< Ayuba 35 >

1 Sai Elihu ya ce,
Eliú respondeu mais, dizendo:
2 “Ko kana tsammani wannan gaskiya ne? Kana cewa, ‘Ni mai adalci ne a gaban Allah.’
Pensas tu ser direito dizeres: Maior é a minha justiça do que a de Deus?
3 Duk da haka kana tambayarsa cewa, ‘Wace riba nake da ita, kuma mene ne zan samu ta wurin ƙin yin zunubi?’
Porque disseste: Para que ela te serve? [Ou]: Que proveito terei dela mais que meu pecado?
4 “Zan so in ba ka amsa kai tare da abokanka.
Eu darei reposta a ti, e a teus amigos contigo.
5 Ku ɗaga kai ku dubi sama ku gani; ku dubi gizagizai a samanku.
Olha para os céus, e vê; e observa as nuvens, [que] são mais altas que tu.
6 In kun yi zunubi ta yaya wannan zai shafi Allah? In zunubanku sun yi yawa, me wannan zai yi masa?
Se tu pecares, que [mal] farás contra ele? Se tuas transgressões se multiplicarem, que [mal] lhe farás?
7 In kuna da adalci, me kuka ba shi, ko kuma me ya karɓa daga hannunku?
Se fores justo, que lhe darás? Ou o que ele receberá de tua mão?
8 Muguntarku takan shafi mutum kamar ku ne kaɗai, adalcinku kuma yakan shafi’yan adam ne kaɗai.
Tua perversidade [poderia afetar] a outro homem como tu; e tua justiça [poderia ser proveitosa] a [algum] filho do homem.
9 “Mutane suna kuka don yawan zalunci; suna roƙo don taimako daga hannu mai ƙarfi.
[Os aflitos] clamam por causa da grande opressão; eles gritam por causa do poder dos grandes.
10 Amma ba wanda ya ce, ‘Ina Allah wanda ya halicce ni, mai ba da waƙoƙi cikin dare,
Porém ninguém diz: Onde está Deus, meu Criador, que dá canções na noite,
11 wanda ya fi koya mana fiye da dabbobin duniya ya kuma sa muka fi tsuntsayen cikin iska hikima.’
Que nos ensina mais que aos animais da terra, e nos faz sábios mais que as aves do céu?
12 Ba ya amsawa lokacin da mutane suka yi kira don taimako domin girman kan mugaye.
Ali clamam, porém ele não responde, por causa da arrogância dos maus.
13 Lalle Allah ba ya sauraron roƙonsu na wofi; Maɗaukaki ba ya kula da roƙonsu.
Certamente Deus não ouvirá a súplica vazia, nem o Todo-Poderoso dará atenção a ela.
14 Ta yaya zai saurara sosai ko zai saurara lokacin da kake cewa ba ka ganinsa, cewa ka kawo ƙara a wurinsa kuma dole ka jira shi.
Quanto menos ao que disseste: que tu não o vês! Porém o juízo está diante dele; portanto espera nele.
15 Kuma ka ce, ba ya ba da horo cikin fushinsa ko kaɗan ba ya kula da mugunta.
Mas agora, já que a ira dele [ainda] não está castigando, e ele não deu completa atenção à arrogância,
16 Saboda haka Ayuba ya buɗe baki yana magana barkatai; yana ta yawan magana ba tare da sani ba.”
Por isso Jó abriu sua boca em vão, e multiplicou palavras sem conhecimento.

< Ayuba 35 >