< Ayuba 8 >

1 Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
Then Bildad the Shuhite answered and said,
2 “Har yaushe za ka gama faɗa waɗannan abubuwa? Maganganunka ba su da amfani.
“How long will you say these things? How long will the words of your mouth be a mighty wind?
3 Allah ba mai shari’ar gaskiya ba ne? Ko Maɗaukaki yakan yi abin da ba daidai ba?
Does God pervert justice? Does the Almighty pervert righteousness?
4 Lokacin da’ya’yansa suka yi masa zunubi, yakan bar su su sha wahalar da zunubi yake kawowa.
Your children have sinned against him; we know this, for he gave them into the hand of their sins.
5 Amma in za ka dubi Allah ka roƙi Maɗaukaki,
But suppose you diligently sought God and presented your request to the Almighty.
6 in kai mai tsarki ne, kuma mai adalci, ko yanzu ma zai taimake ka, yă mayar maka iyalinka da farin cikinka.
If you are pure and upright, then he would surely stir himself on your behalf and restore you to your rightful place.
7 Ko da yake za ka fara da kaɗan, duk da haka za ka gama da samu mai yawa.
Even though your beginning was small, still your final condition would be much greater.
8 “Tambayi na gaba da kai ka ji abin da iyayenka suka koya
Please ask the former generations, and give your attention to what our ancestors learned.
9 gama jiya kaɗai aka haife mu ba mu san kome ba, kuma kwanakinmu a duniya masu wucewa ne.
(We were only born yesterday and know nothing because our days on earth are a shadow).
10 Ba za su bishe ka su kuma gaya maka abin da za ka yi ba? Ba za su yi magana daga cikin hikimar da suke da ita ba?
Will they not teach you and tell you? Will they not speak words from their hearts?
11 Ko kyauro zai iya yi girma a wurin da ba ruwa? Ko za tă taɓa iya yin girma ba tare da ruwa ba?
Can papyrus grow without a marsh? Can reeds grow without water?
12 Yayinda take girma ba a yanka ta, takan mutu da sauri fiye da ciyawa.
While they are still green and not cut down, they wither before any other plant.
13 Abin da yake faruwa ke nan da duk wanda yake mantawa da Allah; waɗanda ba su da Allah, ba su da bege.
So also are the paths of all who forget God; the hope of the godless will perish.
14 Abin da yake dogara a kai ba shi da ƙarfi; abin da yake dogara a kai yanar gizo ce.
His confidence will break apart, and his trust is as weak as a spider's web.
15 Ya jingina ga yanar gizo, amma ba ta tare shi, sun kama ta, amma ba za tă taimake su tsayawa ba.
He leans on his house, but it will not support him; he takes hold of it, but it does not stand.
16 Yana kama da shukar da aka ba ta ruwa sosai lokacin da akwai rana sosai, tana yaɗuwa da kyau;
Under the sun he is green, and his shoots go out over his entire garden.
17 shukar tana bin yaɗuwa, jijiyoyinta suna nannaɗe duwatsu, suna neman wurin da za su kama sosai a cikin duwatsu.
His roots are wrapped about the heaps of stone; they look for good places among the rocks.
18 Amma lokacin da aka tuge shukar daga wurin da take, wurin ba zai san da ita kuma ba, wurin zai ce, ‘Ban taɓa ganin ki ba.’
But if this person is destroyed out of his place, then that place will deny him and say, 'I never saw you.'
19 Ba shakka shukar ta mutu ke nan, kuma waɗansu za su tsiro a wurin.
See, this is the “joy” of such a person's behavior; other plants will sprout out of the same soil in his place.
20 “Ba shakka, Allah ba ya ƙin marar laifi, ko kuma yă ƙarfafa masu aikata mugunta.
See, God will not cast away an innocent man; neither will he take the hand of evildoers.
21 Sai dai yă cika bakinka da dariya, yă sa ka yi sowa ta murna.
He will yet fill your mouth with laughter, your lips with shouting.
22 Maƙiyanka za su sha kunya, za a kawar da tentin mugaye.”
Those who hate you will be clothed with shame; the tent of the wicked will be no more.”

< Ayuba 8 >