< Ayuba 35 >

1 Sai Elihu ya ce,
Још говори Елијуј и рече:
2 “Ko kana tsammani wannan gaskiya ne? Kana cewa, ‘Ni mai adalci ne a gaban Allah.’
Мислиш ли да си право рекао: Моја је правда већа од Божије?
3 Duk da haka kana tambayarsa cewa, ‘Wace riba nake da ita, kuma mene ne zan samu ta wurin ƙin yin zunubi?’
Јер си рекао: Шта ће ми помоћи, каква ће ми бити корист, да не грешим?
4 “Zan so in ba ka amsa kai tare da abokanka.
Ја ћу одговорити теби и друговима твојим с тобом.
5 Ku ɗaga kai ku dubi sama ku gani; ku dubi gizagizai a samanku.
Погледај небо, и види; погледај облаке, како су виши од тебе.
6 In kun yi zunubi ta yaya wannan zai shafi Allah? In zunubanku sun yi yawa, me wannan zai yi masa?
Ако грешиш, шта ћеш Му учинити? Или ако се умноже безакоња твоја, шта ћеш Му наудити?
7 In kuna da adalci, me kuka ba shi, ko kuma me ya karɓa daga hannunku?
Ако си праведан, шта ћеш Му дати? Или шта ће примити из руке твоје?
8 Muguntarku takan shafi mutum kamar ku ne kaɗai, adalcinku kuma yakan shafi’yan adam ne kaɗai.
Човеку какав си може наудити твоја злоћа, и сину човечијем помоћи твоја правда.
9 “Mutane suna kuka don yawan zalunci; suna roƙo don taimako daga hannu mai ƙarfi.
Вапију од великог насиља којима се чини, и вичу на руку силних;
10 Amma ba wanda ya ce, ‘Ina Allah wanda ya halicce ni, mai ba da waƙoƙi cikin dare,
А ни један не говори: Где је Бог, Створитељ мој, који даје песму ноћу;
11 wanda ya fi koya mana fiye da dabbobin duniya ya kuma sa muka fi tsuntsayen cikin iska hikima.’
Који чини те смо разумнији од зверја земаљског, и мудрији од птица небеских.
12 Ba ya amsawa lokacin da mutane suka yi kira don taimako domin girman kan mugaye.
Тамо вичу с охолости злих људи, али не бивају услишени.
13 Lalle Allah ba ya sauraron roƙonsu na wofi; Maɗaukaki ba ya kula da roƙonsu.
Јер Бог не слуша таштину, и Свемогући не гледа на њу.
14 Ta yaya zai saurara sosai ko zai saurara lokacin da kake cewa ba ka ganinsa, cewa ka kawo ƙara a wurinsa kuma dole ka jira shi.
А камоли кад кажеш: Не видиш то. Пред Њим је суд; чекај Га.
15 Kuma ka ce, ba ya ba da horo cikin fushinsa ko kaɗan ba ya kula da mugunta.
А сада чим те гнев походи, није ништа, нити је гледао на све што си учинио;
16 Saboda haka Ayuba ya buɗe baki yana magana barkatai; yana ta yawan magana ba tare da sani ba.”
Зато Јов на празно отвара уста своја, и безумно умножава речи.

< Ayuba 35 >