< Ayuba 9 >
Then Job answered and said,
2 “Lalle, na san wannan gaskiya ne. Amma ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah?
“I truly know that this is so. But how can a person be in the right with God?
3 Ko da mutum yana so yă yi gardama da shi, ba zai taɓa amsa masa ba ko da sau ɗaya cikin dubu.
If he wants to argue with God, he cannot answer him once in a thousand times.
4 Hikimarsa tana da zurfi, ikonsa yana da yawa. Wane ne ya taɓa yin faɗa da shi har ya yi nasara?
God is wise in heart and mighty in strength; who has ever hardened himself against him and succeeded?—
5 Yana matsar da manyan duwatsu kafin su sani kuma yana juya su cikin fushinsa.
he who removes the mountains without warning anyone when he overturns them in his anger—
6 Yana girgiza ƙasa, yana girgiza harsashenta.
he who shakes the earth out of its place and sets its supports trembling.
7 Yana magana da rana sai ta ƙi yin haske; yana hana taurari yin haske.
It is the same God who tells the sun not to rise, and it does not, and who covers up the stars,
8 Shi kaɗai ya shimfiɗa sammai ya kuma yi tafiya a kan raƙuman ruwan teku.
who by himself stretches out the heavens and tramples down the waves of the sea,
9 Shi ne ya halicci Mafarauci da Kare da Zomo, da Kaza, da’Ya’yanta da tarin taurari a sama, da taurarin kudu.
who makes the Bear, Orion, the Pleiades, and the constellations of the south.
10 Yana yin abubuwan banmamaki waɗanda ba a iya ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a iya ƙirgawa.
He does great and unsearchable things, and wonderful things that cannot be counted.
11 Ba na iya ganinsa lokacin da ya wuce ni; ba na sani ya wuce lokacin da ya wuce.
See, he goes by me, and I do not see him; he passes on also, but I do not perceive him.
12 Wane ne ya isa yă hana shi in ya ƙwace abu? Wa zai ce masa, ‘Me kake yi?’
If he takes something away, who can stop him? Who can say to him, 'What are you doing?'
13 Allah ba ya danne fushinsa; ko dodannin ruwan da ake kira ayarin Rahab ya tattake su.
God will not withdraw his anger; the helpers of Rahab bow beneath him.
14 “Ta yaya zan iya yin faɗa da shi? Ina zan iya samun kalmomin da zan yi gardama da shi?
How much less could I answer him, could I choose words to reason with him?
15 Ko da yake ba ni da laifi, ba zan iya amsa masa ba; sai dai roƙon jinƙai zan iya yi ga mahukuncina.
Even if I were righteous, I could not answer him; I could only plead for mercy with my judge.
16 Ko da na yi kira gare shi ya amsa mini, ban yarda cewa zai saurare ni ba.
Even if I called and he answered me, I would not believe that he was listening to my voice.
17 Zai sa hadari yă danne ni yă ƙara mini ciwona ba dalili.
For he breaks me with a tempest and multiplies my wounds without cause.
18 Ba zai bari in yi numfashi ba, sai dai yă ƙara mini azaba.
He does not allow me to regain my breath; but he fills me with bitterness.
19 In maganar ƙarfi ne, shi babban mai ƙarfi ne! In kuma maganar shari’a ne, wa zai kai kararsa?
If it is a matter of strength, behold, he is mighty! If it is a matter of justice, who can summon him?
20 Ko da ni marar ƙarfi ne, bakina ya isa yă sa in zama mai laifi; in ba ni da laifi, zai sa in yi laifi.
Though I am in the right, my own mouth would condemn me; and though I am blameless, my words would prove me to be guilty.
21 “Ko da yake ba ni da laifi, ban damu da kaina ba; na rena raina.
I am blameless, but I do not care any more about myself; I despise my own life.
22 Ba bambanci; shi ya sa na ce, ‘Yana hallaka marasa laifi da kuma mugaye.’
It makes no difference, which is why I say that he destroys blameless people and wicked people together.
23 Lokacin da bala’i ya kawo ga mutuwa, yakan yi dariyar baƙin cikin marasa laifi.
When a whip suddenly kills, he mocks the despair of the innocent.
24 Lokacin da ƙasa ta faɗa a hannun mugaye, yakan rufe idanun masu shari’a. In ba shi ba wa zai yi wannan?
The earth is given into the hand of wicked people; God covers the faces of its judges. If it is not he who does it, then who is it?
25 “Kwanakina sun fi mai gudu wucewa da sauri; suna firiya babu wani abin jin daɗi a cikinsu.
My days are swifter than a running messenger; my days flee away; they see no good anywhere.
26 Suna wucewa kamar jirgin ruwan da aka yi da kyauro, kamar jahurma da ta kai wa namanta cafka.
They are as fast as papyrus reed boats, and as fast as the eagle that swoops down on its victim.
27 ‘In na ce zan manta da abin da yake damu na, zan yi murmushi in daina nuna ɓacin rai,’
If I said that I would forget about my complaints, that I would take off my sad face and be happy,
28 duk da haka ina tsoron duk wahalata, domin na san ba za ka ɗauke ni marar laifi ba.
I would be afraid of all my sorrows because I know that you will not consider me innocent.
29 Tun da an riga an ɗauke ni mai laifi, duk ƙoƙarina a banza yake.
I will be condemned; why, then, should I try in vain?
30 Ko da na wanke jikina duka da sabulu, na wanke hannuwana kuma da soda,
If I washed myself with snow water and made my hands ever so clean,
31 duk da haka za ka jefa ni cikin ƙazamin wuri, yadda ko rigunan jikina ma za su ƙi ni.
God would plunge me in a ditch, and my own clothes would be disgusted with me.
32 “Shi ba mutum ba ne kamar ni wanda zan iya amsa masa, har da za mu yi faɗa da juna a wurin shari’a.
For God is not a man, as I am, that I could answer him, that we could come together in court.
33 In da akwai wanda zai iya shiga tsakaninmu, ya ɗora hannunsa a kanmu tare,
There is no judge between us who might lay his hand upon us both.
34 wani wanda zai sa Allah yă daina duka na, don yă daina ba ni tsoro.
There is no other judge who could take God's rod off me, who could keep his terror from frightening me.
35 Sa’an nan ne zan iya yin magana ba tare da jin tsoronsa ba, amma a yadda nake a yanzu ba zan iya ba.
Then would I speak up and not fear him. But as things are now, I cannot do that.