< Ayuba 35 >

1 Sai Elihu ya ce,
۱
2 “Ko kana tsammani wannan gaskiya ne? Kana cewa, ‘Ni mai adalci ne a gaban Allah.’
«آیا این را انصاف می‌شماری که گفتی من از خدا عادل تر هستم؟۲
3 Duk da haka kana tambayarsa cewa, ‘Wace riba nake da ita, kuma mene ne zan samu ta wurin ƙin yin zunubi?’
زیرا گفته‌ای برای توچه فایده خواهد شد، و به چه چیز بیشتر از گناهم منفعت خواهم یافت.۳
4 “Zan so in ba ka amsa kai tare da abokanka.
من تو را جواب می‌گویم ورفقایت را با تو.۴
5 Ku ɗaga kai ku dubi sama ku gani; ku dubi gizagizai a samanku.
به سوی آسمانها نظر کن و ببین وافلاک را ملاحظه نما که از تو بلندترند.۵
6 In kun yi zunubi ta yaya wannan zai shafi Allah? In zunubanku sun yi yawa, me wannan zai yi masa?
اگر گناه کردی به او چه رسانیدی؟ و اگر تقصیرهای تو بسیار شد برای وی چه کردی؟۶
7 In kuna da adalci, me kuka ba shi, ko kuma me ya karɓa daga hannunku?
اگر بی‌گناه شدی به او چه بخشیدی؟ و یا از دست تو چه چیز را گرفته است؟۷
8 Muguntarku takan shafi mutum kamar ku ne kaɗai, adalcinku kuma yakan shafi’yan adam ne kaɗai.
شرارت تو به مردی چون تو (ضرر می‌رساند) و عدالت تو به بنی آدم (فایده می‌رساند).۸
9 “Mutane suna kuka don yawan zalunci; suna roƙo don taimako daga hannu mai ƙarfi.
از کثرت ظلمها فریاد برمی آورند واز دست زورآوران استغاثه می‌کنند،۹
10 Amma ba wanda ya ce, ‘Ina Allah wanda ya halicce ni, mai ba da waƙoƙi cikin dare,
و کسی نمی گوید که خدای آفریننده من کجا است که شبانگاه سرودها می‌بخشد۱۰
11 wanda ya fi koya mana fiye da dabbobin duniya ya kuma sa muka fi tsuntsayen cikin iska hikima.’
و ما را از بهایم زمین تعلیم می‌دهد، و از پرندگان آسمان حکمت می‌بخشد.۱۱
12 Ba ya amsawa lokacin da mutane suka yi kira don taimako domin girman kan mugaye.
پس به‌سبب تکبر شریران فریادمی کنند اما او اجابت نمی نماید،۱۲
13 Lalle Allah ba ya sauraron roƙonsu na wofi; Maɗaukaki ba ya kula da roƙonsu.
زیرا خدابطالت را نمی شنود و قادر مطلق برآن ملاحظه نمی فرماید.۱۳
14 Ta yaya zai saurara sosai ko zai saurara lokacin da kake cewa ba ka ganinsa, cewa ka kawo ƙara a wurinsa kuma dole ka jira shi.
هرچند می‌گویی که او رانمی بینم، لیکن دعوی در حضور وی است پس منتظر او باش.۱۴
15 Kuma ka ce, ba ya ba da horo cikin fushinsa ko kaɗan ba ya kula da mugunta.
و اما الان از این سبب که درغضب خویش مطالبه نمی کند و به کثرت گناه اعتنا نمی نماید،۱۵
16 Saboda haka Ayuba ya buɗe baki yana magana barkatai; yana ta yawan magana ba tare da sani ba.”
از این جهت ایوب دهان خودرا به بطالت می‌گشاید و بدون معرفت سخنان بسیار می‌گوید.»۱۶

< Ayuba 35 >