< Ayuba 40 >

1 Ubangiji ya ce wa Ayuba,
And the Lord continued, and he said to Job:
2 “Mai neman sa wa wani laifi zai iya ja da Maɗaukaki? Bari mai tuhumar Allah yă amsa masa.”
Will he who contends with God be so easily silenced? Certainly, he who argues with God must also respond to him.
3 Sai Ayuba ya amsa wa Ubangiji,
Then Job answered the Lord, saying:
4 “Ai, ni ba a bakin kome nake ba ne, ta yaya zan iya amsa maka? Na rufe bakina da hannuna.
What could I possibly answer, since I have been speaking thoughtlessly? I will place my hand over my mouth.
5 Na yi magana sau ɗaya amma ba ni da amsa, sau biyu, amma ba zan ƙara cewa kome ba.”
One thing I have spoken, which I wish I had not said; and another, to which I will add no more.
6 Sa’an nan Ubangiji ya yi wa Ayuba magana ta cikin guguwa,
But the Lord, answering Job out of the whirlwind, said:
7 “Ka tashi tsaye ka tsaya da ƙarfi kamar namiji; zan yi maka tambaya kuma za ka amsa mini.
Gird your waist like a man. I will question you, and you must answer me.
8 “Ko za ka ƙi yarda da shari’ata? Za ka ba ni laifi don ka nuna kai marar laifi ne?
Will you make my judgment null and void; and will you condemn me so that you may be justified?
9 Ko hannunka irin na Allah ne, kuma ko muryarka za tă iya tsawa kamar ta Allah?
And do you have an arm like God, or a voice like thunder?
10 Sai ka yi wa kanka ado da ɗaukaka da girma, ka yafa daraja da muƙami.
Envelop yourself with splendor, and raise yourself up on high, and be glorious, and put on splendid garments.
11 Ka saki fushinka, ka dubi dukan wani mai girman kai ka wulaƙanta shi.
Scatter the arrogant with your wrath, and, when you see all the arrogant, humble them.
12 Ka dubi duk wani mai girman kai ka ƙasƙantar da shi, ka tattake mugaye a inda ka tsaya.
Look down upon each of the arrogant and confound them, and crush the impious in their place.
13 Ka bizne su duka tare ka rufe fuskokinsu a cikin kabari.
Hide them in the dust together and plunge their faces into the pit.
14 Sa’an nan ni kaina zan shaida maka cewa hannun damanka zai iya cetonka.
Then I will confess that your right hand is able to save you.
15 “Dubi dorina, wadda na halicce ku tare kuma ciyawa take ci kamar sa.
Behold, the behemoth, whom I created along with you, eats hay like an ox.
16 Ga shi ƙarfinta yana a ƙugunta ikonta yana cikin tsokar cikinta.
His strength is in his lower back, and his power is in the center of his abdomen.
17 Wutsiyarta tana da ƙarfi kamar itacen al’ul; jijiyoyin cinyoyinta suna haɗe a wuri ɗaya.
He draws up his tail like a cedar; the sinews of his thighs have been drawn together.
18 Ƙasusuwanta bututun tagulla ne, haƙarƙarinta kamar sandunan ƙarfe.
His bones are like pipes of brass; his cartilage is like plates of iron.
19 Tana ta farko cikin ayyukan Allah, Mahaliccinta kaɗai yake iya tunkarar ta da takobi.
He is the beginning of the ways of God, who made him; he will use him as his sword.
20 Tuddai su suke tanada mata abinci a inda duk namun jeji suke wasa.
The mountains bring forth grass for him; all the beasts of the field will play there.
21 Tana kwanciya a ƙarƙashin inuwar itacen lotus ta ɓuya cikin kyauro da fadama.
He sleeps in the shadows, under the cover of branches, and in moist places.
22 Inuwa ta rufe ta da ƙaddaji, itatuwan wardi na rafi, sun kewaye ta.
The shadows cover his shadow; the willows of the brook will encircle him.
23 Sa’ad da kogi ya cika yana hauka, ba tă damu ba; ba abin da zai same ta ko da a gaban bakinta Urdun yake wucewa.
Behold, he will drink a river and not be amazed, and he has confidence that the Jordan could flow into his mouth.
24 Ko akwai wanda zai iya kama ta ba ta kallo, ko kuma a kama ta da tarko a huda hancinta?
He will seize him through his eyes, as if with a hook, and he will bore through his nostrils, as if with stakes.

< Ayuba 40 >