a point de Sauveur que moi.
5 Na lura da ku a hamada, cikin ƙasar mai ƙunar zafi.
Je t'ai connu au désert, en une terre aride.
6 Sa’ad da na ciyar da su sun ƙoshi; sa’ad da suka ƙoshi, sai suka fara taƙama; sai suka manta da ni.
Ils ont été rassasiés selon [l'abondance de] leurs pâturages, ils ont été rassasiés, et leur cœur s'est élevé; et ils m'ont oublié.
7 Saboda haka zan hau kansu kamar zaki, zan ɓuya a bakin hanya kamar damisa.
Je leur ai donc été comme un grand lion; et je les ai épiés sur le chemin comme un léopard.
8 Kamar beyar da aka ƙwace mata’ya’yanta, zan fāɗa musu in ɓarke su. Kamar zaki zan cinye su; kamar naman jeji zan yayyage su.
Je les rencontrerai comme une ourse à qui on a ôté ses petits, et je déchirerai la taie de leur cœur, et là je les dévorerai comme un vieux lion; la bête des champs les déchirera.
9 “An hallaka ku, ya Isra’ila, domin kun tayar mini, kun tayar wa mai taimakonku.
On t'a perdu, ô Israël! mais en moi réside ton secours.
10 Ina sarkinku, da zai cece ku? Ina masu mulkinku cikin dukan garuruwanku, waɗanda kuka ce, ‘Ba mu sarki da shugabanni’?
Serai-je ton Roi? Où est-il [ton roi?] et qu'il te délivre en toutes tes villes; où sont tes Gouverneurs, desquels tu as dit: Donne-moi un Roi, et des Seigneurs?
11 Saboda haka cikin fushina na ba ku sarki, kuma cikin hasalata na ɗauke shi.
Je t'ai donné un Roi en ma colère, et je l'ôterai en ma fureur.
12 An yi ajiyar laifin Efraim, aka lissafta zunubansa.
L'iniquité d'Ephraïm est liée, et son péché est serré.
13 Naƙuda ta zo masa kamar a mace mai haihuwa, amma shi yaro ne marar hikima; sa’ad da lokaci ya kai, ba ya zuwa inda mahaifa ta buɗe.
Les douleurs [comme] de celle qui enfante le surprendront; c'est un enfant qui n'est pas sage, car il ne se tient pas à temps à la brèche des enfants.
14 “Zan fanshe su daga ikon kabari; zan cece su daga mutuwa. Ina annobanki, ya mutuwa? Ina hallakarka, ya kabari? “Ba zan ji tausayi ba, (Sheol h7585)
Je les eusse rachetés de la puissance du sépulcre, et les eusse garantis de la mort; j'eusse été tes pestes, ô mort! et ta destruction, ô sépulcre! [mais] la repentance est cachée loin de mes yeux. (Sheol h7585)
15 ko da ma ya ci gaba cikin’yan’uwansa. Iskar gabas daga Ubangiji za tă zo, tana hurawa daga hamada; maɓulɓularsa za tă kafe rijiyarsa kuma ta bushe. Za a kwashi kaya masu daraja na ɗakin ajiyarsa ganima.
Quand il aura fructifié entre ses frères, le vent Oriental, le vent de l'Eternel montant du désert, viendra, et ses sources sécheront, et sa fontaine tarira, et on pillera le trésor de toutes les choses désirables.
16 Dole mutanen Samariya su ɗauki laifinsu, domin sun tayar wa Allahnsu. Za a kashe su da takobi; za a fyaɗa ƙananansu da ƙasa, za a ɓarke matansu masu ciki.”
Samarie sera désolée, car elle s'est rebellée contre son Dieu; ils tomberont par l'épée, leurs petits enfants seront écrasés, et on fendra le ventre de leurs femmes enceintes.

< Hosiya 13 >