< Ayuba 1 >

1 A ƙasar Uz akwai wani mutum mai suna Ayuba. Mutum ne marar laifi kuma mai adalci; yana tsoron Allah, ba ruwansa da mugunta.
Bil je mož v deželi Uc, katerega ime je bilo Job, in ta mož je bil popoln in iskren in nekdo, ki se je bal Boga in se ogibal zla.
2 Yana da’ya’ya maza bakwai da’yan mata uku,
Tam se mu je rodilo sedem sinov in tri hčere.
3 yana da tumaki dubu bakwai, raƙuma dubu uku, shanu ɗari biyar, da jakuna ɗari biyar, yana kuma da masu yi masa aiki da yawa. A ƙasar Gabas ba wani kamar sa.
Njegovo imetje je bilo tudi sedem tisoč ovc, tri tisoč kamel, petsto jarmov volov, petsto oslic in zelo velika družina, tako da je bil ta človek največji izmed vseh mož vzhoda.
4 ’Ya’yansa maza sukan yi biki a gidajensu, wannan yă yi yă ba wancan, sai su kira’yan’uwansu mata ukun su ci, su sha tare.
Njegovi sinovi so šli in praznovali v svojih hišah vsak svoj dan. Poslali so in dali poklicati svoje tri sestre, da jedo in pijejo z njimi.
5 Bayan lokacin bikin ya wuce, sai Ayuba yă aika su zo don yă tsarkake su. Tun da sassafe zai miƙa hadaya ta ƙonawa domin kowannensu, don yana tunani cewa, “Mai yiwuwa’ya’yana sun yi wa Allah zunubi, ko sun la’anta shi a cikin zuciyarsu.” Haka Ayuba ya saba yi.
Bilo je tako, da ko so se dnevi njihovega praznovanja iztekli, je Job poslal, jih posvečeval in vstajal zgodaj zjutraj ter daroval žgalne daritve glede na število njih vseh, kajti Job je rekel: »Morda so moji sinovi grešili in v svojih srcih prekleli Boga.« Tako je Job nenehno delal.
6 Wata rana mala’iku suka kawo kansu gaban Ubangiji, Shaiɗan shi ma ya zo tare da su.
Bil je torej dan, ko so prišli Božji sinovi, da se pokažejo pred Gospodom in tudi Satan je prišel med njimi.
7 Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “Daga ina ka fito?” Shaiɗan ya amsa wa Ubangiji ya ce, “Daga yawo a duniya ina kai da kawowa a cikinta.”
Gospod je rekel Satanu: »Od kod prihajaš?« Nató je Satan odgovoril Gospodu in rekel: »Od potikanja sem ter tja po zemlji in od hoje gor in dol po njej.«
8 Sai Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “Ko ka ga bawana Ayuba? A cikin duniya babu wani kamar sa; shi marar laifi ne, adali kuma, mutum ne mai tsoron Allah, ba ruwansa da mugunta.”
Gospod je rekel Satanu: »Si kaj preudaril [o] mojem služabniku Jobu, ker na zemlji ni nikogar podobnega njemu; popoln in pošten človek je, ki se boji Boga in se ogiblje zla?«
9 Sai Shaiɗan ya amsa ya ce, “Haka kawai Ayuba yake tsoron Allah?
Potem je Satan odgovoril Gospodu in rekel: »Mar se Job zastonj boji Boga?
10 Ba ka kāre shi da iyalinsa gaba ɗaya da duk mallakarsa ba? Ka Albarkaci ayyukan hannunsa yadda dabbobinsa duk sun cika ko’ina.
Mar nisi ti naredil ograje okoli njega, okoli njegove hiše in okoli vsega, kar ima na vsaki strani? Blagoslovil si delo njegovih rok in njegovo imetje se je povečalo v deželi.
11 Ka ɗan miƙa hannunka ka raba shi da duk abin da yake da shi, ba shakka zai la’anta ka kana ji, kana gani.”
Toda iztegni sedaj svojo roko in se dotakni vsega, kar ima in preklinjal te bo v tvoj obraz.«
12 Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “To, shi ke nan, duk abin da yake da shi yana hannunka, amma kada ka taɓa shi, shi kansa.” Sai Shaiɗan ya bar Ubangiji.
Gospod je rekel Satanu: »Glej, vse, kar ima, je v tvoji oblasti, samo nanj ne iztegni svoje roke.« Tako je Satan odšel izpred Gospodove prisotnosti.
13 Wata rana lokacin da’ya’yan Ayuba suke cikin biki a gidan babban ɗansa,
Bil je dan, ko so njegovi sinovi in njegove hčere jedli in pili vino v hiši njihovega najstarejšega brata.
14 sai ɗan aika ya zo wurin Ayuba ya ce masa, “Shanu suna huɗa, jakuna kuma suna kiwo nan kusa,
K Jobu je prišel poslanec in rekel: »Voli so orali in osli so se pasli poleg njih
15 sai Sabenawa suka auka musu suka kwashe su suka tafi, suka karkashe masu yi maka aiki duka, ni kaɗai na tsira na zo in gaya maka!”
in Sabejci so padli nadnje ter jih odvlekli proč. Da, z ostrino meča so umorili služabnike in samo jaz sam sem pobegnil, da ti povem.«
16 Yana cikin magana sai ga wani ɗan aika ya zo ya ce, “Wutar Allah ta sauko daga sama ta ƙona dukan tumaki da masu lura da su, wato, bayinka, ni kaɗai na tsira na zo in gaya maka!”
Medtem ko je še govoril, je prišel še drugi in rekel: »Ogenj od Boga je padel z neba in sežgal ovce in služabnike, jih použil in samo jaz sam sem pobegnil, da ti povem.«
17 Yana cikin magana sai ga wani ɗan aika ya zo ya ce, “Ƙungiyoyin mahara uku na Kaldiyawa sun auka wa raƙumanka sun kwashe su duka, suka kuma karkashe masu yi maka aiki, ni kaɗai ne na tsira na zo in gaya maka!”
Medtem ko je še govoril, je prišel še drugi in rekel: »Kaldejci so postavili tri čete in vpadli na kamele in jih odvedli proč. Da, in z ostrino meča umorili služabnike in samo jaz sam sem pobegnil, da ti povem.«
18 Yana cikin magana, sai ga wani ɗan aika ya zo ya ce, “’Ya’yanka maza da mata suna biki, suna ci suna sha a gidan babban ɗanka,
Medtem ko je še govoril, je prišel še drugi in rekel: »Tvoji sinovi in tvoje hčere so jedli in pili vino v hiši njihovega najstarejšega brata.
19 sai wata iska mai ƙarfi daga hamada ta auka ta rushe gidan, gidan kuwa ya fāɗi a kan’ya’yanka ya kashe su, ni kaɗai na tsira na zo in gaya maka!”
Glej, iz divjine je prihrumel mogočen veter in udaril štiri vogale hiše in ta je padla na mladeniče in ti so mrtvi. Samo jaz sam sem pobegnil, da ti povem.«
20 Da jin haka sai Ayuba ya tashi ya yayyaga tufafin jikinsa, ya aske kansa. Ya fāɗi a ƙasa ya yi sujada
Potem je Job vstal, raztrgal svoje ogrinjalo, obril svojo glavo, padel dol na tla in oboževal
21 ya ce, “Tsirara na fito daga cikin mahaifiyata, tsirara kuma zan koma. Ubangiji ya bayar, Ubangiji kuma ya karɓa; yabo ya tabbata ga Ubangiji.”
ter rekel: »Nag sem prišel iz maternice svoje matere in nag se bom vrnil tja. Gospod je dal in Gospod je vzel. Blagoslovljeno bodi Gospodovo ime.«
22 Cikin wannan duka Ayuba bai yi wa Allah zunubi ta wurin ba shi laifi ba.
V vsem tem Job ni grešil niti ni nespametno obdolžil Boga.

< Ayuba 1 >