< Ayuba 42 >

1 Sa’an nan Ayuba ya amsa wa Ubangiji,
Then Job replied to Yahweh. [He said],
2 “Na san cewa za ka iya yin dukan abubuwa; ba wanda zai iya ɓata shirinka.
“I know that you can do everything and that no one can stop you from doing what you want to do.
3 Ka yi tambaya, ‘Wane ne wannan da ya ƙi karɓar shawarata shi marar ilimi?’ Ba shakka na yi magana game da abubuwan da ban gane ba, abubuwan ban al’ajabi da sun fi ƙarfin ganewata.
[You asked me], ‘(Who are you, who by speaking ignorantly, question what I plan to do?/You have no right to question what I plan to do by speaking ignorantly.)’ [RHQ] It is true that I spoke about things that I did not understand, things that are very wonderful/marvelous, and therefore I am not able to know them.
4 “Ka ce, ‘Saurara yanzu, zan kuma yi magana zan tambaye ka, kuma za ka amsa mini.’
You said to me, ‘Listen while I talk to you. I want to ask you some questions, so prepare yourself to answer them.’
5 Kunnuwana sun ji game da kai amma yanzu na gan ka.
I had heard about you previously, but now [it is as though] I have seen you with my own eyes.
6 Saboda haka na rena kaina na kuma tuba cikin ƙura da toka.”
Therefore I (am ashamed of/withdraw) what I said, and I sit in dust and ashes to show that I am sorry [for what I said].”
7 Bayan Ubangiji ya gaya wa Ayuba waɗannan abubuwa, ya ce wa Elifaz mutumin Teman, “Ina fushi da kai da abokanka guda biyu domin ba ku faɗi abin da yake daidai game da ni ba, kamar yadda bawana Ayuba ya yi.
After Yahweh said these things to Job, he said to Eliphaz, “I am angry with you and your two friends, [Bildad and Zophar], because what my servant Job said about me was right/true, but what you have spoken about me was not right/true.
8 Saboda haka yanzu sai ku ɗauki bijimai guda bakwai, da raguna bakwai, ku je wurin bawana Ayuba ku miƙa hadaya ta ƙonawa domin kanku. Bawana Ayuba zai yi muku addu’a zan kuwa karɓi addu’arsa in bi da ku nisa da wawancinku. Ba ku faɗi abin da yake daidai game da ni ba yadda bawana Ayuba ya yi ba.”
So now you must take to Job seven young bulls and seven rams and [kill them and] burn them on the altar as a sacrifice for yourselves. Then Job will pray for you, and I will do what he requests me to do, [and I will forgive you for speaking wrongly about me]. I will not punish you, even though you deserve to be punished, because what you said about me was not right/true, but what Job said about me was right/true.”
9 Saboda haka Elifaz mutumin Teman, Bildad mutumin Shuwa da Zofar mutumin Na’ama, suka yi abin da Ubangiji ya gaya masu; Ubangiji kuma ya karɓi addu’ar Ayuba.
So Eliphaz, Bildad, and Zophar did what Yahweh commanded them to do, and Yahweh did what Job requested him to do [for the three of them].
10 Bayan Ayuba ya yi wa abokansa addu’a, Ubangiji ya sa shi ya sāke zama mai arziki ya ninka abin da yake da shi a dā sau biyu.
After Job prayed for his three friends, Yahweh [healed him and] caused him to become rich again. Yahweh gave him twice as many things as he had before.
11 Dukan’yan’uwansa maza da mata da duk waɗanda suka san shi a dā suka zo suka ci abinci tare da shi a cikin gidansa. Suka ta’azantar da shi suka ƙarfafa shi game da duk wahalar da Ubangiji ya auka masa, kowannensu kuma ya ba shi azurfa da zobe na zinariya.
Then all his brothers and sisters, and all the people who had known him before, came to his house, and they ate a meal together. They consoled/comforted [DOU] him because of all the troubles that Yahweh had allowed him to experience.
12 Ubangiji ya albarkaci ƙarshen Ayuba fiye da farkonsa. Yana da tumaki guda dubu goma sha huɗu, raƙuma guda dubu shida; shanun noma guda dubu da jakuna guda dubu.
Then Yahweh blessed Job in the second half of his life more than he had blessed him in the first half of his life. He now acquired/owned 14,000 sheep, 6,000 camels, 2,000 oxen, and 1,000 female donkeys.
13 Ya kuma haifi’ya’ya maza bakwai, mata uku.
And he also had seven [more] sons and three [more] daughters.
14 ’Yar farko ya kira ta Yemima, ta biyun Keziya ta ukun Keren-Haffuk.
He named the first daughter Jemimah, he named the second daughter Keziah, and he named the third daughter Keren-Happuch.
15 Duk a cikin ƙasar ba a samu kyawawan mata kamar’ya’yan Ayuba ba, kuma babansu ya ba su gādo tare ta’yan’uwansu maza.
In all of [Uz] land there were no young women who were as beautiful as the daughters of Job, and Job declared that they would inherit some of his possessions, just like their brothers would inherit some.
16 Bayan wannan Ayuba ya rayu shekara ɗari da arba’in; ya ga’ya’yansa da’ya’yansu har tsara ta huɗu.
After that, Job lived 140 more years. Before he died, he (saw/enjoyed being with) his great-great-grandchildren.
17 Sa’an nan Ayuba ya rasu da kyakkyawan tsufa.
He was very old [DOU] when he died.

< Ayuba 42 >