< Ayuba 35 >

1 Sai Elihu ya ce,
Entonces Elihú continuó diciendo:
2 “Ko kana tsammani wannan gaskiya ne? Kana cewa, ‘Ni mai adalci ne a gaban Allah.’
“¿Crees que es honesto afirmar que tienes razón ante Dios?
3 Duk da haka kana tambayarsa cewa, ‘Wace riba nake da ita, kuma mene ne zan samu ta wurin ƙin yin zunubi?’
Y preguntas: ‘¿Qué beneficio obtengo? ¿De qué me ha servido no pecar?’
4 “Zan so in ba ka amsa kai tare da abokanka.
“¡Te lo diré, y a tus amigos también!
5 Ku ɗaga kai ku dubi sama ku gani; ku dubi gizagizai a samanku.
Sólo tienes que mirar al cielo y ver. Observa las nubes en lo alto.
6 In kun yi zunubi ta yaya wannan zai shafi Allah? In zunubanku sun yi yawa, me wannan zai yi masa?
Si pecas, ¿en qué perjudica eso a Dios? ¿Cómo afectan tus muchos pecados a Dios?
7 In kuna da adalci, me kuka ba shi, ko kuma me ya karɓa daga hannunku?
Si haces lo correcto, ¿qué bien le haces a él?
8 Muguntarku takan shafi mutum kamar ku ne kaɗai, adalcinku kuma yakan shafi’yan adam ne kaɗai.
No. Tus pecados sólo afectan a la gente como tú, y cualquier bien que hagas también les afecta a ellos.
9 “Mutane suna kuka don yawan zalunci; suna roƙo don taimako daga hannu mai ƙarfi.
“La gente clama a causa de las terribles persecuciones, pide que alguien la salve de sus opresores.
10 Amma ba wanda ya ce, ‘Ina Allah wanda ya halicce ni, mai ba da waƙoƙi cikin dare,
Pero nadie pregunta: ‘¿Dónde está mi Dios creador, el que inspira cantos en la noche,
11 wanda ya fi koya mana fiye da dabbobin duniya ya kuma sa muka fi tsuntsayen cikin iska hikima.’
que nos enseña más que los animales y nos hace más sabios que las aves?’
12 Ba ya amsawa lokacin da mutane suka yi kira don taimako domin girman kan mugaye.
Cuando claman por ayuda, Dios no responde porque son gente orgullosa y malvada.
13 Lalle Allah ba ya sauraron roƙonsu na wofi; Maɗaukaki ba ya kula da roƙonsu.
Dios no escucha sus gritos vacíos; el Todopoderoso no les hace caso.
14 Ta yaya zai saurara sosai ko zai saurara lokacin da kake cewa ba ka ganinsa, cewa ka kawo ƙara a wurinsa kuma dole ka jira shi.
¿Cuánto menos te escuchará Dios cuando le digas que no te ve? Tu caso está ante él, así que tienes que esperarlo.
15 Kuma ka ce, ba ya ba da horo cikin fushinsa ko kaɗan ba ya kula da mugunta.
“Estás diciendo que Dios no castiga a la gente en su ira y presta poca atención al pecado.
16 Saboda haka Ayuba ya buɗe baki yana magana barkatai; yana ta yawan magana ba tare da sani ba.”
Tú, Job, hablas sin sentido, haciendo largos discursos cuando no sabes nada!”

< Ayuba 35 >