< Ayuba 40 >

1 Ubangiji ya ce wa Ayuba,
INkosi yasiphendula uJobe yathi:
2 “Mai neman sa wa wani laifi zai iya ja da Maɗaukaki? Bari mai tuhumar Allah yă amsa masa.”
Ophikisana loSomandla uzamqondisa yini? Osola uNkulunkulu kakuphendule.
3 Sai Ayuba ya amsa wa Ubangiji,
UJobe waseyiphendula iNkosi wathi:
4 “Ai, ni ba a bakin kome nake ba ne, ta yaya zan iya amsa maka? Na rufe bakina da hannuna.
Khangela, ngiphansi; ngingakuphendula ngithini? Ngibeka isandla sami emlonyeni wami.
5 Na yi magana sau ɗaya amma ba ni da amsa, sau biyu, amma ba zan ƙara cewa kome ba.”
Ngikhulumile kanye, kodwa kangiyikuphendula; kumbe kabili, kodwa kangiyikuqhubeka.
6 Sa’an nan Ubangiji ya yi wa Ayuba magana ta cikin guguwa,
INkosi yasimphendula uJobe isesivunguzaneni yathi:
7 “Ka tashi tsaye ka tsaya da ƙarfi kamar namiji; zan yi maka tambaya kuma za ka amsa mini.
Bopha khathesi ukhalo lwakho njengendoda; ngizakubuza, ubusungazisa.
8 “Ko za ka ƙi yarda da shari’ata? Za ka ba ni laifi don ka nuna kai marar laifi ne?
Isibili, uzachitha isahlulelo sami yini? Ungilahle, ukuze ube ngolungileyo yini?
9 Ko hannunka irin na Allah ne, kuma ko muryarka za tă iya tsawa kamar ta Allah?
Njalo ulengalo yini njengoNkulunkulu? Kumbe ungaduma yini ngelizwi njengaye?
10 Sai ka yi wa kanka ado da ɗaukaka da girma, ka yafa daraja da muƙami.
Khathesi zicecise ngobukhosi lokuphakama, uzembese ngodumo lenkazimulo.
11 Ka saki fushinka, ka dubi dukan wani mai girman kai ka wulaƙanta shi.
Usabalalise intukuthelo zolaka lwakho, ukhangele wonke ozigqajayo, umthobise.
12 Ka dubi duk wani mai girman kai ka ƙasƙantar da shi, ka tattake mugaye a inda ka tsaya.
Khangela wonke ozigqajayo, umehlisele phansi, unyathelele phansi ababi endaweni yabo.
13 Ka bizne su duka tare ka rufe fuskokinsu a cikin kabari.
Ubafihle bonke ethulini, ubophe ubuso babo ngasese.
14 Sa’an nan ni kaina zan shaida maka cewa hannun damanka zai iya cetonka.
Khona lami ngizavuma kuwe, ukuthi isandla sakho sokunene singakusindisa.
15 “Dubi dorina, wadda na halicce ku tare kuma ciyawa take ci kamar sa.
Ake ukhangele imvubu engayenza kanye lawe; idla utshani njengenkabi.
16 Ga shi ƙarfinta yana a ƙugunta ikonta yana cikin tsokar cikinta.
Ake ukhangele, amandla ayo asekhalweni lwayo, lokuqina kwayo kusemisipheni yesisu sayo.
17 Wutsiyarta tana da ƙarfi kamar itacen al’ul; jijiyoyin cinyoyinta suna haɗe a wuri ɗaya.
Iyagobisa umsila wayo njengomsedari; imisipha yemilenze yayo yelukene.
18 Ƙasusuwanta bututun tagulla ne, haƙarƙarinta kamar sandunan ƙarfe.
Amathambo ayo anjengempompi zethusi, amathambo ayo anjengemigoqo yensimbi.
19 Tana ta farko cikin ayyukan Allah, Mahaliccinta kaɗai yake iya tunkarar ta da takobi.
Ingeyokuqala yezindlela zikaNkulunkulu; owayenzayo wasondeza inkemba yayo.
20 Tuddai su suke tanada mata abinci a inda duk namun jeji suke wasa.
Ngoba intaba ziyayivezela ukudla, lapho okudlala khona inyamazana zonke zeganga.
21 Tana kwanciya a ƙarƙashin inuwar itacen lotus ta ɓuya cikin kyauro da fadama.
Ilala phansi kwesihlahla esiluhlaza, ekusithekeni kwemihlanga lamaxhaphozi.
22 Inuwa ta rufe ta da ƙaddaji, itatuwan wardi na rafi, sun kewaye ta.
Izihlahla eziluhlaza ziyayisibekela ngomthunzi wazo; imidubu yesifula iyayiphahla.
23 Sa’ad da kogi ya cika yana hauka, ba tă damu ba; ba abin da zai same ta ko da a gaban bakinta Urdun yake wucewa.
Khangela, umfula uyayicindezela, kayiphangisi; ilesibindi lanxa iJordani ingaphuphumela emlonyeni wayo.
24 Ko akwai wanda zai iya kama ta ba ta kallo, ko kuma a kama ta da tarko a huda hancinta?
Ongayibamba yini ngamehlo ayo? Ongahlaba yini amakhala ayo ngemijibila?

< Ayuba 40 >