< Ayuba 36 >

1 Elihu ya ci gaba,
حوصله کن و به آنچه که دربارهٔ خدا می‌گویم گوش بده.
2 “Ka ɗan ƙara haƙuri da ni kaɗan, zan kuma nuna maka cewa akwai sauran abubuwan da zan faɗa a madadin Allah.
3 Daga nesa na sami sanina; zan nuna cewa Mahaliccina shi mai gaskiya ne.
من با دانش وسیع خود به تو نشان خواهم داد که خالق من عادل است.
4 Abin da zan gaya maka ba ƙarya ba ne; mai cikakken sani yana tare da kai.
بدان کسی که در مقابل تو ایستاده، مردی فاضل است و آنچه می‌گوید عین حقیقت می‌باشد.
5 “Allah mai iko ne, amma ba ya rena mutane; shi mai girma ne cikin manufarsa.
فهم و دانایی خدا کامل است. او قادر به انجام هر کاری است، با وجود این کسی را خوار نمی‌شمارد.
6 Ba ya barin mugaye da rai sai dai yana ba waɗanda ake tsanantawa hakkinsu.
او بدکاران را بی‌سزا نمی‌گذارد و به داد مظلومان می‌رسد.
7 Ba ya fasa duban masu adalci; yana sa su tare da sarakuna yana ɗaukaka su har abada.
از نیکان حمایت کرده، آنها را چون پادشاهان سرافراز می‌نماید و عزت ابدی به آنها می‌بخشد.
8 Amma in mutane suna daure da sarƙoƙi, ƙunci kuma ya daure su,
هرگاه در زحمت بیفتند و اسیر و گرفتار شوند،
9 yana gaya musu abin da suka yi, cewa sun yi zunubi da girman kai.
خدا اعمال گناه‌آلود و تکبر ایشان را که موجب گرفتاریشان شده به آنها نشان می‌دهد
10 Yana sa su saurari gyara yă kuma umarce su su tuba daga muguntarsu.
و به ایشان کمک می‌کند که به سخنان او توجه نمایند و از گناه دست بکشند.
11 In sun yi biyayya suka bauta masa, za su yi rayuwa dukan kwanakinsu cikin wadata shekarunsu kuma cikin kwanciyar zuciya.
اگر به او گوش داده، از او اطاعت کنند، آنگاه تمام عمر شادمان و خوشبخت خواهند بود؛
12 Amma in ba su saurara ba, za su hallaka da takobi kuma za su mutu ba ilimi.
و اگر گوش ندهند، در جنگ هلاک شده، در جهل و نادانی خواهند مرد.
13 “Waɗanda ba su da Allah a zuciyarsu su ne suke riƙe fushi; ko sa’ad da ya ba su horo, ba su neman taimakonsa.
اشخاص خدانشناس در دل خود خشم را می‌پرورانند و حتی وقتی خدا آنها را تنبیه می‌کند از او کمک نمی‌طلبند.
14 Suna mutuwa tun suna matasa, cikin ƙazamar rayuwar karuwanci.
آنها به سوی فساد و هرزگی کشیده می‌شوند و در عنفوان جوانی می‌میرند.
15 Amma yana kuɓutar da masu wahala; yana magana da su cikin wahalarsu.
خدا به‌وسیلۀ سختی و مصیبت با انسان سخن می‌گوید و او را از رنجهایش می‌رهاند.
16 “Yana so yă rinjaye ka daga haƙoran ƙunci, zuwa wuri mai sauƙi inda ba matsi zuwa teburinka cike da abincin da kake so.
خدا می‌خواهد تو را از این سختی و مصیبت برهاند و تو را کامیاب سازد تا بتوانی در امنیت و وفور نعمت زندگی کنی.
17 Amma yanzu an cika ka da hukuncin da ya kamata a yi wa mugaye; shari’a da kuma gaskiya sun kama ka.
اما در حال حاضر فکرت با داوری شریران درگیر است. نگران نباش داوری و عدالت اجرا خواهند شد.
18 Ka yi hankali kada wani yă ruɗe ka da arziki; kada ka bar toshiya ta sa ka juya.
مواظب باش کسی با رشوه و ثروت، تو را از راه راست منحرف نسازد.
19 Dukiyarka ko dukan yawan ƙoƙarinka sun isa su riƙe ka su hana ka shan ƙunci?
فریاد تو به جایی نخواهد رسید و با همۀ تلاشهای سختت نمی‌توانی از این تنگنا آزاد شوی.
20 Kada ka yi marmari dare yă yi, don a fitar da mutane daga gidajensu.
در آرزوی فرا رسیدن شب نباش، تا مردم را از مکانشان بیرون بِکِشی.
21 Ka kula kada ka juya ga mugunta, abin da ka fi so fiye da wahala.
از گناه دوری کن، زیرا خدا این گرفتاری را به همین سبب فرستاده است تا تو را از گناه دور نگه دارد.
22 “An ɗaukaka Allah cikin ikonsa. Wane ne malami kamar sa?
بدان که قدرت خدا برتر از هر قدرتی است. کیست که مثل او بتواند به انسان تعلیم دهد؟
23 Wane ne ya nuna masa hanyar da zai bi, ko kuma wane ne ya ce masa, ‘Ba ka yi daidai ba?’
چه کسی می‌تواند چیزی به خدا یاد دهد و یا او را به بی‌انصافی متهم سازد؟
24 Ka tuna ka ɗaukaka aikinsa, waɗanda mutane suka yaba a cikin waƙa.
به یاد داشته باش که کارهای او را تجلیل کنی، کارهایی که مردمان در وصف آنها سراییده‌اند.
25 Dukan’yan adam sun gani; mutane sun hanga daga nesa.
همهٔ مردم کارهای خدا را مشاهده می‌کنند، هر چند از درک کامل آنها عاجزند.
26 Allah mai girma ne, ya wuce ganewarmu! Yawan shekarunsa ba su bincikuwa.
زیرا خدا به قدری عظیم است که نمی‌توان او را آنچنان که باید شناخت و به ازلیت وی پی برد.
27 “Yana sa ruwa yă zama tururi yă zubo daga sama.
او بخار آب را به بالا می‌فرستد و آن را به باران تبدیل می‌کند.
28 Gizagizai suna zubo da raɓarsu kuma ruwan sama yana zubowa’yan adam a wadace.
سپس ابرها آن را به فراوانی برای انسان فرو می‌ریزند.
29 Wane ne zai iya gane yadda ya shimfiɗa gizagizai yadda yake tsawa daga wurin zamansa?
آیا واقعاً کسی چگونگی گسترده شدن ابرها در آسمان و برخاستن غرش رعد از درون آنها را می‌فهمد؟
30 Dubi yadda ya baza walƙiyarsa kewaye da shi, tana haskaka zurfin teku.
ببینید چگونه سراسر آسمان را با برق روشن می‌سازد، ولی اعماق دریا همچنان تاریک می‌ماند.
31 Haka yake mulkin al’ummai yana kuma tanada abinci a wadace.
خدا با کارهای حیرت‌انگیز خود غذای فراوان در دسترس همهٔ انسانها قرار می‌دهد.
32 Yana cika hannuwansa da walƙiya kuma yana ba ta umarni tă fāɗi a inda ya yi nufi.
او دستهای خود را با تیرهای آتشین برق پر می‌کند و هر یک از آنها را به سوی هدف پرتاب می‌نماید.
33 Tsawarsa tana nuna cewa babbar iska da ruwa suna zuwa; ko shanu sun san da zuwansa.
رعد او از فرا رسیدن طوفان خبر می‌دهد؛ و حتی حیوانات نیز از آمدن آن آگاه می‌شوند.

< Ayuba 36 >