< Ayuba 35 >
И продолжал Елиуй и сказал:
2 “Ko kana tsammani wannan gaskiya ne? Kana cewa, ‘Ni mai adalci ne a gaban Allah.’
считаешь ли ты справедливым, что сказал: я правее Бога?
3 Duk da haka kana tambayarsa cewa, ‘Wace riba nake da ita, kuma mene ne zan samu ta wurin ƙin yin zunubi?’
Ты сказал: что пользы мне? и какую прибыль я имел бы пред тем, как если бы я и грешил?
4 “Zan so in ba ka amsa kai tare da abokanka.
Я отвечу тебе и твоим друзьям с тобою:
5 Ku ɗaga kai ku dubi sama ku gani; ku dubi gizagizai a samanku.
взгляни на небо и смотри; воззри на облака, они выше тебя.
6 In kun yi zunubi ta yaya wannan zai shafi Allah? In zunubanku sun yi yawa, me wannan zai yi masa?
Если ты грешишь, что делаешь ты Ему? и если преступления твои умножаются, что причиняешь ты Ему?
7 In kuna da adalci, me kuka ba shi, ko kuma me ya karɓa daga hannunku?
Если ты праведен, что даешь Ему? или что получает Он от руки твоей?
8 Muguntarku takan shafi mutum kamar ku ne kaɗai, adalcinku kuma yakan shafi’yan adam ne kaɗai.
Нечестие твое относится к человеку, как ты, и праведность твоя к сыну человеческому.
9 “Mutane suna kuka don yawan zalunci; suna roƙo don taimako daga hannu mai ƙarfi.
От множества притеснителей стонут притесняемые, и от руки сильных вопиют.
10 Amma ba wanda ya ce, ‘Ina Allah wanda ya halicce ni, mai ba da waƙoƙi cikin dare,
Но никто не говорит: где Бог, Творец мой, Который дает песни в ночи,
11 wanda ya fi koya mana fiye da dabbobin duniya ya kuma sa muka fi tsuntsayen cikin iska hikima.’
Который научает нас более, нежели скотов земных, и вразумляет нас более, нежели птиц небесных?
12 Ba ya amsawa lokacin da mutane suka yi kira don taimako domin girman kan mugaye.
Там они вопиют, и Он не отвечает им, по причине гордости злых людей.
13 Lalle Allah ba ya sauraron roƙonsu na wofi; Maɗaukaki ba ya kula da roƙonsu.
Но неправда, что Бог не слышит и Вседержитель не взирает на это.
14 Ta yaya zai saurara sosai ko zai saurara lokacin da kake cewa ba ka ganinsa, cewa ka kawo ƙara a wurinsa kuma dole ka jira shi.
Хотя ты сказал, что ты не видишь Его, но суд пред Ним, и - жди Его.
15 Kuma ka ce, ba ya ba da horo cikin fushinsa ko kaɗan ba ya kula da mugunta.
Но ныне, потому что гнев Его не посетил его и он не познал Его во всей строгости,
16 Saboda haka Ayuba ya buɗe baki yana magana barkatai; yana ta yawan magana ba tare da sani ba.”
Иов и открыл легкомысленно уста свои и безрассудно расточает слова.