< Ayuba 35 >

1 Sai Elihu ya ce,
Ainsi Eliu dit encore ceci:
2 “Ko kana tsammani wannan gaskiya ne? Kana cewa, ‘Ni mai adalci ne a gaban Allah.’
Est-ce qu’il te semble que ta pensée était équitable, quand tu as dit: Je suis plus juste que Dieu?
3 Duk da haka kana tambayarsa cewa, ‘Wace riba nake da ita, kuma mene ne zan samu ta wurin ƙin yin zunubi?’
Car tu as dit: Ce qui est juste ne vous plaît pas: ou quel avantage retirez-vous, si je pèche?
4 “Zan so in ba ka amsa kai tare da abokanka.
C’est pourquoi je répondrai à tes discours et à tes amis avec toi.
5 Ku ɗaga kai ku dubi sama ku gani; ku dubi gizagizai a samanku.
Regarde en haut le ciel, et vois: et contemple combien la région de l’air est plus haute que toi.
6 In kun yi zunubi ta yaya wannan zai shafi Allah? In zunubanku sun yi yawa, me wannan zai yi masa?
Si tu pèches, en quoi lui nuiras-tu? et si tes iniquités se multiplient, que feras-tu en cela contre lui?
7 In kuna da adalci, me kuka ba shi, ko kuma me ya karɓa daga hannunku?
Mais si tu as agi justement, que lui donneras-tu, ou que recevra-t-il de ta main?
8 Muguntarku takan shafi mutum kamar ku ne kaɗai, adalcinku kuma yakan shafi’yan adam ne kaɗai.
C’est à un homme semblable à toi que nuira ton impiété, et c’est au fils d’un homme que ta justice servira.
9 “Mutane suna kuka don yawan zalunci; suna roƙo don taimako daga hannu mai ƙarfi.
À cause de la multitude des calomniateurs, ils crieront; et ils se lamenteront à cause de la violence du bras des tyrans.
10 Amma ba wanda ya ce, ‘Ina Allah wanda ya halicce ni, mai ba da waƙoƙi cikin dare,
Et aucun d’eux n’a dit: Où est Dieu, qui m’a fait, qui inspire des cantiques pendant la nuit,
11 wanda ya fi koya mana fiye da dabbobin duniya ya kuma sa muka fi tsuntsayen cikin iska hikima.’
Qui nous donne plus d’instruction qu’aux bêtes de la terre, et plus d’intelligence qu’aux oiseaux du ciel?
12 Ba ya amsawa lokacin da mutane suka yi kira don taimako domin girman kan mugaye.
Alors ils crieront, et il ne les exaucera pas, à cause de l’orgueil des méchants.
13 Lalle Allah ba ya sauraron roƙonsu na wofi; Maɗaukaki ba ya kula da roƙonsu.
Ce n’est donc pas en vain que Dieu écoulera leurs cris; et le Tout-Puissant considérera avec attention la cause de chacun.
14 Ta yaya zai saurara sosai ko zai saurara lokacin da kake cewa ba ka ganinsa, cewa ka kawo ƙara a wurinsa kuma dole ka jira shi.
Même lorsque tu as dit: Il ne considère point; juge-toi toi-même en sa présence, et attends-le.
15 Kuma ka ce, ba ya ba da horo cikin fushinsa ko kaɗan ba ya kula da mugunta.
Car ce n’est pas maintenant qu’il exerce sa fureur, et qu’il lire une grande vengeance du crime.
16 Saboda haka Ayuba ya buɗe baki yana magana barkatai; yana ta yawan magana ba tare da sani ba.”
C’est donc en vain que Job ouvre sa bouche, et que, sans science, il multiplie des paroles.

< Ayuba 35 >