< Ayuba 40 >
1 Ubangiji ya ce wa Ayuba,
Puis l'Éternel s'adressant à Job lui dit:
2 “Mai neman sa wa wani laifi zai iya ja da Maɗaukaki? Bari mai tuhumar Allah yă amsa masa.”
Le censeur prend-il encore le Tout-puissant à partie? Que l'accusateur de Dieu réponde maintenant!
3 Sai Ayuba ya amsa wa Ubangiji,
Et Job répondit à l'Éternel et dit:
4 “Ai, ni ba a bakin kome nake ba ne, ta yaya zan iya amsa maka? Na rufe bakina da hannuna.
Voici, je suis trop chétif, que répliquerais-je? Je mets ma main sur ma bouche.
5 Na yi magana sau ɗaya amma ba ni da amsa, sau biyu, amma ba zan ƙara cewa kome ba.”
J'ai parlé une fois, je ne répondrai pas, une seconde fois, et je ne le ferai plus.
6 Sa’an nan Ubangiji ya yi wa Ayuba magana ta cikin guguwa,
Et l'Éternel répondit à Job du milieu de la tempête et dit:
7 “Ka tashi tsaye ka tsaya da ƙarfi kamar namiji; zan yi maka tambaya kuma za ka amsa mini.
Allons! ceins tes reins, comme un homme! Je t'interrogerai, et tu m'instruiras!
8 “Ko za ka ƙi yarda da shari’ata? Za ka ba ni laifi don ka nuna kai marar laifi ne?
Penses-tu à déchirer aussi mes arrêts, à me condamner, pour paraître innocent?
9 Ko hannunka irin na Allah ne, kuma ko muryarka za tă iya tsawa kamar ta Allah?
Ou bien as-tu un bras comme Dieu, et de la voix comme Lui peux-tu tonner?
10 Sai ka yi wa kanka ado da ɗaukaka da girma, ka yafa daraja da muƙami.
Eh bien! revêts donc l'éclat et la grandeur! pare-toi de la gloire et de la magnificence!
11 Ka saki fushinka, ka dubi dukan wani mai girman kai ka wulaƙanta shi.
Epanche les flots de ta colère, Et d'un regard terrasse tous les superbes!
12 Ka dubi duk wani mai girman kai ka ƙasƙantar da shi, ka tattake mugaye a inda ka tsaya.
D'un regard abats le superbe, et écrase les impies sur la place!
13 Ka bizne su duka tare ka rufe fuskokinsu a cikin kabari.
Abîme-les tous dans la poudre, et cache leurs fronts dans les ténèbres!
14 Sa’an nan ni kaina zan shaida maka cewa hannun damanka zai iya cetonka.
Alors de mon côté je pourrai te louer de ce qu'en ta main tu trouves des ressources.
15 “Dubi dorina, wadda na halicce ku tare kuma ciyawa take ci kamar sa.
Vois le Béhémoth que je créai comme toi! Ainsi que le bœuf, il broute l'herbe.
16 Ga shi ƙarfinta yana a ƙugunta ikonta yana cikin tsokar cikinta.
Vois la force qu'il a dans ses reins, et la vigueur qu'il a dans les muscles de sa panse.
17 Wutsiyarta tana da ƙarfi kamar itacen al’ul; jijiyoyin cinyoyinta suna haɗe a wuri ɗaya.
Il replie sa queue [roide] comme un cèdre; les tendons de ses flancs sont entrelacés;
18 Ƙasusuwanta bututun tagulla ne, haƙarƙarinta kamar sandunan ƙarfe.
ses os sont des tubes d'airain, et ses jambes, des barres de fer.
19 Tana ta farko cikin ayyukan Allah, Mahaliccinta kaɗai yake iya tunkarar ta da takobi.
Il est le chef-d'œuvre de Dieu; son Créateur l'arma du glaive
20 Tuddai su suke tanada mata abinci a inda duk namun jeji suke wasa.
dont il fauche sa pâture sur les monts, où folâtrent toutes les bêtes des champs.
21 Tana kwanciya a ƙarƙashin inuwar itacen lotus ta ɓuya cikin kyauro da fadama.
Il se couche sous les feuilles du lotus, et les joncs et le marécage lui donnent un abri.
22 Inuwa ta rufe ta da ƙaddaji, itatuwan wardi na rafi, sun kewaye ta.
Pour lui le lotus entrelace son ombrage, les saules de la rivière l'environnent.
23 Sa’ad da kogi ya cika yana hauka, ba tă damu ba; ba abin da zai same ta ko da a gaban bakinta Urdun yake wucewa.
Voici, que le fleuve se soulève, il n'a point peur; il prend plutôt de l'assurance, quand un Jourdain bouillonne jusqu'à sa bouche.
24 Ko akwai wanda zai iya kama ta ba ta kallo, ko kuma a kama ta da tarko a huda hancinta?
Peut-on, pour le prendre, tromper son regard, ou percer son naseau pour l'enchaîner?