< Ayuba 35 >

1 Sai Elihu ya ce,
エリフまた答へて曰く
2 “Ko kana tsammani wannan gaskiya ne? Kana cewa, ‘Ni mai adalci ne a gaban Allah.’
なんぢは言ふ 我が義しきは神に愈れりと なんぢ之を正しとおもふや
3 Duk da haka kana tambayarsa cewa, ‘Wace riba nake da ita, kuma mene ne zan samu ta wurin ƙin yin zunubi?’
すなはち汝いへらく 是は我に何の益あらんや 罪を犯すに較ぶれば何の愈るところか有んと
4 “Zan so in ba ka amsa kai tare da abokanka.
われ言詞をもて汝およびなんぢにそへる汝の友等に答へん
5 Ku ɗaga kai ku dubi sama ku gani; ku dubi gizagizai a samanku.
天を仰ぎて見よ 汝の上なる高き空を望め
6 In kun yi zunubi ta yaya wannan zai shafi Allah? In zunubanku sun yi yawa, me wannan zai yi masa?
なんぢ罪を犯すとも神に何の害か有ん 愆を熾んにするとも神に何を爲えんや
7 In kuna da adalci, me kuka ba shi, ko kuma me ya karɓa daga hannunku?
汝正義かるとも神に何を與るを得んや 神なんぢの手より何をか受たまはん
8 Muguntarku takan shafi mutum kamar ku ne kaɗai, adalcinku kuma yakan shafi’yan adam ne kaɗai.
なんぢの惡は只なんぢに同じき人を損ぜん而已 なんぢの善は只人の子を益せんのみ
9 “Mutane suna kuka don yawan zalunci; suna roƙo don taimako daga hannu mai ƙarfi.
暴虐の甚だしきに因て叫び 權勢ある者の腕に壓れて呼はる人々あり
10 Amma ba wanda ya ce, ‘Ina Allah wanda ya halicce ni, mai ba da waƙoƙi cikin dare,
然れども一人として我を造れる神は何處にいますやといふ者なし 彼は人をして夜の中に歌を歌ふに至らしめ
11 wanda ya fi koya mana fiye da dabbobin duniya ya kuma sa muka fi tsuntsayen cikin iska hikima.’
地の獸畜よりも善くわれらを教へ 空の鳥よりも我らを智からしめたまふ者なり
12 Ba ya amsawa lokacin da mutane suka yi kira don taimako domin girman kan mugaye.
惡き者等の驕傲ぶるに因て斯のごとく人々叫べども應ふる者あらず
13 Lalle Allah ba ya sauraron roƙonsu na wofi; Maɗaukaki ba ya kula da roƙonsu.
虚しき語を神かならず之を聽たまはず 全能者これを顧みたまはじ
14 Ta yaya zai saurara sosai ko zai saurara lokacin da kake cewa ba ka ganinsa, cewa ka kawo ƙara a wurinsa kuma dole ka jira shi.
汝は我かれを見たてまつらずと言といへども審判は神の前にあり この故に汝彼を待べきなり
15 Kuma ka ce, ba ya ba da horo cikin fushinsa ko kaɗan ba ya kula da mugunta.
今かれ震怒をもて罰することを爲ず 罪愆を深く心に留たまはざる(が如くなる)に因て
16 Saboda haka Ayuba ya buɗe baki yana magana barkatai; yana ta yawan magana ba tare da sani ba.”
ヨブ口を啓きて虚しき事を述べ無知の言語を繁くす

< Ayuba 35 >