< Ayuba 35 >
2 “Ko kana tsammani wannan gaskiya ne? Kana cewa, ‘Ni mai adalci ne a gaban Allah.’
Crois-tu avoir une juste raison, penses-tu être fondé en droit devant Dieu,
3 Duk da haka kana tambayarsa cewa, ‘Wace riba nake da ita, kuma mene ne zan samu ta wurin ƙin yin zunubi?’
quand tu dis: A quoi bon? Qu'y gagné-je plus qu'à pécher?
4 “Zan so in ba ka amsa kai tare da abokanka.
Je veux te faire une réponse, et à tes amis avec toi.
5 Ku ɗaga kai ku dubi sama ku gani; ku dubi gizagizai a samanku.
Regarde les Cieux! et vois!… Contemple les airs!… ils sont plus hauts que toi!
6 In kun yi zunubi ta yaya wannan zai shafi Allah? In zunubanku sun yi yawa, me wannan zai yi masa?
En péchant, qu'est-ce que tu Lui fais? Par mille péchés comment Lui nuirais-tu?
7 In kuna da adalci, me kuka ba shi, ko kuma me ya karɓa daga hannunku?
En étant juste, que Lui procures-tu? ou que recevrait-Il de la main?
8 Muguntarku takan shafi mutum kamar ku ne kaɗai, adalcinku kuma yakan shafi’yan adam ne kaɗai.
C'est à l'homme, comme à toi, que le péché nuit, et à l'enfant de l'homme, que profite ta justice.
9 “Mutane suna kuka don yawan zalunci; suna roƙo don taimako daga hannu mai ƙarfi.
Oui, de grandes oppressions font pousser des cris, et l'on se plaint des violences de plusieurs;
10 Amma ba wanda ya ce, ‘Ina Allah wanda ya halicce ni, mai ba da waƙoƙi cikin dare,
mais nul ne demande: « Où est Dieu, mon créateur, qui dans les jours sombres sait donner des joies,
11 wanda ya fi koya mana fiye da dabbobin duniya ya kuma sa muka fi tsuntsayen cikin iska hikima.’
qui nous a mieux dotés que les bêtes des champs, et nous a faits plus sages que les oiseaux des Cieux? »
12 Ba ya amsawa lokacin da mutane suka yi kira don taimako domin girman kan mugaye.
Sans doute ils réclament; mais Dieu ne répond pas à l'orgueil des impies.
13 Lalle Allah ba ya sauraron roƙonsu na wofi; Maɗaukaki ba ya kula da roƙonsu.
Non! c'est en vain! Dieu n'exauce pas, et le Tout-puissant n'a point égard à ces cris.
14 Ta yaya zai saurara sosai ko zai saurara lokacin da kake cewa ba ka ganinsa, cewa ka kawo ƙara a wurinsa kuma dole ka jira shi.
Combien toi, tu seras moins écouté, si tu dis que tu peux parvenir à le voir! La cause est sous ses yeux! mets en lui ton espoir!
15 Kuma ka ce, ba ya ba da horo cikin fushinsa ko kaɗan ba ya kula da mugunta.
Mais parce que sa colère ne punit pas à ton gré, le crime, selon toi, lui importe fort peu;
16 Saboda haka Ayuba ya buɗe baki yana magana barkatai; yana ta yawan magana ba tare da sani ba.”
et Job ouvre la bouche pour de vains discours, et entasse des propos dénués de raison.