< Ayuba 37 >

1 “Wannan ya sa gabana ya fāɗi, zuciyata ta yi tsalle.
Ja, vid sådant förskräckes mitt hjärta, bävande spritter det upp.
2 Ka saurara! Ka saurari rurin muryarsa, tsawar da take fita daga bakinsa.
Hören, hören huru hans röst ljuder vred, hören dånet som går ut ur hans mun.
3 Ya saki walƙiyarsa, a ƙarƙashin dukan sammai ya kuma aika ta ko’ina a cikin duniya.
Han sänder det åstad, så långt himmelen når, och sina ljungeldar bort till jordens ändar.
4 Bayan wannan sai ƙarar rurinsa ta biyo; Ya tsawata da muryarsa mai girma. Sa’ad da ya sāke yin tsawa ba ya rage wani abu.
Efteråt ryter så dånet, när han dundrar med sin väldiga röst; och på ljungeldarna spar han ej, då hans röst låter höra sig.
5 Muryar Allah tana tsawatawa a hanyoyi masu ban al’ajabi; yana yin manyan abubuwa waɗanda sun wuce ganewarmu.
Ja, underbart dundrar Gud med sin röst, stora ting gör han, utöver vad vi förstå.
6 Yakan ce wa dusar ƙanƙara, ‘Fāɗo a kan duniya,’ ya kuma ce wa ruwa, ‘Zubo da ƙarfi.’
Se, åt snön giver han bud: "Fall ned till jorden", så ock åt regnskuren, åt sitt regnflödes mäktiga skur.
7 Domin dukan mutanen da ya halitta za su san aikinsa, ya hana kowane mutum yin wahalar aiki.
Därmed fjättrar han alla människors händer, så att envar som han har skapat kan lära därav.
8 Dabbobi sun ɓoye; sun zauna cikin kogunansu.
Då draga sig vilddjuren in i sina gömslen, och i sina kulor lägga de sig till ro.
9 Guguwa tana fitowa daga inda take, sanyi kuma daga iska mai sanyi.
Från Stjärngemaket kommer då storm och köld genom nordanhimmelens stjärnor;
10 Da numfashinsa Allah yana samar da ƙanƙara sai manyan ruwaye su zama ƙanƙara.
med sin andedräkt sänder Gud frost, och de vida vattnen betvingas.
11 Yana cika gizagizai da lema; yana baza walƙiyarsa ta cikinsu.
Skyarna lastar han ock med väta och sprider omkring sina ljungeldsmoln.
12 Bisa ga bishewarsa suke juyawa a kan fuskar duniya, suna yin dukan abin da ya umarce su su yi.
De måste sväva än hit, än dit, alltefter hans rådslut och de uppdrag de få, vadhelst han ålägger dem på jordens krets.
13 Yana aiko da ruwa domin horon mutane, ko kuma don yă jiƙa duniya yă kuma nuna ƙaunarsa.
Än är det som tuktoris, än med hjälp åt hans jord, än är det med nåd som han låter dem komma.
14 “Ka saurari wannan Ayuba; ka tsaya ka dubi abubuwan al’ajabi na Allah.
Lyssna då härtill, du Job; stanna och betänk Guds under.
15 Ko ka san yadda Allah yake iko da gizagizai ya kuma sa walƙiyarsa ta haskaka?
Förstår du på vad sätt Gud styr deras gång och låter ljungeldarna lysa fram ur sina moln?
16 Ko ka san yadda gizagizai suke tsayawa cik a sararin sama, waɗannan abubuwa al’ajabi na mai cikakken sani.
Förstår du lagen för skyarnas jämvikt, den Allvises underbara verk?
17 Kai mai sa kaya don ka ji ɗumi lokacin da iska mai sanyi take hurawa,
Förstår du huru kläderna bliva dig så heta, när han låter jorden domna under sunnanvinden?
18 ko za ka iya shimfiɗa sararin sama tare da shi da ƙarfi kamar madubi?
Kan du välva molnhimmelen så som han, så fast som en spegel av gjuten metall?
19 “Gaya mana abin da ya kamata mu ce masa; ba za mu iya kawo ƙara ba domin duhunmu.
Lär oss då vad vi skola säga till honom; för vårt mörkers skull hava vi intet att lägga fram.
20 Ko za a gaya masa cewa ina so in yi magana? Ko wani zai nemi a haɗiye shi?
Ej må det bebådas honom att jag vill tala. Månne någon begär sitt eget fördärv?
21 Yanzu ba wanda zai iya kallon rana, yadda take da haske a sararin sama bayan iska ta share ta.
Men synes icke redan skenet? Strålande visar han sig ju mellan skyarna, där vinden har gått fram och sopat dem undan.
22 Yana fitowa daga arewa da haske na zinariya, Allah yana zuwa da ɗaukaka mai ban al’ajabi.
I guldglans kommer han från norden. Ja, Gud är höljd i fruktansvärt majestät;
23 Maɗaukaki ya fi ƙarfin ganewarmu, shi babban mai iko ne, mai gaskiya da babban adalci, ba ya cutar mutum.
den Allsmäktige kunna vi icke fatta, honom som är så stor i kraft, honom som ej kränker rätten, ej strängaste rättfärdighet.
24 Saboda haka, mutane suke girmama shi, ko bai kula da waɗanda suke gani su masu hikima ba ne?”
Fördenskull frukta människorna honom; men de självkloka -- dem alla aktar han ej på.

< Ayuba 37 >