< Ayuba 35 >
Y PROCEDIENDO Eliú en su razonamiento, dijo:
2 “Ko kana tsammani wannan gaskiya ne? Kana cewa, ‘Ni mai adalci ne a gaban Allah.’
¿Piensas ser conforme á derecho esto [que] dijiste: Más justo soy yo que Dios?
3 Duk da haka kana tambayarsa cewa, ‘Wace riba nake da ita, kuma mene ne zan samu ta wurin ƙin yin zunubi?’
Porque dijiste: ¿Qué ventaja sacarás tú de ello? ¿ó qué provecho tendré de mi pecado?
4 “Zan so in ba ka amsa kai tare da abokanka.
Yo te responderé razones, y á tus compañeros contigo.
5 Ku ɗaga kai ku dubi sama ku gani; ku dubi gizagizai a samanku.
Mira á los cielos, y ve, y considera que las nubes son más altas que tú.
6 In kun yi zunubi ta yaya wannan zai shafi Allah? In zunubanku sun yi yawa, me wannan zai yi masa?
Si pecares, ¿qué habrás hecho contra él? y si tus rebeliones se multiplicaren, ¿qué le harás tú?
7 In kuna da adalci, me kuka ba shi, ko kuma me ya karɓa daga hannunku?
Si fueres justo, ¿qué le darás á él? ¿ó qué recibirá de tu mano?
8 Muguntarku takan shafi mutum kamar ku ne kaɗai, adalcinku kuma yakan shafi’yan adam ne kaɗai.
Al hombre como tú [dañará] tu impiedad, y al hijo del hombre [aprovechará] tu justicia.
9 “Mutane suna kuka don yawan zalunci; suna roƙo don taimako daga hannu mai ƙarfi.
A causa de la multitud de las violencias clamarán, y se lamentarán por el poderío de los grandes.
10 Amma ba wanda ya ce, ‘Ina Allah wanda ya halicce ni, mai ba da waƙoƙi cikin dare,
Y ninguno dice: ¿Dónde está Dios mi Hacedor, que da canciones en la noche,
11 wanda ya fi koya mana fiye da dabbobin duniya ya kuma sa muka fi tsuntsayen cikin iska hikima.’
Que nos enseña más que á las bestias de la tierra, y nos hace sabios más que las aves del cielo?
12 Ba ya amsawa lokacin da mutane suka yi kira don taimako domin girman kan mugaye.
Allí clamarán, y él no oirá, por la soberbia de los malos.
13 Lalle Allah ba ya sauraron roƙonsu na wofi; Maɗaukaki ba ya kula da roƙonsu.
Ciertamente Dios no oirá la vanidad, ni la mirará el Omnipotente.
14 Ta yaya zai saurara sosai ko zai saurara lokacin da kake cewa ba ka ganinsa, cewa ka kawo ƙara a wurinsa kuma dole ka jira shi.
Aunque más digas, No lo mirará; haz juicio delante de él, y en él espera.
15 Kuma ka ce, ba ya ba da horo cikin fushinsa ko kaɗan ba ya kula da mugunta.
Mas ahora, porque en su ira no visita, ni conoce con rigor,
16 Saboda haka Ayuba ya buɗe baki yana magana barkatai; yana ta yawan magana ba tare da sani ba.”
por eso Job abrió su boca vanamente, y multiplica palabras sin sabiduría.