< Ayuba 9 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Konsa, Job te reponn. Li te di:
2 “Lalle, na san wannan gaskiya ne. Amma ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah?
“Anverite, mwen konnen sa se vrè; alò, kijan yon nonm kapab genyen dwa devan Bondye?
3 Ko da mutum yana so yă yi gardama da shi, ba zai taɓa amsa masa ba ko da sau ɗaya cikin dubu.
Si yon moun te vle diskite avèk Li, li pa t ap kab byen reponn li menm yon fwa nan mil.
4 Hikimarsa tana da zurfi, ikonsa yana da yawa. Wane ne ya taɓa yin faɗa da shi har ya yi nasara?
Bondye saj nan kè e pwisan nan fòs; se kilès ki konn reziste ak Li san donmaj?
5 Yana matsar da manyan duwatsu kafin su sani kuma yana juya su cikin fushinsa.
Se Li Menm ki deplase mòn yo, ki jan yo pa menm konnen, lè Li boulvèse yo nan fachez Li.
6 Yana girgiza ƙasa, yana girgiza harsashenta.
Li souke latè sòti nan plas li, e fè pilye fondasyon li yo tranble.
7 Yana magana da rana sai ta ƙi yin haske; yana hana taurari yin haske.
Li kòmande solèy la pou l pa klere e ki mete yon so sou zetwal yo.
8 Shi kaɗai ya shimfiɗa sammai ya kuma yi tafiya a kan raƙuman ruwan teku.
Se Li menm sèl ki rale lonje syèl yo e bese vag lanmè yo.
9 Shi ne ya halicci Mafarauci da Kare da Zomo, da Kaza, da’Ya’yanta da tarin taurari a sama, da taurarin kudu.
Li sèl ki fè sou syèl la gwo Ourse la ak Orion an, avèk Pleiades yo, avèk chanm ki nan sid yo.
10 Yana yin abubuwan banmamaki waɗanda ba a iya ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a iya ƙirgawa.
Li menm ki fè gwo bagay mèvèy yo, avèk zèv mèvèy san kontwòl yo.
11 Ba na iya ganinsa lokacin da ya wuce ni; ba na sani ya wuce lokacin da ya wuce.
Si Li ta vin pase bò kote mwen, mwen pa t ap wè L. Si Li ta depase m nan wout, mwen pa t ap apèsi L.
12 Wane ne ya isa yă hana shi in ya ƙwace abu? Wa zai ce masa, ‘Me kake yi?’
Gade byen, Li rache retire, se kilès ki ka anpeche L? Kilès ki ka di L: ‘Kisa w ap fè la a’?
13 Allah ba ya danne fushinsa; ko dodannin ruwan da ake kira ayarin Rahab ya tattake su.
“Bondye p ap detounen kòlè Li. Anba Li, byen akwoupi, se asistan a Rahab yo.
14 “Ta yaya zan iya yin faɗa da shi? Ina zan iya samun kalmomin da zan yi gardama da shi?
Kijan mwen kab reponn Li, e chwazi pwòp pawòl mwen yo devan L?
15 Ko da yake ba ni da laifi, ba zan iya amsa masa ba; sai dai roƙon jinƙai zan iya yi ga mahukuncina.
Paske malgre mwen te gen rezon, mwen pa t kab reponn. Mwen ta oblije mande gras a Jij mwen an.
16 Ko da na yi kira gare shi ya amsa mini, ban yarda cewa zai saurare ni ba.
Menmsi mwen te rele, e Li te reponn mwen, mwen pa t ap kab kwè ke Li ta koute vwa m.
17 Zai sa hadari yă danne ni yă ƙara mini ciwona ba dalili.
Paske Li fin brize m nèt ak yon tanpèt, e ogmante blese mwen yo san koz.
18 Ba zai bari in yi numfashi ba, sai dai yă ƙara mini azaba.
Li pa lèse m pran souf, men fè m debòde ak sa ki anmè.
19 In maganar ƙarfi ne, shi babban mai ƙarfi ne! In kuma maganar shari’a ne, wa zai kai kararsa?
Men pou pouvwa, men gade, se Li menm ki gen fòs! Epi pou jistis, se kilès menm k ap voye pwosè vèbal bay Li menm?
20 Ko da ni marar ƙarfi ne, bakina ya isa yă sa in zama mai laifi; in ba ni da laifi, zai sa in yi laifi.
Malgre mwen dwat, bouch mwen ap kondane m; malgre mwen san tò, Li va deklare m koupab.
21 “Ko da yake ba ni da laifi, ban damu da kaina ba; na rena raina.
Mwen inosan; mwen pa okipe mwen menm; mwen rayi lavi m.
22 Ba bambanci; shi ya sa na ce, ‘Yana hallaka marasa laifi da kuma mugaye.’
“Tout se menm bagay. Akoz sa mwen di Li detwi inosan yo avèk koupab yo.’
23 Lokacin da bala’i ya kawo ga mutuwa, yakan yi dariyar baƙin cikin marasa laifi.
Si frèt la vin touye sibitman, l ap moke dezolasyon inosan an.
24 Lokacin da ƙasa ta faɗa a hannun mugaye, yakan rufe idanun masu shari’a. In ba shi ba wa zai yi wannan?
Ak lemonn nan ki sede nan men a mechan yo, Li fin kouvri figi a jij latè yo. Si se pa Li menm, eh byen se kilès?
25 “Kwanakina sun fi mai gudu wucewa da sauri; suna firiya babu wani abin jin daɗi a cikinsu.
“Alò, jou m yo vin pi rapid pase yon nonm k ap fè kous; Yo kouri ale. Yo pa wè anyen ki bon.
26 Suna wucewa kamar jirgin ruwan da aka yi da kyauro, kamar jahurma da ta kai wa namanta cafka.
Yo glise pase tankou kannòt k ap pase nan wozo, tankou yon èg ki vole plonje sou viktim li.
27 ‘In na ce zan manta da abin da yake damu na, zan yi murmushi in daina nuna ɓacin rai,’
Malgre mwen di ke m va bliye plent mwen, ke m va kite figi tris la pou fè kè kontan,
28 duk da haka ina tsoron duk wahalata, domin na san ba za ka ɗauke ni marar laifi ba.
mwen krent tout doulè mwen yo. Mwen konnen ke Ou p ap bliye fot mwen yo.
29 Tun da an riga an ɗauke ni mai laifi, duk ƙoƙarina a banza yake.
Mwen gen tan fin jije koupab. Konsa, poukisa mwen ta dwe fè fòs anven?
30 Ko da na wanke jikina duka da sabulu, na wanke hannuwana kuma da soda,
Si m ta lave m nèt ak lanèj, e pwòpte men m ak savon lesiv ki fò,
31 duk da haka za ka jefa ni cikin ƙazamin wuri, yadda ko rigunan jikina ma za su ƙi ni.
malgre sa, Ou ta plonje mwen nan kanal la, e pwòp rad mwen yo ta vin rayi m.
32 “Shi ba mutum ba ne kamar ni wanda zan iya amsa masa, har da za mu yi faɗa da juna a wurin shari’a.
Paske Li pa yon nonm kon mwen, pou m ta reponn Li, pou nou ta kab rive nan tribinal ansanm.
33 In da akwai wanda zai iya shiga tsakaninmu, ya ɗora hannunsa a kanmu tare,
Nanpwen moun ki pou fè antant antre nou, ki ta kab mete men l sou nou toulède.
34 wani wanda zai sa Allah yă daina duka na, don yă daina ba ni tsoro.
Kite Li retire baton Li sou mwen, e pa kite laperèz Li plen m ak gwo latèrè.
35 Sa’an nan ne zan iya yin magana ba tare da jin tsoronsa ba, amma a yadda nake a yanzu ba zan iya ba.
Konsa, mwen ta pale san fè laperèz devan L; men mwen pa kab konsa pou kont mwen.”

< Ayuba 9 >