< Ayuba 2 >

1 Wata rana kuma mala’iku suka sāke kawo kansu gaban Ubangiji, sai Shaiɗan shi ma ya zo tare da su yă nuna kansa a gabansa.
Ponovno je bil dan, ko so prišli Božji sinovi, da se predstavijo pred Gospodom in tudi Satan je prišel med njimi, da se predstavi pred Gospodom.
2 Sai Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “Daga ina ka fito?” Shaiɗan ya amsa wa Ubangiji ya ce, “Daga yawo a duniya ina kai da kawowa a cikinta.”
Gospod je rekel Satanu: »Od kod prihajaš?« Satan je Gospodu odgovoril in rekel: »Od potikanja sem ter tja po zemlji in od hoje gor in dol po njej.«
3 Sai Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “Ko ka ga bawana Ayuba? A cikin duniya babu wani kamar sa; shi marar laifi ne, adali kuma, mutum ne mai tsoron Allah ba ruwansa da mugunta. Kuma har yanzu bai fasa zama mai aminci ba duk da wahalar da ka sa na bari ka ba shi ba tare da wani dalili ba.”
Gospod je rekel Satanu: »Si preudaril [o] mojem služabniku Jobu, da tam ni nikogar podobnega njemu na zemlji? Popoln in iskren človek je, nekdo, ki se boji Boga in se ogiblje zla. Še vedno se trdno drži svoje neokrnjenosti, čeprav me spodbujaš zoper njega, da bi ga uničil brez razloga.«
4 Shaiɗan ya amsa ya ce, “Fata don fata! Mutum zai iya rabuwa da duk abin da yake da shi domin ransa.
Satan je Gospodu odgovoril in rekel: »Kožo za kožo, da, vse, kar človek ima, bo dal za svoje življenje.
5 Ka ɗan taɓa lafiyar jikinsa ka gani ba shakka zai la’anta ka kana ji kana gani.”
Toda iztegni sedaj svojo roko in se dotakni njegove kosti in njegovega mesa in preklel te bo v tvoj obraz.«
6 Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “To, shi ke nan, duk abin da yake da shi yana hannunka, amma kada ka taɓa shi, shi kansa.”
Gospod je rekel Satanu: »Glej, on je v tvoji roki, toda ohrani njegovo življenje.«
7 Sai Shaiɗan ya bar Ubangiji, ya je ya sa wa Ayuba ƙuraje masu zafi a jikinsa daga tafin ƙafafunsa har zuwa kansa.
Tako je Satan odšel izpred Gospodove prisotnosti in Joba udaril s hudimi tvori od podplata njegovega stopala do njegovega temena.
8 Sai Ayuba ya ɗauki kaskon tukunya yana ta sosa ƙurajen da shi, yayinda yake zaune cikin toka.
Ta si je vzel črepinjo, se strgal z njo in se usedel med pepel.
9 Matarsa ta ce masa, “Har yanzu kana nan da amincinka? Ka la’anta Allah ka mutu!”
Potem mu je njegova žena rekla: »Mar še vedno ohranjaš svojo neokrnjenost? Prekolni Boga in umri.«
10 Ya amsa ya ce, “Kina magana kamar wawiya. Alheri kaɗai za mu dinga samu daga Allah ban da wahala?” A cikin wannan duka Ayuba bai yi zunubi ba cikin maganarsa.
Toda rekel ji je: »Govoriš kot govori ena izmed nespametnih žensk. Kaj? Dobro smo sprejeli iz Božje roke, pa ne bi sprejeli hudega?« V vsem tem Job s svojimi ustnicami ni grešil.
11 Lokacin da abokan Ayuba su uku wato, Elifaz mutumin Teman, Bildad mutumin Shuwa, da Zofar mutumin Na’ama suka ji wahalar da ta auka wa Ayuba, sai suka shirya suka bar gidajensu suka je don su ta’azantar da shi.
Torej ko so Jobovi trije prijatelji slišali o vsem tem zlu, ki je prišlo nadenj, so prišli, vsak iz svojega lastnega kraja: Elifáz Temánec, Bildád Suhéjec in Cofár Naámčan, kajti skupaj so se dogovorili, da pridejo in da žalujejo z njim in da ga tolažijo.
12 Sa’ad da suka gan shi daga nesa, da ƙyar suka gane shi; sai suka fara kuka da ƙarfi, suka yayyaga tufafinsu suka zuba toka a kawunansu,
Ko pa so od daleč povzdignili svoje oči in ga niso spoznali, so povzdignili svoj glas ter zajokali. Vsak izmed njih je pretrgal svoje ogrinjalo in proti nebu so potresli prah na svoje glave.
13 sai suka zauna da shi a ƙasa har kwana bakwai. Ba wanda ya ce masa kome, don sun ga tsananin wahalar da yake ciki.
Tako so sedeli z njim na tleh sedem dni in sedem noči in nihče mu ni spregovoril niti besede, kajti videli so, da je bila njegova žalost zelo velika.

< Ayuba 2 >