< Ayuba 35 >

1 Sai Elihu ya ce,
Und Elihu hob wieder an und sprach:
2 “Ko kana tsammani wannan gaskiya ne? Kana cewa, ‘Ni mai adalci ne a gaban Allah.’
Hast du recht, wenn du sprichst: «Meine Gerechtigkeit kommt von Gott»,
3 Duk da haka kana tambayarsa cewa, ‘Wace riba nake da ita, kuma mene ne zan samu ta wurin ƙin yin zunubi?’
und wenn du sagst: «Was macht es dir, und was schadet es mir, wenn ich sündige?»
4 “Zan so in ba ka amsa kai tare da abokanka.
Ich will dir eine Antwort geben und deinen Gefährten mit dir!
5 Ku ɗaga kai ku dubi sama ku gani; ku dubi gizagizai a samanku.
Siehe zum Himmel empor und betrachte ihn und schau die Wolken an, die höher sind als du!
6 In kun yi zunubi ta yaya wannan zai shafi Allah? In zunubanku sun yi yawa, me wannan zai yi masa?
Wenn du sündigst, was tust du ihm zuleide? Und sind deiner Missetaten viele, was schadest du ihm?
7 In kuna da adalci, me kuka ba shi, ko kuma me ya karɓa daga hannunku?
Bist du aber gerecht, was gibst du ihm, und was empfängt er von deiner Hand?
8 Muguntarku takan shafi mutum kamar ku ne kaɗai, adalcinku kuma yakan shafi’yan adam ne kaɗai.
Aber ein Mensch wie du leidet unter deiner Sünde, und den Menschenkindern nützt deine Gerechtigkeit.
9 “Mutane suna kuka don yawan zalunci; suna roƙo don taimako daga hannu mai ƙarfi.
Sie seufzen unter den vielen Bedrückungen, sie schreien vor dem Arm des Gewaltigen.
10 Amma ba wanda ya ce, ‘Ina Allah wanda ya halicce ni, mai ba da waƙoƙi cikin dare,
Aber man denkt nicht: Wo ist Gott, mein Schöpfer, der Loblieder gibt in der Nacht,
11 wanda ya fi koya mana fiye da dabbobin duniya ya kuma sa muka fi tsuntsayen cikin iska hikima.’
der uns mehr Belehrung zuteil werden ließ als den Tieren des Feldes und uns mehr Verstand gegeben hat als den Vögeln unter dem Himmel?
12 Ba ya amsawa lokacin da mutane suka yi kira don taimako domin girman kan mugaye.
Jene schreien, und er sollte nicht hören trotz des Übermutes der Bösen?
13 Lalle Allah ba ya sauraron roƙonsu na wofi; Maɗaukaki ba ya kula da roƙonsu.
Sollte es umsonst sein, sollte Gott nicht hören und der Allmächtige es nicht sehen?
14 Ta yaya zai saurara sosai ko zai saurara lokacin da kake cewa ba ka ganinsa, cewa ka kawo ƙara a wurinsa kuma dole ka jira shi.
Auch wenn du sagst, du sehest ihn nicht, so liegt die Sache doch vor ihm; warte du nur auf ihn!
15 Kuma ka ce, ba ya ba da horo cikin fushinsa ko kaɗan ba ya kula da mugunta.
Und nun, weil sein Zorn noch nicht gestraft hat, sollte er deshalb das Verbrechen nicht sehr wohl wissen?
16 Saboda haka Ayuba ya buɗe baki yana magana barkatai; yana ta yawan magana ba tare da sani ba.”
So hat also Hiob seinen Mund umsonst aufgesperrt und aus lauter Unverstand so freche Reden geführt!

< Ayuba 35 >